Skip to content
Part 25 of 48 in the Series Akan So by Lubna Sufyan

Kallon kanta ta ke yi a mudubi. Wannan ne kaya na biyar da ta saka ta na cirewa. Yanzu riga da skirt ne na Atamfa brown. 

Ya karɓe ta sosai. Ba wata kwalliya a fuskarta ban da jagirar da ta yi. A sati ɗayan nan da Khadija ta koya mata jagira ta zama ƙwararriya. 

Kamar ba ita ba. Ga hannunta ya sha ƙunshi. Har gida su Khadija suka kawo mai kunshi jiya ta yi nata jan lalle da baƙi a hannuwa da ƙafa. 

Murmushi ta ke yi ita kaɗai. Ba ƙaramar kewar Fu’ad ta ke yi ba. Ji ta ke ya ƙi sauri ya ƙaraso. 

Sai ƙamshin turaruka ta ke yi. Musamman humrar da Anty Fatima ta ba ta. In ta shafa sai ta wuni da ita a jiki. 

Falo ta fita ta sake duba dining. Komai a shirye ya ke. Mama Indo ta tayata gamawa tun ɗazun ta koma na ta ɓangaren. 

Window ta leƙa ko za ta ga ta inda zai ɓullo. Ta gaji da tsayuwa a wajen ta koma bedroom. 

Sam ta kasa zama waje ɗaya. Sai yawo ta ke yi a cikin gida. Ɗakinshi ta shiga da ta feshe da turaruka. 

Ta zauna kan gadon. Ta lumshe idanuwanta ta buɗe su. Ta ƙagu ya zo ya ga yanda duniyar shi ta canza ta. 

“Sofi…”

Muryarshi ta ji da sauri ta buɗe idanuwanta. Baya cikin ɗakin. Zuciyarta na son fita daga ƙirjinta ta bi inda ta ji kiranshi da yadda ta ke doka mata. 

“Sofi…”

Ta sake ji. Ba ta san sanda ƙafafunta suka yi hanyar fita ɗakin ba. Tsakiyar falo ta ganshi tsaye hannunshi riƙe da akwati. Sai jaka rataye a hannunshi. Tun daga takalmin ƙafarshi ja ta soma kallo zuwa crazy jeans ɗin da ke jikinshi blue. Sai hoodie ɗin da ya ke sanye da ita fari da ja. 

Sannan ta tsaya kan fuskarshi. Hannuwanshi ya buɗe mata yana tarbarta da wani murmushi da ya sa zuciyarta ci gaba da ƙoƙarin fita daga ƙirjinta ta same shi. 

Ƙafafuwanta har sarƙewa suke yi kafinn ta ƙarasa inda ya ke. Taimaka mata ya yi ta hanyar kamo hannayenta. Su ya fara kaiwa bakinshi yana kissing babu ƙaƙƙautawa. Ji ya ke kamar ya haɗiyeta ya ciccike ramukan missing ɗinta da ya yi sannan ya fito da ita ya ƙare mata kallo. 

Lumshe idanuwa ta yi ta na jin ɗumin hannayenta cikin nashi. Laɓɓanshi kan hannuwanta. 

Sai ta ji kama wani abu ya ɗan matsa cikin zuciyarta da ba ta san ba daidai yake ba sai yanzun. 

Ɗagowa ya yi ya kalli fuskarta. Wani abu ya faɗi can ƙasan maƙoshi da ta kasa gane wane yare ne. Kafin ya ja ta jikinshi ya rungume. 

Tana jin yadda ya sauke wata ajiyar zuciya. Hannuwanta ta sa a bayanshi ta ƙanƙame shi. 

Cikin kunnenshi ta ke faɗin, 

“Sannu da zuwa. Na yi kewarka sosai.”

Sumbatar gefen fuskarta ya yi kafin ya ce, 

“Ba sosai ba tunda kina iya ɗorawa akan kalamai.”

Murmushi ta yi. So ta ke ta sake kallon fuskarshi amma zuciyarta na mata ihu saboda tunanin rabata da jikin Fu’ad da ta ke yi. 

A hankali ya kamota yana dawo da ita zuwa ga dubanshi. Idanuwanshi ke yawo kan fuskarta. Sai ka ce ba Sofin shi da ya tafi ya bari ba. Ta ƙara wani kyau. Sai ya ga kamar yankan idanuwanta sun ƙara girma da wani haske. 

Sumba ya manna mata a kowanne ido. Ya yi Muryarshi can ƙasa kuma ya ce, 

“Kinyi kyau sosai.”

Ita ma tashi fuskar ta ke kallo. Akwai abinda ya canza mata. Gashin kanshi ta ke kallo. Haba ta san ya canza ko yaya ne. 

Maimakon askin da ta saba ganin shi da shi wannan karon suma ce cike da kan ko’ina. Irin old school ɗin nan. 

Hannunshi ta kamo ta na faɗin, 

“Mu je ka yi wanka.”

Jakar da ke rataye a hannunshi ya sauke a tsakiyar falon. Ya ɗago da hannunta. Ɗayan ya kamo yana kallon su.

“Ban san ina son ƙunshi ba sai da na fara ganin hannuwanki da shi.”

Murmushin nan da ya ke bala’in so ta yi. Juya idanuwanshi ya yi. Sofi na ƙarasa kashe mishi zuciya ba kaɗan ba. Ta gefe ya zagaya hannunshi ya tsayar da shi a kan ƙugunta suka yi ɗakin shi a haka. Yana turawa wani ƙamshi mai sanyi ya daki hancinshi. 

Kallonta ya ɗan yi. Ya yi murmushi kawai saboda bai da abinda zai ce. Gefen gadonshi ta zauna ya ɗauki towel ya shiga wanka. Tuna abinda ta karanta ta yi. Da sauri ta miƙe ta buɗe wardrobe ɗinshi. Rasa kayan da za ta ɗauko mishi ta yi. 

Irin wandon jikinshi ta gani baƙi. Ta ɗauko masa sai wata Porlo fara ƙal ta ajiye masa a kan gado. 

Turaruka ta ɗauko ta feshe kayan da su sannan ta samu waje ta zauna. Har yanzu zuciyarta ta kasa tsayawa waje ɗaya. 

Tana nan zaune ya fito ɗaure da towel da singlet. Lokaci ɗaya bugun zuciyarta ya ƙaru. Ga wata kunya da ta lulluɓeta. 

Daurewa ta yi ta ɗauki cream ɗin da ta ajiye a gefe ta ƙarasa inda yake kanta a ƙasa. Ɗora shi ta yi kan tafin hannunta ta miƙa mishi kanta na kasa. 

Murmushi ya ke yi tunda ta taso saboda banda ƙafafuwanshi babu inda idanuwanta ke iya kaiwa. Hannunta da man ya haɗa ya riƙe ya ja ta jikinshi. 

Ya yi wani ƙasa da murya kafin ya ce,

“Ba taya ni za ki yi ba?”

Hakan ne niyyarta amma sai ta ji kunya duk ta rufeta. Kai ta ɗaga mishi. Man ya saka cikin hannunta ya ja ta. 

Sam ta ƙi kallonshi. Kan gado ya zauna. Ta ajiye man a ƙasa ta na tsugunnawa. Man ta dangwala tana murza shi cikin hannunta. 

Kanta a ƙasa ya ke ammanl tana jin idanuwan Fu’ad kafe a kanta da suke sa ta jin wani iri. 

Ƙafarshi ta kama kamar yaro ta murza mishi man tun daga ƙwaurinshi zuwa ƙasa. Sake dangwalowa ta yi ta ɗan ɗaga ƙafarshi tana haɗa tafin hannunta da tafin kafarshi ya wani motsa yatsun ƙafar. Sake ƙoƙarin murzawa ta yi ya janye ƙafar yana dariya. Ba ya so komai ya taɓa mishi tafin ƙafa. Wajen is ticklish. 

Kula ta yi ta nufi ɗayar ƙafar ta janyo ta. Hannu ta sa da sauri jikin tafin ƙafarshi tana wasa da ita. Ba shiri ya miƙe yana dariya tare da murza ƙafafun a jikin kafet. 

Kamar yana son goge abinda ta bari. Don har lokacin yana jin hannuwanta a jiki. Gaba ɗaya tsikar jikinshi ta yi wani irin tashi. 

Dariya sosai Safiyya ta ke yi. Ta ɗauka ita kaɗai ke jin wannan abin. Shi a ƙafa ne. Ita wuyanta ne ba ta so a taɓa sam. 

“Ka zauna a ƙarasa.”

Daƙuna fuska ya yi yana ɗaga mata kafaɗa ɗaya.

“Ba na so…”

Kallonta ya ke da murmushi a fuskarshi. Dariya ta ke mishi sosai sosai. Towel ɗin da ke ƙugunshi ya sa hannu ya cire. 

Wani ihu ta saki tana rufe idanuwanta. Dariya ya kama yi sosai har da riƙe ciki. 

“O. M. G Sofi da boxers ɗina fa…”

Mikewa ta yi da gudu ta bar ɗakin. Har ya sa kaya dariya ya ke. Man ya ƙarasa shafawa a hannuwanshi kawai sannan ya fita. 

Tana zaune falo tana raba idanuwa. Yana kallonta ya sake kwashewa da dariya. Ta yi ƙasa da kanta tana murmushi. 

Miƙewa ta yi tana nufar dining. Ya bi ta ya zauna cikinshi har wata ƙara ya ke yi. 

Muryarshi babu wasa ya ce mata, 

“Sofi wa ya yi girki?”

Tun kafin ma ta buɗe warmers ɗin. Kallon fuskarshi ta yi. 

“Ni na dafa maka.”

Kai ya ɗan ɗaga kawai. Yunwa ke cin shi tun shigowarshi. Ganin Safiyya ne ma ya sa ya share.

Tana buɗewa wani ƙamshi ya doki hancin shi. Plate ta ɗauka ta zuba mishi farar shinkafar da ta dafa da ruwan kwakwa. 

Sannan ta samu ɗan wajen zuba miya ta zuba masa miyar da ta sha ganye da naman kaji. 

Ta saka cokali a ciki ta tura gabanshi a nutse. Wani ɗan kwanon ta ɗauka ta zuba dambun naman da ta yi a ciki ta ajiye masa a gefe. 

Sannan ta ɗauki kofuna guda biyu ɗaya ta zuba masa ruwa ɗaya ta zuba masa exotic. Tunda ya tafi suna nan shaƙe da fridge. 

Ba damunta suka yi ba. Ba sha ta ke yi ba. Komawa ta yi ta zauna ta zuba mishi idanuwan. A sanyaye ta ce, 

“Ban san me kafi so ba. Ban san ko kana cin wannan ba.”

Cokalin ya sa ya ɗibi miyar ya zuba a gefe ya ɗan cakuɗa. Ci ya yi ya ɗan yi jim. 

Gabanta faɗuwa ya ke yi kar ko abincin bai mishi ba. Ɗagowa ya yi ya sakar mata wani murmushi mai taushi tare da faɗin,

“Ya min daɗi Sofi. Kin iya girki haka ba kya min?”

‘Yar dariya ta yi ta ce, 

“Da ba ka nan na koya. Anty Laurat da su Khadija su ke koya min.”

Sosai ya ke cin abincin. Ta kuma ji daɗin ganin yana cin abinda ta girka da hannuwanta. 

Kallonshi ta ke. Yanayin yadda ya ke cin abinci na burgeta tun ranar da ta fara gani. Za ka rantse yanayin don cin abinci kawai aka halitta mishi shi. A nutse ya ke yi fuskarshi na nuna yadda abincin ke mishi daɗi. 

Ɗagowa ya yi ya kalleta. 

“Ke ba za ki ci ba?”

Ya buƙata. Kai ta girgiza mishi. Nutsuwa ta yi tana kallonshi. Tsaf ya cinye plate ɗin da ta zuba mishi ya na faɗin,

“Sofi ƙara min…”

Ƙara mishin ta yi. Bai ma cinye ba ya sha lemon kaɗan ya shanye ruwan yana hamdala. 

Kallonta ya yi. 

“Thank you.”

Ta rasa me ya sa turancin shi ke mata daban. A kunyace ta ce,

“Don’t mention.”

Ware idanuwanshi ya yi a kanta. Ta sa hannu tana rufe fuska tare da yin dariya.

“Bude fuskarki Sofi. Na ji daɗi fa. Come on buɗe fuskarki ki kalle ni.”

A hankali ta sauke hannunta. Ta kalle shi. Yanayin da ke fuskarshi na ƙara mata ƙwarin gwiwar yi masa magana da iya turancin da ta yi ƙoƙarin ji.

“You look good.”

Dariya ya yi cike da jin daɗi. Miƙewa ya yi ya zagaya inda ta ke ya ɗan tsugunna ya sumbace ta.

“I fucking love you Sofi.”

Ɗan daƙuna fuska ta yi tare da faɗin, 

“Meye fucking?”

Ɗan sosa kai ya yi maimakon amsa tambayarta sai cewa ya yi, 

“Taso ki ga…”

Yana kama hannunta zuwa falon. Zama suka yi tare ya janyo akwatin ya buɗe. 

Wani ɗan kwali ya fiddo. Zobe ne me kyau sosai silver. Ya zaro shi daga ɗan gidanshi. 

“Ban ma san ko zai zauna a yatsunki ba..”

Hannunta ya kamo cikin nashi ya sa zoben a yatsanta na biyu ya ɗan yi yawa. Na tsakiyar ya saka. Cif ya zauna. 

Kallon zoben da ta ke yi.Wani ɗan kwalin ya ɗauko ya buɗe ya miƙa mata. Iri ɗaya ne sai dai na shi S ne a jiki. Kamar yadda ya yi mata ta yi mishi. Ta kama hannunshi ta saka zoben. Saidai na shi yatsa na biyu ya zauna. 

“Na gode…”

Hannunta ya kamo ya sumbaci inda zoben ya ke. Ita ma mayar mishi da abinda ya yi mata ta yi.

Dariya ya yi ya fito da wasu takalma Pink da suka yi mishi kyau ya miƙa mata. Ita ma kyau suka yi mata sosai ma. 

Miƙewa ta yi tana ture kunyar da ke addabarta gefe ta manna mishi sumba a kunci sannan ta koma ta zauna. Ya kasa daina murmushi. Cikin kanshi ya ke gode wa duk wanda ya canza Sofin shi haka.

Mayar da akwatin ya yi ya rufe don sauran kayan da ke ciki na su Fa’iza ne. Kallon Safiyya ya yi. 

“Ina son zuwa gida amma ban gaji da ganinki ba wallahi.”

Dariya ta yi mishi. 

“Ka je na san suma sun yi kewarka. Ina nan me zan dafa maka?”

Hannu ya kai ya tallabi fuskarta. Sannan ya ce, 

“Akwai sauran abincin da na ci ɗazun?”

Ta ɗaga mishi kai. Ya lumshe idanuwa kafin ya buɗe su a kanta. 

“Zan taho da fruits. Shi zan sake ci.”

Da mamaki ta ke kallonshi ta san da yawan mutane ba sa son sake maimaita kalar abinci a rana ɗaya. Ta ce,

“Shi ka ci yanzun fa. Ka faɗa wallahi in dai na iya zan dafa maka.”

Miƙewa ya yi yana murmushi. 

“Banda matsala da cin kalar abinci ɗaya kullum in dai zai min maganin yunwa balle kuma in ya min daɗi.”

Fu’ad ba zai gaji da ba ta mamaki ba. Har ƙofa ta raka shi. Ya sumbace ta sannan ta tafi. 

Kwanonin da ya ba ta ta ɗauke daga wajen ta yi kitchen da su. Ba ta wani jira Mama Indo ba tunda ba yawane da su ba ta wanke. 

*****

Yana shiga gida Hussaina ta fara ganinshi da gudu ta ƙaraso ta riƙe shi. 

“Ina ta kiranka ba ya zuwa ashe ka dawo ne. Ka ga na ce Anty Fa’iza takai ni gidanka ta ƙi.”

Daƙuna fuska Fu’ad ya yi. 

“Fa’iza ba ta kyauta ba. Ki bar ni da ita. Ni zan zo da kaina in ɗauke ki mu je.”

Riƙe da hannun Hussaina da ta karɓi akwatin da ya shigo da shi ta na taya shi ja suka shiga cikin gida. Gaisawa suka yi da Momma ta ke tambayar Safiyya. 

“Momma ina Haneef?”

Da fara’a ta ce,

“Yana wajen aiki.”

Zaro idanuwa Fu’ad ya yi. Sau nawa suka yi waya da Haneef bai faɗa mishi ya fara aiki ba. Muryarshi a sanyaye ya ce, 

“Bai faɗa min ba.”

Kallon wannan matsalarku ce Momma ta yi mishi. Don bai shafeta ba. 

“Na yi kewar Abba sosai.”

A tausashe Momma ta ce mishi,

“Yana ɗakin shi. Shi ma jiya ya dawo.”

Bai ko bari ta rufe baki ba ya miƙe. Tana kiranshi ko juyowa bai yi ba ya wuce da saurin shi. 

Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ya yi. Muryar Abba ta amsa shi da,

“Shigo…”

Sallama ya yi ya tura ƙofar. Hade rai Abba ya yi da ya ga Fu’ad ne. 

Ƙarasawa Fu’ad ya yi ya tsugunna a gaban Abba. Idanuwanshi ya sauke cikin na Abba. 

“Wallahi na gane laifina Abba. Ya zanga albarka in ka na fushi da ni? 

Abba ba ka ɗaga wayata. Ba ka son ganina. Laifin da na yi ba zai yafu bane?”

Ganin Abba ya yi shiru ya sa shi riƙo hannunshi da na shi duka biyun. Cikin ido ya ke kallonshi yana so ya ga nadamar kuskuren da ya aikata cikin idanuwanshi. 

“Abbah ka yafemun don Allah. Ba zan sake ba. Ka min kowanne hukunci banda nisanta ta.”

Gaba ɗaya yanayinshi ya karyarma da Abba zuciya. A sanyaye ya ce,

“Allah ya yi maka albarka.”

Da sauri Fu’ad ya amsa da,

“Amin Abba na gode. Na gode Allah ya ƙara girma.”

Hira suka ɗan yi da Abba sannan ya mishi sallama ya fito. Momma ya kalla da fara’a a fuskarshi.

“Ni da Abba mun shirya.”

Numfashi Momma ta sauke. Ta ji daɗi sosai. Don har tsoron yin maganar Fu’ad ta ke yi a gaban Abban.

Wucewa ya yi da faɗin,

“Momma na tafi. Ina so in ga Lukman sannan in wuce gida.”

Ta amsa da,

“To shike nan. A kula don Allah.”

“In shaa Allah.”

Fu’ad ya faɗi yana ficewa.

Ya jima sosai a wajen Lukman suna hira. Har yamma liƙis kafin ya miƙe da faɗin, 

“Bari in wuce kar magriba ta yi.”

Lukman ya ce,

“Ya kamata kuwa. Ka barta ita kaɗai.”

Wayarshi ya zaro yana danne danne. Kafin ya kalli Lukman ya ce,

“Sofi ta faɗa min kana zuwa duba ta. Ba na son in faɗa ta cikin waya..”

Kallon shi Lukman ya yi yana katse shi da,

“Wallahi karka fara. Karka soma Fu’ad.”

Wayarshi ya ji text ya shigo. Ya ɗauko ta kan gado. A ƙufule ya kalli Fu’ad. 

“Meye hakan?”

Don ganin kuɗi ne ya tura mishi a account. 

“Biyana za ka yi ko me?”

Da sauri ya ke girgiza kai. 

“Bazan taɓa iya biyanka karamcinka ba Lukman. 

An biyani kuɗina ne na wannan watan. Na yi laifi don na ba wa ɗan uwana?”

Sauke numfashi Lukman ya yi. Fu’ad ɗin ya ɗora da, 

“In ba ka karɓa ba zan ji kamar ban isa in maka kyauta ba.”

“Ba haka ba ne Fu’ad abin ne yana yawa.”

Girgiza kai Fu’ad ya yi. 

“Za mu ɓata duk ranar da ka sake ce min na maka abu ya yi yawa Lukman. Kamar ka na zagin abokantakarmu ne. Za kai min fin haka in kaine a matsayina.”

Jim Lukman ya ɗan yi kafin ya ce, 

“Hakane. Na gode..”

Daƙuna fuska Fu’ad ya yi. 

“Emotional freak…”

Dariya suka yi su duka sannan suka yi sallama Fu’ad ɗin ya fice. Haneef ya kira bugu ɗaya ya ɗauka da yin sallama. 

Amsa shi Fu’ad ya yi ya ɗora da.

“Na zo ba ka nan.”

“Yanzun na shigo gida. Ruwa kawai na watsa Momma ke faɗa min.”

“To bari in ƙaraso gidan yanzun nima na fito gidan su Lukman.”

Amsa shi Haneef ya yi da faɗin, 

“Alright…”

Sannan ya kashe wayar. 

“Ashe ka fara zuwa aiki ba ka faɗa min ba.”

Da mamaki Haneef ya ce, 

“Seriously?”

Yana kallon Fu’ad cikin fuska. Langaɓe kai ya yi. 

“Eh mana. Ko addu’a ai zan maka dai.”

Taɓe baki Haneef ya yi sannan ya ce,

“Yaushe rabon dakae faɗa min za ka yi abu?  Bari na yi in ka dawo ka ji.”

Sake langaɓe fuska Fu’ad ya yi. 

“Na ɗauka we are good fa. Maganar ta wuce.”

“Na ce ba ta wuce ba ne?”

Sosai Fu’ad ya kalle shi. 

“Please. Ba zan sake ba fa. Ka ga Abba ma ya dai na min fushi. Wallahi na ji daban da Momma ta faɗa min.”

Sauke numfashi Haneef ya yi yana kallon Fu’ad. 

“Shikenan. Mu je mu yi Sallah na ji an kira.”

Tare suka wuce masallaci suna taɓa hira. Ana idar da Sallah Fu’ad ya ce gida zai je don ya bar Sofi tun ɗazun. 

*****

Wata miƙa Fu’ad ya yi kan gadon tare da yamutsa fuska yana kallon Safiyya da ke kwance gefenshi. 

“Gajiya ko?”

Ta tambaye shi cike da kulawa. Haɗe sauran space ɗin da ya rage ta yi a tsakaninsu ya yi. Ya ɗora hannunshi kan nata. Ƙafar shi ya mayar kan pillow ɗinta ya haɗe goshinsu. 

Wani taɓare mata fuskarshi ya yi. 

“Sosai fa. Jikina duka ciwo.”

Hannu ta sa ta dangwale mishi hanci ya riƙe hannun ya na sumbatarshi. Lokaci ɗaya ya shiga nuna mata yadda ya yi kewarta. 

Mamaki da sonta ne ya shige shi jin yadda ta saki jiki da shi ta ke tarbar duk wata soyayyar shi da ya ke son nuna mata. 

Kamar wanda aka doka ma guduma akai yai tsaye cik. Fuskarshi Safiyya ta taɓa don jin yai tsaya kamar wanda ya sandare. 

Muryarshi can ƙasan maƙoshi ya ce mata, 

“I love you.”

Yana gyara mata kwanciya a jikinshi. Ba ta amsa shi ba. Shiru kawai ta yi yanajin har bacci ya ɗauke ta. Dafe goshin shi ya yi. Sam bai zaci za ta sake da shi haka ba. Ba a shirye yake ba. Baya son kuskure ɗaya ya ja masa da na sani. Ya yi haƙurin kusan watanni biyu da ɗori. Kwana ɗaya ba zai canza komai ba. Sosai ya yi bincike kan tsarin iyali komawarshi. 

Sai dai gaba ɗaya wanda ya danganci ɓangaren mata akwai complications da side effects da yawa. Ba zai taɓa iya risking ɗin Sofi ba. 

Duk da akwai yiwuwar ta ƙi samun matsalar da ake samu. Amma ba zai iya ɗaukar wannan ba. In kuma aka samu matsalar ba zai taɓa yafe wa kanshi ba. 

Zai yi amfani da protection a yanzu kafin ya samu yadda ya ke so ya yi maganin matsalar gaba ɗaya. Da ƙyar ya samu wani wahalallen bacci ya yi gaba da shi. 

*****

Sallar Asuba ya dawo  ya sake kayan jikinshi ya fita jogging. Yana dawowa ya samu Safiyya a kitchen. Ta baya ya rungumeta. Hannuwanshi ta kama tana jin yadda zuciyarshi ke bugawa da sauri da sauri da fitar numfashin shi. 

“Sofi ba ki shirya ba?”

Ya faɗi yana wani maida numfashi. Ƙwan da ta ke soyawa ta saki hannunshi yana rungume da ita ta baya ta juya. 

Sannan ta ce, 

“Shirin me?”

“Makaranta…”

Ya amsa cikin kunnenta. Murmushi ta yi tana ƙoƙarin janye jikinta daga riƙon da ya yi mata. Sake maƙeta ya yi yana faɗin, 

“Um um fa…”

Sauke frying fan ɗin ta yi daga kan wuta ta ajiye gefe ta na riƙe hannayenshi sannan ta juya suka fuskanci juna.

“Ka ƙyale ni in ƙarasa aikina.”

Cikin idanuwa ya ke kallonta.

“Bakwai saura Sofi. Za ki makara.”

Murmushi ta yi mishi. 

“Babu inda za ni.”

Ware idanuwa ya yi. 

“Saboda me?”

“Saboda kana gida. Saboda kwana yau kaɗai na ke da ita tare da kai. Sai kuma bayan wata nawa ka ce?”

Yadda ta ƙarasa maganar ya sa shi langaɓe mata fuska. 

“Haba mana Sofi kina magana kamar laifina ne.”

Ajiyar zuciya ta sauke. 

“Kwana biyu ne sun yi kaɗan.”

Saida ya sumbace ta sannan ya haɗa goshin shi da nata. 

“Na sani Sofi. Ba ke kaɗai ba.”

Sumbatar shi ta yi a goshi.

“Ka je ka yi wanka in yi aikina.”

Wani shagwaɓe fuska ya yi. 

“Ni an kore ni.”

Dariya ta yi kawai. Ta juya ta ci gaba da aikinta. Ta baya ya haɗa kumatunta da nashi sannan ya wuce. Ta lumshe idanuwanta soyayyarshi na shigarta. Har ranta kwana biyu ya mata kaɗan. 

Wajen goma na safe suna zaune a falo ta ɗauki wayarta. Game ɗin BASE da Khadija ta tura mata ta nutsu ta na yi.

Wayar ta ji Fu’ad ya fisge ta kalle shi fuskarta a shagwaɓe. 

“Kaban wayata.”

“Me kike yi.”

Hannu ta kai ta karɓe wayarta kafin ta ce,

“Wani game ne mai daɗi khadijaU ta tura min.”

Komawa ya yi kan kujerar da take. Mai guda ɗaya ce don haka ya ɗaga ta ya zauna sannan ya zaunar da ita kan cinyarshi. 

Game ɗin suka dinga yi tare. Ya kai hannu zai danna ta ture hannunshi. 

“Ba fa nan ba ne. Sai ka sa an kama ni…”

Dangwalawa ya yi ta mintsine shi.

“ouuchh Sofi da zafi fa…”

Wayarshi ta hau ringing. Safiyya ta miƙa hannu ta ɗauko mishi. Lukman ne. 

Tana game ɗinta ya gama wayarshi. Matse ta ya yi a jikinshi sannan ya ce, 

“Fita zan yi.”

Haɗe rai ta yi. 

“Haba mana. Don Allah ka ce wa Lukman ya bar min kai yau.”

Dariya ta ba shi. Wayar ya miƙa mata. 

“Kira shi ki faɗa mishi.”

Murmushi ta yi a kunyace tana tashi daga jikinshi. Miƙewa ya yi shi ma ya yi cupping fuskarta.

“I love you…”

“I love you too.”

Ta amsa shi. Sannan ya fice. 

Hijabinta ta ɗauko ta zagaya ta kira Mama Indo don ta tayata ko gyara cefane ne don girkin ya yi mata sauri. 

“Wai me za ka yi a chemist?”

Lukman ya tambaya cike da rashin fahimta. Narrowing idanuwan shi Fu’ad ya yi yana faɗin, 

“Ba kyau yawan bincike.”

Lukman da hankalin shi ke kan tuƙin da ya ke yi ya ɗan juyo ya kalli Fu’ad ɗin kafin ya ci gaba da abinda ya ke yi. 

“Allah ko?”

Shiru ya yi ya ƙyale shi. Bakin wani babban Chemist Lukman ya yi parking. Ya kalli Fu’ad ya ce,

“Ka yi sauri…”

Bai dai kula shi ba ya fice daga motar. Ya kai minti sha biyar sannan ya dawo. 

Sosai Lukman ke nazarin shi ya zauna kanshi a ƙasa yana wasa da zoben hannunshi. 

“Fu’ad?”

Ya kira cike da alamar tambaya. Ɗago fuskar shi da ta yi wani ja ya yi ya kalli Lukman sannan ya maida hankalinshi kan zoben shi.

“Ba damuwar ka bane. Just drop it.”

Kallonshi Lukman ya ci gaba da yi.

“Me ka siyo?”

Ya buƙata. Ɗago idanuwa Fu’ad ya yi ya kalle shi cikin ido. 

“Banda kai please. Ni da kuɗina mai Chemist da mutanen dake ciki sun bi ni da kallon da ke screaming ɗan iska. 

Saboda me mutane ba za su bar abinda bai shafe su bane?”

Riƙe baki Lukman ya yi yana wani jan numfashi. Cike da tashin hankali ya ce, 

“Tell me ba abinda na ke tunani bane Fu’ad..”

Katse shi ya yi da faɗin, 

“I don’t want kids. Fucking shut up.”

“Fu’ad?”

A ƙufule ya ce,

“Fucking stay out of this Lukman.”

Shi ma a ƙufule ya ce, 

“Fine…”

Ya fisgi motar. Lumshe idanuwa Fu’ad ya yi. Bai san sanda ‘yan Nigeria za su canza ba. Shiga abinda babu ruwansu..!”

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Akan So 24Akan So 26 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×