{"id":4003,"date":"2023-10-28T07:22:24","date_gmt":"2023-10-28T07:22:24","guid":{"rendered":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/?p=4003"},"modified":"2024-06-02T12:51:37","modified_gmt":"2024-06-02T12:51:37","slug":"kamanceceniya-a-cikin-wasu-labaran-lubna-sufyan","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/kamanceceniya-a-cikin-wasu-labaran-lubna-sufyan\/","title":{"rendered":"Kamanceceniya a cikin wasu labaran Lubna Sufyan"},"content":{"rendered":"\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Gabatarwa<\/h2>\n\n\n\n<p>Rubutu abu ne mai matu\u0199ar muhimmanci a wurin kowace irin al&#8217;ummar da take rayuwa a cikin wannan duniya. Irin muhimmancin da rubutu ke da shi ne ya sa kai tsaye ake danganta shi da ilimi, domin ya dace da shi \u0199warai da gaske. Duniyar rubutun labarai na \u0199asar Hausa ba ta da fa\u0257i sosai in aka ce za a kwatantata da irin na sauran manyan \u0199asashen duniya. Domin ba a fara rubutun ajami a \u0199asar Hausa ba har sai da Hausawan suka cu\u0257anya da Larabawa. Kuma ba a fara rubutu da Hausar boko ba, har sai da Turawan mulkin mallaka suka zo. Kenan in aka yi la&#8217;akari da wannan, a iya cewa samuwar rubutu, musamman irin na Hausar boko a \u0199asar Hausa bai wani jima can ba.<\/p>\n\n\n\n<p>To sai dai kuma, da yake harshen Hausa gagarabadau ne, daga lokacin da rubutun Hausar boko ya samu zuwa yanzu an samu tarin litattafai da kuma \u0199arin marubutan da ba su da adadi, kuma a kullum \u0199aruwa suke yi. Wannan ya taimaka \u0199warai wajen ci gaban adabi da kuma al&#8217;adun Hausawa. A bisa wannan dalili ne na nazarci wasu litattafan \u0257aya daga cikin za\u0199wa\u0199wuran marubutan wannan zamani, wato Lubna Sufyan. A cikin wannan nazari nawa ne na hango irin kamanceceniyar salo, zubi, tsari da ma taurari da ita marubuciyar ta yi amfani da su wajen gina wa\u0257annan labarai nata. Wannan kamanceceniya kuwa ta zo ta fannoni da da yawa, sai dai zan ta\u0253o ka\u0257an ne kawai daga ciki.<\/p>\n\n\n\n<p>Samun kamanceceniya a cikin labaran marubuta ba sabon abu bane, kuma ba aibu bane kai tsaye. Sai dai a wasu lokutan yana iya zama maimaici ne kawai na abu guda maimakon samar da wani abu sabo. A bisa wannan dalili, wannan mu\u0199ala za ta yi duba ne kawai zuwa ga kamanceceniyar ba wai aibun samuwarsu ko amfaninsu ba. Sai dai daga \u0199arshe, za a samu wasu &#8216;yan shawarwari wa\u0257anda za su taimaka wajen yin amfani da kamanceceniyar yadda ya kamata.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Wacece Lubna Sufyan?<\/h2>\n\n\n\n<p>Marubuciya Lubna Sufyan an haife ta ne a \u0199aramar hukumar Ingawa da ke birnin Katsina. Fitacciyar marubuciyar ta fara karatun addini tun tana \u0199arama kuma ta yi karatunta na Firamare ne a garin Katsina, daga baya ta koma garin Kano inda ta yi karatunta na Sakandire har ta gama. Bayan ta gama ne sai ta koma Katsina in da ta yi karatun Diploma a \u0253angaren zanen taswirar gidaje. Daga baya kuma ta ci gaba da karatu a mataki na gaba, wato babbar Diploma wadda da Turanci ake kira Higher National Diploma (HND) a Kaduna.<\/p>\n\n\n\n<p>Kamar mafi yawancin marubuta, marubuciyar ta fara rubuce-rubuce ne tun tana makaranta, kuma ta kasance \u0257aya daga cikin fitattun marubutan online na wannan zamani, domin abu ne mai wuya ka fa\u0257i sunanta a duniyar marubuta da makarantan wannan zamani ba a samu wanda ya santa ba. Zuwa yanzu marubuciyar ta rubuta <a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/author\/lubnasufyan1\/\" data-type=\"link\" data-id=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/author\/lubnasufyan1\/\">litattafai sama da guda goma sha \u0257aya<\/a>.<\/p>\n\n\n\n<p>Har&#8217;ilayau kuma, marubuciyar ta kasance mai son girke-girke ce sosai. Kuma baya ga rubutu, marubuciyar tana yin fassara daga harshen Turanci zuwa Hausa, wannan aiki na fassara ne ma ya zama sanadin yin aikinta da kamfanoni da \u0199ungiyoyin gwagwarmaya masu zaman kansu a lokuta daban-daban a kuma kan batutuwa iri daban-daban kamar su GiveNorthEducation, WomenInArewa, WomenInFinance da dai sauransu. Sannan kuma, marubuciyar ta sha yin aiki da makarantun Islamiyya da bloggers wajen fassara musu aiyukansu. Haka kuma \u0199wararra ce wajen ha\u0257a \u0257uwatsun \u0199awa na adon mata. Sannan kuma tana aikin juyar da bayanan murya zuwa rubutu (transcription). A ta\u0199aice dai, duk in da aikin rubutu yake, to a nan marubuciyar ta fi \u0199arfi.<\/p>\n\n\n\n<p>Marubuciyar kuma na \u0257aya daga cikin mambobin \u0199ungiyar marubuta na Fikra Writers Association. Lubna Sufyan ta yi aure a shekarar 2022, kuma tana zaune ne a garin Kaduna yanzu haka tare da mijinta.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Litattafan da ta rubuta<\/h2>\n\n\n\n<p>Marubuciya Lubna Sufyan ta rubuta litattafai da dama, ga wasu daga cikinsu;<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Rayuwarmu<br>\u2022 Akan So<br>\u2022 Mijin Noble<br>\u2022 Tskaninmu<br>\u2022 Abdul\u0199adir<br>\u2022 Al\u0199alamin \u0198addara<br>\u2022 Martabarmu<br>\u2022 Rai Da \u0198addara<br>\u2022 Wata Bakwai<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Labaran litattafan a ta\u0199aice<\/h2>\n\n\n\n<p>A wannan mu\u0199ala, na nazarci litattafai guda hu\u0257u ne daga cikin wa\u0257anda ta rubuta. Ga ta\u0199aitaccen bayani game da kowanne daga cikinsu;<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/abdulkadir-1\/\" data-type=\"link\" data-id=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/abdulkadir-1\/\">Abdul\u0199adir<\/a><\/h3>\n\n\n\n<p>Alhaji Ahmad Bugaje yana da matan aure har guda hu\u0257u. Matarshi ta farko ita ce Hajiya Safiyya wadda ake kira da Hajja. Ta haifi yara takwas tare da shi, su ne Muhsin, Yazid, Khadija, Mubarak, Abdul\u0199adir, Zahra, Nazir da kuma Zainab. Matar shi ta biyu kuma ita ce Hajiya Saratu wadda ake kira da Mama. Tana da yara biyar da Alhaji Ahmad dukkan su maza. Ahmad (wanda ake kira da Babangida), Yasir da Yazid wa\u0257anda suka kasance &#8216;yan biyu, sai kuma Salim da Khalid.<\/p>\n\n\n\n<p>Hajiya Sakina ita ce matar shi ta uku da yaransu ke kira Mami, wadda kuma ita ka\u0257ai ce ya aura a bazawara, don shekararta \u0257aya da wata uku da yin aure Allah ya yi wa mijinta rasuwa bayan gajeruwar rashin lafiya da ya yi fama da ita. Ya kuma rasu a lokacin ya barta da cikin wata shida. Ta haifi yarinyarta mace, bayan ta yayeta ne suka ha\u0257u da Alhaji Ahmad Bugaje. Bai aureta ba sai da ya yi mata al\u0199awarin ri\u0199e mata yarinyarta. Bayan Waheedah, ta haifi yara uku da shi, su ne, Sa&#8217;adatu (wadda ake kira da Amatullah), Aminu da kuma Habib. Hajiya Halima kuwa da yaran duka ke kira Anty, ita ce mata ta hu\u0257u kuma amarya a gidan Alhaji Ahmad, &#8216;yar tsohon Wazirin Kano ce da Allah ya yi wa rasuwa ya aura. A cikin matan shi ita ka\u0257ai ce take aikin gwamnati, domin kuwa da aikinta ya aure ta. Allah ya azurta su da yara shida, saboda ta fi sauran matan shi haihuwa gab da gab, kusan abinda akan kira da kwanika ko gwarne. Yaran su ne, Nusaiba, Nabila, Kabiru, Adnan da Baraka.<\/p>\n\n\n\n<p>Duk da wannan yawa nasu, hakan bai sa yaran kansu ya rabu ba, domin suna son junansu kuma suna girmama na gaba da su. Sannan suna da ha\u0257in kai tare da zumunci da kuma damuwa da junansu. Domin ko \u0199urjewa wani ya yi aka ce ga shi can kwance, to yanzu za ka gansu \u0257uuu duk sun yo kanshi. Wannan dalili ne ya sa kusan ko&#8217;ina suka je nan da nan ake gane su. Hatta Waheedah da ba Alhaji Ahmad ya haifeta ba haka suke mata, saboda ba sa nuna mata wani bambanci, komai a tare suke yi.<\/p>\n\n\n\n<p>Abdul\u0199adir tun yana da \u0199arancin shekaru yake sha&#8217;awar aikin soja, kuma har ya girma yana da wannan ra&#8217;ayi. Yana da zafi sosai, kuma ba ya \u0257aukar raini balle \u0257aga \u0199afa. Saboda takurawa \u0199annensa da yake yi ne a gida ma har suka sa mishi suna &#8216;Commander&#8217; a \u0253oye. Yayan shi Yassar ne ka\u0257ai yake \u0257an saurarawa a duk cikin gidan saboda sun fi jituwa.<\/p>\n\n\n\n<p>Waheedah tana da sanyin rai da sau\u0199in hali, ga ha\u0199uri da ladabi da biyayya. Wannan yasa kowa ke sonta. Tana da wata \u0199awa da ke ma\u0199wabtaka da su mai suna Nuriyya. Duk da cewa gidan su Nuriyya talakawa ne, hakan bai sa Waheedah ta \u0199yamace ta ba. Sha\u0199uwar da suka yi ne ma ya sa har \u0257inki da sauran abubuwa na yau da kullum akan yi musu tare. Domin har ce musu ake yi &#8216;yan biyu. Babban abin da ya raba su shi ne, Nuriyya tana da son abin duniya.<\/p>\n\n\n\n<p>Yau da gobe, duk da ba\u0199in hali irin na Abdul\u0199adir da takura da dukan da yake yi wa yaran gidan da zarar sun yi laifi ko wani \u0257an kuskure bai hana zuciyar Waheedah kamuwa da \u0199aunarsa ba. Wannan kuwa ya faru ne tun tana da \u0199arancin shekaru. Sai dai ta \u0253oye soyayyar a zuciyarta domin da fari ita kanta bata san cewa abinda take ji a ranta sunan shi so ba saboda \u0199arancin shekaru. Shi kuwa Abdul\u0199adir sam ba shi da burin auren mace irin Waheedah, wannan yasa ko sau \u0257aya bai ta\u0253a kawota a ranshi ba. Amma bayan ya zo bikin \u0199annensa, a wannan lokaci sai ya ji zuciyarsa ta fara bugawa Nuriyya, domin tana da siffa irin ta macen da yake so, sai dai ya \u0199i bayyana mata saboda a lokacin yana tsaka da kar\u0253ar horo a makarantar Sojoji ta NDA da ke Kaduna, kuma ya \u0199udurce a ranshi cewa sai ya kammala tukunna ko da zai sa ranshi a wani al&#8217;amari da ya shafi aure.<\/p>\n\n\n\n<p>A gefe kuma, Yazid ya kamu da son Waheedah sosai, sai dai shi ma bai fa\u0257a mata ba saboda yana tunanin ta yi yarinya da yawa. Ita kuma Nuriyya, ta samu wani saurayi mai suna Anas wanda yake sonta tsakaninsa da Allah, sai dai ita kuma bata son shi, tana dai kula shi ne kawai saboda yana kashe mata ku\u0257i. A \u0199arshe dai Mahaifinta ya aura mata shi duk da bata so ba. Hakan ya sa Abdul\u0199adir ya ji ba da\u0257i sosai.<\/p>\n\n\n\n<p>Da Yassar ya gane cewa Yazid na son Waheedah, sai ya yi marmaza ya sanar mishi da cewa ai suna soyayya da Abdul\u0199adir. Shi kuma saboda ba zai iya ha\u0257a soyayya da \u0199aninsa ba sai ya ja baya, a \u0199arshe ma ya yi nesa da garin. Abdul\u0199adir kuwa, da dai ya ji cewa ai Waheedah tana son shi, sai ya nemi ji daga bakin ta. Ko da ya samu tabbaci, sai nan take ya samu mahaifinsa da maganar aure.<\/p>\n\n\n\n<p>Kowa na gidan sai da ya jinjina maganar auren, amma hakanan aka yi tunda sun nuna suna so. Bayan an yi auren da wasu &#8216;yan shekaru ne Nuriyya ta kaso nata auren ta fito, ta kuma zo ta aure wa babbar \u0199awarta miji, wato Waheedah.<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/akan-so-1\/\" data-type=\"link\" data-id=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/akan-so-1\/\">Akan So<\/a><\/h3>\n\n\n\n<p>Fu&#8217;ad Arabi shi ne \u0257a na hu\u0257u daga cikin &#8216;ya&#8217;ya bakwai da Alhaji Salman Arabi da Hajiya Aisha suka mallaka. Fu&#8217;ad ya fita daban da sauran &#8216;yan gidansu. Domin ya kasance mai son kai, ta\u0199ama da kuma nuna isa. Bugu da \u0199ari baya kallon kowa da gashi bayan iyayensa da &#8216;yan uwansa sai kuma babban abokinsa wato Lukman. Tun tasowarshi ba shi da aiki sai buga wasan \u0199wallon \u0199afa. Ya sha \u0199in zuwa makaranta akan wasan \u0199wallo. Tun suna duka da fa\u0257a har suka gaji suka soma ba shi goyon baya. Lokacin da ya shiga aji shida a Sakandire ne ya samu \u0257aukaka zuwa \u0199asar Europe.<br>Dole su Alhaji Salman suka \u0199yale Fu&#8217;ad ya tafi. Da \u0199yar ya dawo ya zana jarabawar WAEC ka\u0257ai.<br>A can ya nemi gurbin karatu saboda aikinsa na wasan \u0199wallon \u0199afar ya sa zaman shi ya koma can.<\/p>\n\n\n\n<p>Fu\u2019ad da Safiyya sun yi aure ne ba tare da amincewar iyayensu ba, domin ana gab da \u0257aura wa Safiyya aure ta bi Fu\u2019ad suka je wani wurin aka \u0257aura musu aure. Sai dai rashin samun albarka daga iyayen nasu ya sa auren bai yi \u0199arko ba.<\/p>\n\n\n\n<p>Safiyya ita ce yarinya ta biyu cikin &#8216;yaya uku kacal da Malam Audu da Zainabu suka mallaka a duniya. Safiyya na da &#8216;ya guda \u0257aya jal, wata yarinya me \u0257ankaren wayo tare da saurin shiga rai da ake kira da suna Nana wacce ke fama da cutar daji. Likitoci sun bayyana cewa, domin Nana ta rayu sai an yi mata dashe (transplant). Idan ba a samu wanda ya yi daidai da ita ba, za ta iya rasa ranta cikin watanni shida ko \u0199asa da haka. Mutun na farko da ake sa ran ko nashi zai zo daidai da nata shi ne mahaifinta, wato Fu\u2019ad Arabi wanda aka fi sani da &#8216;Moh&#8217; wanda bai ma san da ita ba.<\/p>\n\n\n\n<p>Shi kuwa Fu\u2019ad tun asali baya son haihuwa, domin har zuwa ya yi aka yi masa aikin da ya kashe masa \u0199wayoyin haihuwarsa gaba \u0257aya don kada ma ya haihu. Samun cikin Nana da Safiyya ta yi ne ma yasa ya saketa kuma ya rabu da &#8216;yan uwanshi ya koma Turai da zama har na tsawon shekaru goma sha \u0257aya. Nana na son ganin mahaifinta kafin ta rasu, a gefe kuma masoyanta na fata babanta ya zama dai dai da abinda likitoci ke so domin ta tsira da rayuwarta. To amma ita Safiyya tana ganin wannan abu ba mai yiwuwa bane, domin ta san halin Fu\u2019ad da yadda yake da son rai. Kuma maganar da ya yi mata na \u0199arshe kafin ya bar \u0199asar ita ce; &#8220;I don&#8217;t do happily ever after. Daga ranar da kika yarda da soyayyata ya kamata ki san ban yi kalar wanda zai dinga zarya da yara da pampers ba. Ban yi kama da wanda zai yi asarar lokaci da soyayyar shi akan yara ba. Ina da su Haneef, ina da su Fa&#8217;iza. A duk lokacin da na ji marmarin ganin yara zan je gidansu in ga nasu.&#8221;<\/p>\n\n\n\n<p>Dr. Jana ita ce likitar da ke kula da Nana. Auren soyayya suka yi da mijinta Jabir. Suna matu\u0199ar son junansu, kuma sun aminta da juna sosai. Sannan Allah ya azurta su da zuri&#8217;a. To sai dai kuma, aikin da Jana ke yi na neman zama matsala a tsakaninsu, wanda hakan ya sa Jabir ya fara tunanin \u0199ara aure. Aina abokiyar aikin Jabir ce, domin waje guda suke aiki. Tana burge Jabir sosai saboda kamun kai, hankali da kuma nutsuwarta.<\/p>\n\n\n\n<p>Nuriyya matashiya ce mai kamun kai da ri\u0199on addini, sai dai ta yi rashin samun nagartacciyar uwa. Domin kuwa, ita kullum \u0199o\u0199ari take yi ta sa ta a hanyar ba\u0257ala. Ta kamu da son wani bawan Allah mai suna Farhan wanda ya taimaka mata a rayuwa sakamakon mummunan halin da ta tsinci kanta a ciki. A dai dai lokacin da ya yi yun\u0199urin aurenta, a dai dai wannan lokaci ne kuma mahaifinsa ya turje akan shi \u0257ansa ba zai auri mace irin Nuriyya ba, ya kuma ba shi za\u0253i ko su ahalinsa ko Nuriyyar. Wannan dalili ne yasa Farhan bin mahaifinsa suka bar \u0199asar. Bayan tafiyar su ne Nuriyya ta ha\u0257u da Nawaf, wanda ya maye mata gurbin Farhan ta fannoni da dama har suka yi aure. Allah ya jarabci Nawaf da shaye-shaye da kuma ba\u0199in kishi na nunawa a kasuwa. Ita kuma Nuriyya duk da irin son da take yi wa Nawaf, ta kasa cire Farhan daga zuciyarta.<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/alkalamin-kaddara-1\/\" data-type=\"link\" data-id=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/alkalamin-kaddara-1\/\">Al\u0199alamin \u0198addara<\/a><\/h3>\n\n\n\n<p>Mahaifin Tasneem mai suna Muftahu wanda aka fi sani da Abba, wani mutumin kirki ne talaka mai neman na kanshi domin ganin ya rufa wa kanshi da ahalinsa asiri. Amma matarsa Bara&#8217;atu wacce ake kira da Ummi irin matan nan ne da basu da godiyar Allah. Duk abinda ya kawo bata godewa, kuma sai ta fita ta je inda take so ba tare da ta tambaye shi ba, yaran kuwa bata kula d su yadda ya kamata. Kullum cikin maula take tare da kiran babu. Bisa wannan dalili ne har \u0199addara ta kai Tasneem wani gida a matsayin &#8216;yar aiki har yaron gidan ya yi mata fya\u0257e. Wannan ne ya jawo silar da ta fara biye-biyen maza domin ta kula da \u0199annenta.<\/p>\n\n\n\n<p>Hankalin Tasneem ya yi matu\u0199ar tashi sakamakon asirinta da ya tonu tun a daren ta na farko da auren Rafiq. Domin kuwa Ya gano cewa bata zo gidan shi da budurcinta ba Wannan yasa ta shiga tashin hankalin da har zuwa \u0199arshen littafi na biyu bata fita daga cikin shi ba.<\/p>\n\n\n\n<p>Alhaji Mustafa Shettima wanda tsohon lauya ne, \u0257an kasuwa kuma \u0257an siyasa ya kasance yana iya yin komai don ganin ya cimma burikansa na siyasa. Ciki kuwa har da yi &#8216;yarsa auren dole ta hanyar ro\u0199onta da ta auri wanda bata ta\u0253a gani ba, ita kuma ta amince saboda biyayyarta, duk kuwa da cewa tana da wanda take so wato Muneeb.<\/p>\n\n\n\n<p>A gefe kuma ga Altaaf da matarsa Majida wa\u0257anda ke neman haihuwa ruwa a jallo amma basu samu ba. Kwatsam! Sai Altaaf ya gano cewa yana da yara &#8216;yan biyu a wani \u0199auye wa\u0257anda Nuwaira ta haifa ba tare da ya sani ba bayan ya mata fya\u0257e shekaru da dama da suka wuce.<\/p>\n\n\n\n<p>Ashfaq, wanda mutuwar mahaifansa da ta &#8216;yan uwanshi har guda biyu tare da \u0253acewar \u0199anin shi \u0257aya suka sa shi neman ku\u0257i ido rufe domin kauce wa \u0199addarar talauci kuma na kwance yana jinyar raunin harbin da aka yi mishi da bindiga sakamakon har\u0199allar miyagun \u0199wayoyi da ta ha\u0257a shi da wasu. Ga kuma \u0199aninsa watau Tariq wanda shi kuma yake fama da jarabar shan kayan maye wadda ya kasa dainawa, duk kuwa da cewa har gidan nahaukata ya ta\u0253a zuwa a dalilin hakan.<\/p>\n\n\n\n<p>Rafiq na cikin tashin hankali na sanin cewa matar da ya aura ta san wasu mazan a waje, sai kuma wani sabon tashin hankalin ya fa\u0257o mishi, domin kuwa baya iya tu\u0199i sai dai a tu\u0199a shi, duk kuwa da cewa yana iya tuno lokacin da yake tu\u0199in da kanshi. A gefe kuma \u0199anwar shi da aka yi wa auren dole ta kira shi tana neman ya zo ya \u0257auke ta sakamakon azabar da take sha a gidan mijin ya ishe ta. A daidai lokacin da ya gano cewa hatsarin mota ne da ya yi ya sa ya manta rayuwarsa ta baya, a daidai wannan lokacin ne kuma ya gano cewa wannan hatsarin ne ya yi sanadiyyar mutuwar matarsa da &#8216;yarsa wa\u0257anda ya kasa tuno ko da sunan su balle rayuwar da suka gudanar a tare.<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/rayuwarmu-1\/\" data-type=\"link\" data-id=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/rayuwarmu-1\/\">Rayuwarmu<\/a><\/h3>\n\n\n\n<p>Rayuwarmu labari ne akan wani babban ahali da ya \u0199unshi mutane da dama a cikinsa. Ko da yake kusan kowa da ke cikin ahalin mutumin kirki ne, hakan ba ya nufin babu saniyar ware a cikinsu, kuma hakan ba ya nufin ba za su fuskanci \u0199alubale ba a rayuwarsu.<\/p>\n\n\n\n<p>A daidai lokacin da rayuwa ke yi wa su Dawud da\u0257i duk da \u0199arancin wadatar arzi\u0199i da ta same su, kwatsam sai gashi wata mata ta yi wa rayuwarsu dirar mikiya ta hanyar \u0199wallafa ranta akan mahaifinsu wato Auwal. A dalilin wannan mata ne suka tsinci kansu a cikin tashin hankalin da ko a mafarki basu ta\u0253a tsammanin shiga cikin irinsa ba. Hakan ya sa Dawud \u0257aukar nauyin da bai shirya ba a kafa\u0257ar shi wadda ita ma neman wanda za ta jingina da shi take yi.<\/p>\n\n\n\n<p>Labeeb jarumin fim ne wanda ya yi shura. Baya ga wannan, ya fito daga gidan ku\u0257i ta yadda ba za ka ta\u0253a tunanin yana da damuwa ba a rayuwarsa. Sai dai kash, ya fa\u0257a cikin rayuwar shaye-shaye da neman mata. Kwatsam kuma sai \u0199addarar rayuwa ha\u0257a shi da Mamdud wanda ya \u0257auka a matsayin aboki kuma \u0257an uwanshi. Abinda bai sani ba shi ne, zuciyar Mamdud a koda yaushe \u0199una take yi bisa ganin yadda komai ke zuwa mishi da sau\u0199i sakamakon ku\u0257i da kuma baiwar shura da Allah ya yi mishi. Abin da Mamdud bai fahimta ba shi ne, duk iya farincikin da Labeeb ke bayyanawa a fili, damuwar da ke cikin rayuwarshi ta fi wannan. Rikici da turka-turkar da ke tsakaninsu ba ta fito fili ba sai da \u0199addara ta ha\u0257a su son mace \u0257aya.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Kamanceceniyar da ke tsakanin labaran<\/h2>\n\n\n\n<p>Ire-iren kamanceceniyar da ke tsakanin wa\u0257annan labarai suna da yawa, akwai manya sannan kuma akwai \u0199anana. Ga jerangiyar wasu manya daga cikinsu;<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\">Manyan kamanceceniya<\/h3>\n\n\n\n<p>1. Soyayyar &#8216;yanuwantaka a tsakanin taurari maza da mata &#8211; marubuciyar takan kawo irin wannan soyayya a tsakanin taurari sosai ta yadda mai karatu zai dinga jin kamar gaske ne ba labari ba. Misali shi ne irin soyayyar da ke tsakanin Raafiq da \u0199annenshi (Al\u0199alamin \u0198addara), Tasneem da \u0199annenta (Al\u0199alamin \u0198addara), Faq da &#8216;yan&#8217;uwanshi (Al\u0199alamin \u0198addara), Fu\u2019ad da &#8216;yan&#8217;uwanshi (Akan So), Abdul\u0199adir da &#8216;yan&#8217;uwanshi (Abdul\u0199adir), Labeeb da &#8216;yan&#8217;uwanshi (Rayuwarmu), sai kuma Dawud da &#8216;yan&#8217;uwanshi (Rayuwarmu).<\/p>\n\n\n\n<p>2. Kula da sallah sosai daga taurari &#8211; marubuciyar ta bayyana wannan \u0253angaren sosai a cikin litattafan. Daga cikin taurarin da aka bayyana suna da irin wannan halin akwai Fu&#8217;ad da Safiyya (Akan So), Abdul\u0199adir da Waheedah (Abdul\u0199adir), Labeeb da Ummi (Rayuwarmu), sai kuma Rafiq (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>3. Samuwar &#8216;yan mata masu mutunci wa\u0257anda mummunar \u0199addara ke fa\u0257a wa &#8211; a wannan \u0253angaren ma marubuciyar ta sako su a cikin dukkan wa\u0257annan litattafan. Ga su kamar haka; Fadila da Nuwaira (Al\u0199alamin \u0198addara), Yumna da Tasneem (Rayuwarmu), Sofi (Akan So) da Waheedah (Abdul\u0199adir).<\/p>\n\n\n\n<p>4. Tarin ku\u0257i ga taurari maza da kuma talauci ga taurari mata &#8211; wannan ma wani abu ne da marubuciyar ta yi amfani da su a cikin dukkan litattafai hu\u0257un da na nazarta. Taurari maza da suka fito a matsayin masu tarin dukiya suna ha\u0257a da Abdul\u0199adir (Abdul\u0199adir), Altaaf Tafida (Al\u0199alamin \u0198addara), Fu&#8217;ad (Akan So), El Labeeb (Rayuwarmu) da kuma Rafiq (Al\u0199alamin \u0198addara). Mata kuma da aka bayyana sun fito daga gidan talauci su ne kamar haka; Sofi (Akan So), Yumna (Rayuwarmu), Nuriyya (Abdul\u0199adir) da kuma Nuwaira (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>5. Kashe taurari &#8211; Marubuciyar ta kashe taurari da yawa a cikin wa\u0257annan labarai guda hu\u0257u. Taurarin da ta kashe sun ha\u0257a da; Ummi (Rayuwarmu), Sameera da &#8216;yarta (Al\u0199alamin \u0198addara), Nana (Akan So), Sajda da Arif (Rayuwarmu), Abba (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>6. Kawo hoton na\u0199uda &#8211; marubuciyar ta kasance mai ba wa allurar mata muhimmanci sosai a cikin labaranta, musamman abinda ya shafi na\u0199uda. Ta kan kawo bayanin yadda wahalar na\u0199uda take da kuma irin halin da mata masu na\u0199udar ke shiga ta yadda mai karatu zai ji tamkar a gabansa abin ke faruwa. Ta bayyana hakan ya faru a da taurari kamar haka; Ateefa (Rayuwarmu); Waheedah (Abdul\u0199adir) Ummi (Rayuwarmu).<\/p>\n\n\n\n<p>7. Gagarumar Sadaukarwa &#8211; Wannan ma wani \u0253angare ne da marubuciyar ta yi amfani da shi sosai a cikin labaran. Misali; Lukman ya sadaukar da jaririyar da aka haifa masa ga Fu&#8217;ad (Akan So), Da kuma yadda Yazid ya ha\u0199ura da soyayyar Waheedah saboda \u0199aninsa yana tunanin \u0199aninsa na so (Abdul\u0199adir), Yadda Aslam ya yarda ya auri Nuwaira, wadda yayansa Altaf ya yi wa fya\u0257e (Al\u0199alamin \u0198addara) sai kuma yadda Labeeb ya sadaukar wa Mamdud da \u0257ansa (Rayuwarmu).<\/p>\n\n\n\n<p>8. Salon tafiyar kura &#8211; gaba \u0257aya labaran nan guda hu\u0257u ta yi amfani da salon tafiyar kura ne wajen rubuta su. Ma&#8217;ana, daga tsakiya take \u0257aukar labarin ta tafi sannan daga baya ta zo ta warware farkonsa kafin kuma ta ci gaba suwa \u0199arshe.<\/p>\n\n\n\n<p>9. Kawo wani ilimi da ya shafi likitanci &#8211; a cikin litattafai biyu daga cikin hu\u0257un nan marubuciyar ta yi amfani da wasu manyan matsaloli na \u0253angaren likitanci masu kama da juna. A cikin littafin Rayuwarmu ta yi amfani da P.C.O.S (Polycystic Ovary Syndrome) wato matsalar da ka iya sa wa mutum ya kasa samun haihuwa. Kamar yadda a cikin littafin Akan So kuma ta yi amfani da Vesectomy, wato fi\u0257ar da ake yi wa maza ta yadda \u0199wayoyin halittarsa ba za su iya samar da \u0257a ba ko da ya sadu da mace.<\/p>\n\n\n\n<p>10. Taurari likitoci &#8211; a yayin da muke magana game da abinda ya shafi lafiya, marubuciyar ta yi amfani da taurari likitoci sosai a cikin labaran. Misali, Dawud (Rayuwarmu), Jana (Akan So) Fawzan (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>11. Yawan ahali: a cikin dukkan labaran ta bayyana taurarin a matsayin wa\u0257anda suka fito daga cikin babban ahali mai mutane da yawa. Kuma dukkan taurarin suna son ahalin nasu sosai. Ko me ya faru duka suke \u0257unguma su tafi.<br>12. Abota ta ban mamaki a tsakanin taurari maza &#8211; misali; Altaaf da Wadata (Al\u0199alamin \u0198addara) Labeeb da Mamdud (Rayuwarmu) Fu\u2019ad da Lukman (Akan So) sai Yasir da Abdul\u0199adir (Abdul\u0199adir)<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\">\u0198ananan kamanceceniya<\/h3>\n\n\n\n<p>Kamar yadda na fa\u0257a, \u0199ananan kamanceceniyar da ke tsakanin wa\u0257annan labaran. Ga wasu daga cikinsu kamar haka;<\/p>\n\n\n\n<p>1. Yawan ambaton turare &#8211; duk labaran tana ba wa tuarare muhimmanci, musammaan ta hanyar nuna soyayyar taurarin labaran ga turaruka, har ma collections take nuna suna da shi.<\/p>\n\n\n\n<p>2. Taurarin da ke auren matan da ba cikakku ba ko wani abu makamancin hakan &#8211; misali; Rafiq da Tasneem (Al\u0199alamin \u0198addara, Labeeb da Zulfa (Rayuwarmu) sai kuma Aslam da Nuwaira (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>3. Samuwar matan kirki wa\u0257anda ke auren mazajen da ba na kirki ba &#8211; misali Labeeb da Ateefa (Rayuwarmu), Altaaf da Majida (Al\u0199alamin \u0198addara), Fu&#8217;ad da Sofi (Akan So) da kuma Abdul\u0199adir da Waheedah (Abdul\u0199adir).<\/p>\n\n\n\n<p>4. Samuwar yayye maza masu tsananin son \u0199anninsu mata da kishin su &#8211; misali; Labeeb da Zainab (Rayuwarmu) Haneef da Fa&#8217;iza (Akan so) Altaaf da \u0199anwarshi (Al\u0199alamin \u0198addara) Raafiq da \u0199anwarshi (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>5. Mata masu sau\u0199in kai da ha\u0199uri a zamantakewar aure &#8211; Jana (Akan So) Waheedah (Abdul\u0199adir) Ummi (Rayuwarmu) da Majida (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>6. Samun iyaye mata masu nagartar hali &#8211; Ummi (Rayuwarmu), Momma (Akan So) da kuma Nuri (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>7. Shan ruwa &#8211; a \u0199alla tana ambaton ruwa sau hamsin a cikin kowane labari.<\/p>\n\n\n\n<p>8. Yawan zuwa yin takeaway a waje &#8211; kusan a kowane littafi sai da ta fa\u0257i an je shagon siyayya an yi take away ko an siyo kayan ciye-ciye a \u0199alla sau goma. A cikin littafin Rayuwarmu kawai ta bayyana an yo take away sau goma sha biyu.<\/p>\n\n\n\n<p>9. Iya rawa a tsakanin jarumai &#8211; misali Labeeb (Rayuwarmu) da Altaaf Tafida (Al\u0199alamin \u0198addara).<\/p>\n\n\n\n<p>10. Kawo rayuwar ma&#8217;aurata da matsalolinsu &#8211; wannan wani abu ne da ta yi a cikin duk litattafan.<\/p>\n\n\n\n<p>11. Akwai kuma taurari masu takewa jarumai baya da suke komawa su zama kamar &#8216;yan&#8217;uwa &#8211; misali; Mamdud (Rayuwarmu), Yasir (Abdul\u0199adir), Wadata (Al\u0199alamin \u0198addara) da kuma Lukman (Akan So).<\/p>\n\n\n\n<p>12. Mata jarababbu masu masifa &#8211; Nuriyya (Abdul\u0199adir) Hajiya Beeba (Rayuwarmu).<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Shawarwari<\/h2>\n\n\n\n<p>Kamar yadda na fa\u0257a a baya, manufar wannan mu\u0199alar kawai shi ne ta za\u0199ulo kamanceceniyar da ke cikin labaran, kuma an yi hakan cikin nasara. To, shawarata ga marubuciyar wa\u0257annan litattafai da ma sauran marubuta bai wuce game da abubuwa guda biyu. Na farko dai samun kamanceceniya ba laifi ba ne matu\u0199ar an yi amfani da su ta hanyar da ta dace. Domin samuwar irin hakan na daga cikin abubuwan da ke kama wasu masu karatu, sannan yana daga cikin hanyoyin da ke bambance salon rubutunsa da na sauran marubuta. To amma in aka yi amfani da su kuma ta hanyar d na ta dace ba, zai iya zama tamkar maimaita abu guda kawai ake yi a cikin labarai masu yawa maimakon kawo sabon abu wanda shi ne ke nuna fasaha da zala\u0199ar marubuci.<\/p>\n\n\n\n<p>Abu na biyu kuma shi ne; kome kyawu da nagartar abu irin wannan da marubuci zai dinga maimaita shi a cikin labaransa wata rana za su gunduri masu karatu. Yana kuma iya sa wa su daina karanta littafin marubucin, domin za su ga tamkar yana \u0199o\u0199arin cusa musu wani abu ne da \u0199arfi da yaji shi ya sa yake yawan maimaita su. Kenan kauce wa yawan maimaita abubuwan a inda ya kamata shi ne ya fi.<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Gabatarwa Rubutu abu ne mai matu\u0199ar muhimmanci a wurin kowace irin al&#8217;ummar da take rayuwa a cikin wannan duniya. Irin muhimmancin da rubutu ke da shi ne ya sa kai tsaye ake danganta shi da ilimi, domin ya dace da shi \u0199warai da gaske. Duniyar rubutun labarai na \u0199asar Hausa ba ta da fa\u0257i sosai&hellip;&nbsp;<\/p>\n<div class=\"read-more-wrapper\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/kamanceceniya-a-cikin-wasu-labaran-lubna-sufyan\/\" class=\"button button-secondary\" rel=\"bookmark\">Read More &raquo;<span class=\"screen-reader-text\">Kamanceceniya a cikin wasu labaran Lubna Sufyan<\/span><\/a><\/div>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":4036,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"neve_meta_sidebar":"","neve_meta_container":"","neve_meta_enable_content_width":"","neve_meta_content_width":0,"neve_meta_title_alignment":"","neve_meta_author_avatar":"","neve_post_elements_order":"","neve_meta_disable_header":"","neve_meta_disable_footer":"","neve_meta_disable_title":"","neve_meta_reading_time":"","_jetpack_memberships_contains_paid_content":false,"footnotes":""},"categories":[58,45],"tags":[90,91],"class_list":["post-4003","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa","category-literary-critiques","tag-labaran-lubna-sufyan","tag-literary-critique"],"jetpack_featured_media_url":"https:\/\/efd8kbkoisy.exactdn.com\/blog\/wp-content\/uploads\/2023\/10\/Kamanceceniya-a-cikin-wasu-labaran-Lubna-Sufyan.jpeg?strip=all","jetpack_sharing_enabled":true,"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/4003","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/comments?post=4003"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/4003\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/media\/4036"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/media?parent=4003"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/categories?post=4003"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/tags?post=4003"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}