{"id":4052,"date":"2023-12-16T18:18:57","date_gmt":"2023-12-16T18:18:57","guid":{"rendered":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/?p=4052"},"modified":"2023-12-16T18:19:57","modified_gmt":"2023-12-16T18:19:57","slug":"sharhin-littafin-rayuwarmu-na-lubna-sufyan","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/sharhin-littafin-rayuwarmu-na-lubna-sufyan\/","title":{"rendered":"Sharhin littafin &#8216;Rayuwarmu&#8217; na Lubna Sufyan"},"content":{"rendered":"\n<p>Sunan Littafi: <strong>Rayuwarmu<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Marubuciya: <strong>Lubna Sufyan<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Inda Aka Buga Littafi: <strong><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/\">Bakandamiya Hikaya<\/a><\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Shekarar Bugu: <strong>2022\/23<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Yawan Babi: <strong>51<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Mai Sharhi: <strong>Jamilu Abdulrahman (Haiman Raees)<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>Manufar Sharhi: <em>Bun\u0199asa Harshen Hausa da ciyar da adabi gaba<\/em>.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Gabatarwa<\/h2>\n\n\n\n<p>Rayuwar duniyar nan cike take da \u0199alubale iri-iri. Yadda duk mu ke tunanin mun gama ganin kowane shafi na rayuwa, matu\u0199ar ba mutuwa muka yi ba, to akwai wani shafin a gaba. Wannan littafi na &#8216;Rayuwarmu&#8217; \u0257auke yake da madubin dubawa zuwa ga yadda rayuwarmu ta kasance a baya, yadda take a yanzu da kuma izna zuwa ga yadda za ta kasance a nan gaba.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Tarihin marubuciyar a ta\u0199aice<\/h2>\n\n\n\n<p>Marubuciya Lubna Sufyan an haife ta ne a \u0199aramar hukumar Ingawa da ke birnin Katsina. Fitacciyar marubuciyar ta fara karatun addini tun tana \u0199arama kuma ta yi karatunta na Firamare ne a garin Katsina, daga baya ta koma garin Kano inda ta yi karatun Sakandire har ta gama. Bayan ta gama ne sai ta koma Katsina in da ta yi karatun Diploma a \u0253angaren zanen taswirar gidaje. Daga baya kuma ta ci gaba da karatu a mataki na gaba, wato babbar Diploma wadda da turanci ake ce wa Higher National Diploma (HND) a Kaduna.<\/p>\n\n\n\n<p>Kamar mafi yawancin marubuta, marubuciyar ita fara rubuce-rubuce ne tun tana makaranta, kuma ta kasance \u0257aya daga cikin fitattun marubutan online na wannan zamani, domin abu ne mai wuya ka fa\u0257i sunanta a duniyar marubuta da makarantan wannan zamani ba a samu wanda ya santa ba. Zuwa yanzu marubuciyar ta rubuta litattafai sama da guda goma sha \u0257aya. Wasu daga cikin litattafan da ta rubuta sun ha\u0257a da;<\/p>\n\n\n\n<p><em>Rai Da \u0198addara<br>Wata Bakwai<br>Akan So<br>Tsakaninmu<br>Abdul\u0199adir<br>Mijin Nobel<br>Martabar Mu<br>Al\u0199alamin \u0198addara<\/em> da dai sauransu.<\/p>\n\n\n\n<p>Har&#8217;ilayau kuma, marubuciyar ta kasance mai son girke-girke ce sosai. Kuma baya ga rubutu, marubuciyar tana yin fassara daga harshen Turanci zuwa Hausa, wannan aiki na fassara ne ma ya zama sanadin yin aikinta da kamfanoni da \u0199ungiyoyin gwagwarmaya masu zaman kansu a lokuta daban-daban a kuma kan batutuwa iri daban-daban kamar su GiveNorthEducation, WomenInArewa, WomenInFinance da dai sauransu. Sannan kuma, marubuciyar ta sha yin aiki da makarantun Islamiyya da bloggers wajen fassara musu aiyukansu. Haka kuma \u0199wararra ce wajen ha\u0257a \u0257uwatsun \u0199awa na adon mata. Sannan kuma tana aikin juyar da bayanan murya zuwa rubutu (transcription). A ta\u0199aice dai, duk in da aikin rubutu yake, to a nan marubuciyar ta fi \u0199arfi.<\/p>\n\n\n\n<p>Marubuciyar kuma na \u0257aya daga cikin mambobin \u0199ungiyar marubuta na Fikra Writers Association. Lubna Sufyan ta yi aure a shekarar 2022, kuma tana zaune ne a garin Kaduna yanzu haka tare da mijinta.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Labarin a Ta\u0199aice<\/h2>\n\n\n\n<p>Rayuwarmu labari ne akan wani babban ahali da ya \u0199unshi mutane da dama a cikinsa. Ko da yake kusan kowa da ke cikin ahalin mutumin kirki ne, hakan ba ya nufin babu saniyar ware a cikinsu, kuma hakan ba ya nufin ba za su fuskanci \u0199alubale ba a rayuwarsu.<\/p>\n\n\n\n<p>A daidai lokacin da rayuwa ke yi wa su Dawud da\u0257i duk da \u0199arancin wadatar arzi\u0199i da ta same su, kwatsam sai gashi wata mata ta yi wa rayuwarsu dirar mikiya ta hanyar \u0199wallafa ranta akan mahaifinsu wato Auwal. A dalilin wannan mata ne suka tsinci kansu a cikin tashin hankalin da ko a mafarki basu ta\u0253a tsammanin shiga cikin irinsa ba. Hakan ya sa Dawud \u0257aukar nauyin da bai shirya ba a kafa\u0257ar shi wadda ita ma neman wanda za ta jingina da shi take yi.<\/p>\n\n\n\n<p>Labeeb jarumin fim ne wanda ya yi shura. Baya ga wannan, ya fito daga gidan ku\u0257i ta yadda ba za ka ta\u0253a tunanin yana da damuwa ba a rayuwarsa. Sai dai kash, ya fa\u0257a cikin rayuwar shaye-shaye da neman mata. Kwatsam kuma sai \u0199addarar rayuwa ha\u0257a shi da Mamdud wanda ya \u0257auka a matsayin aboki kuma \u0257an uwanshi. Abinda bai sani ba shi ne, zuciyar Mamdud a koda yaushe \u0199una take yi bisa ganin yadda komai ke zuwa mishi da sau\u0199i sakamakon ku\u0257i da kuma baiwar shura da Allah ya yi mishi. Abin da Mamdud bai fahimta ba shi ne, duk iya farincikin da Labeeb ke bayyanawa a fili, damuwar da ke cikin rayuwarshi ta fi wannan. Rikici da turka-turkar da ke tsakaninsu ba ta fito fili ba sai da \u0199addara ta ha\u0257a su son mace \u0257aya.<\/p>\n\n\n\n<p>Labeeb shi ne wanda ya zamo bangon da su Dawud suka jingina da shi a lokacin da suka shiga halin matsi na rayuwa. Wannan dalili ne ya sa suke ganin girman shi sosai. Kwatsam kuma sai ga wani mummunan al&#8217;amari ya ratso ta cikin wannan kyakykyawar mu&#8217;amala tasu. Yadda al&#8217;amarin ya fara, yadda ya ci gaba da faruwa da kuma yadda ya \u0199are wata tafiya ce wadda za ta ta\u0253a zuciyar duk wanda ya karanta wannan labari.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Jigo<\/h2>\n\n\n\n<p>Duk da cewa soyayya ta yi tasiri babba wajen ginuwar labarin, kai tsaye ba zai yiwu a ce soyayya ce jigon wannan labari ba. Babu ko tantama, babban jigon wannan labari shi ne &#8216;\u0198alubalen Rayuwa.&#8217; Mai karatu zai yarda da ni akan wannan batu da zarar ya karanta babin farko na wannan labari kawai ba tare da ya yi nisa ba. Kuma tun daga nan har zuwa \u0199arshen labarin taurarin cikinsa ba su daina fuskantar \u0199alubale ba. Na da\u0257e ban karanta wani labari wanda taurarinsa ke fuskantar \u0199alubale da yawa irin na wannan littafi na Rayuwarmu ba . Kuma ta wannan hanya ce marubuciyar ta yi ta \u0199o\u0199arin fayyace jigon tare da \u0199arfafa shi a kowane babi na littafin.<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\">Warwarar Jigo<\/h3>\n\n\n\n<p><strong>Ga wasu daga cikin hanyoyin da marubuciyar ta bi wajen warware wannan jigo:<\/strong><\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 A babi na farko ta fara hasko wa mai karatu irin \u0199alubalen da ke biyayyar manya da \u0199ananan taurarin labarin irin su Labeeb, Dawud, Zulfa, Mardiyya ds. Haka ta tafi da wannan salo har zuwa babi na biyu inda daga na uku kuma ta fara komawa baya domin ta bayyana wa mai karatu asalin yadda al&#8217;amuran suka fara afkuwa.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Mahaifin Dawuda, wato Auwal ya samu \u0199alubalen kora daga aiki wanda hakan ya kawo canji babba a zamantakewar shi da iyalinsa. Matsi na rayuwa ya sa shi shiga neman aiki fafur, yayin da matarsa Aisha (Ummi) ita ma hakan ya sa dole ta kakka\u0253e kwalinta na NCE ta nemi aikin koyarwa. (Babi na 30)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Hajiya Beeba ta samo wa Auwal aiki, sai dai kuma a \u0199asan zuciyarta son shi take kamar ta yi hauka, yayin da shi kuma ba ta ita yake ba. Hakan ya sa ita ma ta zagara wajen ganin ta shawo kanshi. Saboda matsin lamba da Hajiya Beeba ke mishi ya sa dole Auwal ya ajiye aikin shi. Ita kuma Ummi hakanan ta siyar da filinta na gado ta bashi ku\u0257in domin su biya ku\u0257in makarantar yara sauran kuma ya ja jari da su. A \u0199arshe dai sai ga Hajiya Beeba a wurin boka ta je neman asirin da za ta mallake zuciyar Auwal \u0257in. (Babi Na 4-5)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Asirin da Hajiya Beeba ta sa aka yi wa Auwal ya fara aiki. Hakan ya kawo mummunan sauyi a tare da shi. Daga \u0199arshe dai sai da aka \u0257aura musu aure da ita wanda hakan ya jefa rayuwar Ummi da &#8216;ya&#8217;yanta a cikin matsanancin hali, ciki har da yi wa &#8216;yarta (Sajda) asiri ta shiga wani yanayi mai kama da hauka. Kamar fa hakan bai isa ba kuma sai da ya sake ta, ya koreta da ciki tare da cewa ba nashi ba ne cikin, kuma sauran yaran ma ba shi da tabbaci akansu. (Babi na 6-9)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Bayan Labeeb ya basu wurin zama, ba a jima ba kuma sai Ummi ta mutu a yayin haihuwar Khateeb. A sanadiyar hakan ne rayuwa ta sake jagule musu. Haka suka yi ta tafiyar da rayuwar har tsawon shekaru bakwai. A daidai wannan lokacin shi kuma Labeeb Mummy ta za\u0253a mishi wadda zai aura ba tare na da yasan ko wacece ba balle a yi maganar soyayya. Shi ma Dawuda a cikin wannan hali ne ya ha\u0257u da Yumna a wani yanayi mai ban mamaki har soyayya ta \u0199ullu a tsakaninsu, sai dai kuma ita ma tana da nata \u0199alubalen da take fuskanta. Kwatsam kuma sai ga Auwal ya dawo cikin rayuwarsu da nufin su dawo wajen shi da zama. Ana cikin haka ne kuma Sajda ita ma ta mutu a sanadiyar gobarar da iskar gas ta haifar yayin da take girki. (Babi na 10-16)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Rikicin ya sake \u0253allewa ne lokacin da Labeeb ya gano cewa Zulfa na \u0257auke da cikin Mamdud. Maimakon ya bayyana gaskiyar magana kawai sai ya tara danginsu gaba \u0257aya ya ce cikin nashi ne domin ya kare ta daga fuskantar \u0199alubalen da za ta shiga. Ana cikin haka kuma sai ga wani yaro an zo da shi wai na Labeeb \u0257in ne alhali bai san da shi ba. Wannan lamari fa shi he ya jawo \u0253allewar sabon rikici a tsakanin shi da matarshi wadda ke da tsohon ciki a daidai wannan lokacin da kuma rashin fahimta a tsakanin shi da sauran &#8216;yan uwanshi. Wa\u0257annan da ma wasu misalai masu yawa irinsu su ne suka taru suka tabbatar da \u0199alubalen rayuwa a matsayin jigon wannan labari<\/p>\n\n\n\n<p>Bayan wannan babban jigo da na yi bayani, marubuciyar ta yi amfani da wasu \u0199ananun jigogi masu yawan gaske wa\u0257anda su ne suka ha\u0257u suka goya wa labarin baya ta hanyar koyar da darussa da dama a cikin wannan labari. Ga wasu ka\u0257an daga cikinsu kamar haka:<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna illar biye-biyen mata ba aiki ba ne nagari. Kuma marubuciyar ta nuna mana haka a wurare da dama a cikin labarin, musamman akan rayuwar Labeeb da Mamdud.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Wani ma bai ta\u0253a sanin ana iya yi wa namiji fya\u0257e ba, amma a wani yanayi irin wanda ba a saba gani ba, sai ga shi an nuna wa mai karatu irin yadda fya\u0257e ke ta\u0253a rayuwar maza idan aka yi musu. Kamar yadda Labeeb ke bayyana wa Mamdud, &#8220;Ba za ka gane ba&#8230;.. Kullum da daddare sai ta shigo \u0257akinaa&#8230;.. She&#8230; She is so big&#8230;.. She raped me&#8230;. Mummy ba ta damu ba, ba ta nan&#8230; Kullum kullum Mamdud, ba zai sake faruwa ba, ba mace bace za ta \u0253ata ni&#8230;.. Ni ne zan \u0253ata ta&#8230;. Ba zai sake faruwa ba&#8230;..&#8221; Kuma wannan ya fito da illar barin yara a hannun &#8216;yan aikin gida. (Babi na 21)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An yi nuni zuwa ga irin ka\u0257aicin da irin yaran da iyayensu ba sa samun lokacinsu kan shiga. Musamman irin yadda su ke kewar iyayen nasu. Misali, inda marubuciyar ta ce, &#8216;Su dukkan su magana suke yi a lokaci \u0257aya. Babu mai bari wani ya gama, duka so suke ta basu hankalinta. So suke ta saurare su. Shi kanshi Labeeb da ke tsaye yana binsu da kallo hakan yake so.<br>Hira yake so su yi da Mummy ko na minti sha biyar ne, su zauna waje \u0257aya, su yi labari, ya ji muryarta, dariyarta. Ba su Zainab ka\u0257ai ke bu\u0199atar kulawarta ba. (Babi na 22)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Ba zai barmu ba? Ba zai dinga tafiya kamar Mummy ba?&#8221; (Babi na 21)<\/p>\n\n\n\n<p>Na gaji da zama ni da TV, na gaji da kallo, ba wanda ya damu da ni, not Mum, not Dad and not you, ba za ka gane ba saboda kana da Yaya Anees&#8230;&#8230;&#8230;just&#8230;. Get out of my room.&#8221; (Babi na 21)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An yi izna zuwa ga rashin dacewar shiga irin wadda ba ta dace ba. Misali, Mutane ne cike, maza da mata, Musulmai da kiristoci da ba za ka gane bambancin su ba, saboda kusan shigar tasu iri \u0257aya ce, kuma sun cure waje \u0257aya. (Babi na 22)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An yi nuni bisa irin yadda makauniyar soyayya ke jawo matsala. Misali, &#8216;In don ta Mummy ne da wahala in basu gama maganar har da Dadyn su ba. Son da Dady yake mata ba ya barinshi ya ga kuskuren hukuncin da duk za ta yanke akansu ko da akwai shi. (Babi na 24)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An koyar da mu darasi a likitance a wurare da dama na littafin. Misali, &#8216;Ni ba hatsari na yi ba&#8230;ina da lalurar PCOS (Polycystic ovary syndrome) ba lallai in haihu ba&#8230; Chances \u0257in ka\u0257an ne. (Babi na 51)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An koyar da muhimmancin sadaukarwa da alfanunta. Misali, dubi yadda labeeb ya ba wa Mamdud kyautar \u0257ansa da kuma inda yake cewa, &#8220;Na san ba daga jikinka ya fito ba&#8230; Na san babu jininka a jikinshi&#8230;sai dai zuciyarshi yanzun take girma&#8230; Soyayyar mahaifi a wajenshi yanzun za ta fara tasiri.<br>Ba zai gane banbancin jinin ba&#8230; \u0198aunar kawai zai fahimta&#8230;Allah ya sa zai iya rage maka ra\u0257a\u0257in abinda ka rasa da wanda ba za ka samu ba&#8230;&#8221; (Babi na 50)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna tsantsar soyayyar da ke tsakanin ma&#8217;aurata ta hanyar nuna misali a zamantakewar Labeeb da Ateefa, Dawud Da Yumna, Abba da Ummi ds.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An hasko mana irin yadda mutane masu halin Mummy suke tunani. Kamar yadda marubuciyar ta ce,<br>&#8216;Ta gama tsara rayuwarta, ta gama hango lokacin da za ta ajiye kasuwancinta ta zauna da yaranta.<br>Lokacin da za ta \u0199aunace su, ta \u0257auka tana da dukkan lokacin da take bu\u0199ata a hannunta. Tun shekaranjiya ta gane ita ba komai bace ba. (Babi na 36)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna irin yadda hassada da rashin tawakkali ke tasiri wajen gur\u0253ata wa mutum tunaninsa,<br>&#8216;Gyara zamanshi ya yi yana kallon Labeeb na cashewa abinshi, sun caku\u0257e waje \u0257aya har da mata.<br>Hannuwan wata tsaf a \u0199ugun Labeeb \u0257in , bai ko nuna hakan ya dame shi ba. Wasu lokutan har mamaki yakan ba Mamdud, komai yana yi kamar abin ya zo mishi natural ne ba tare da koyo ba. Abin na bashi takaici ba ka\u0257an ba. (Babi na 30)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Sau da dama yanke hukunci cikin fushi kan sa mutum yin da na sani. Kamar yadda marubuciyar ta ce, &#8216;Mamdud ke tuna kalaman da ya yi wa Labeeb \u0257in, furuci ne da ya yi cikin fushi, ba don yana nufin abinda ya ce ba. Sai dai ya riga da ya zo akan ga\u0253a.<br>Ya furta, Allah kuma ya \u0199addara faruwarshi, ya san ya ta\u0253a abinda ya fi kusanci da Labeeb. (Babi na 34)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna irin yadda wasu matan ke jefa &#8216;ya&#8217;yansu cikin bala&#8217;i a gidan aure ta hanyar yi musu mummunar hu\u0257uba.<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Maza irin El-labeeb Maska babu kalar matan da basu gani ba. Ba wani daraja za ki yi a idanuwanshi ba.<br>Ki tabbatar kin kwashi rabonki kafin ya gaji da ke. Ku\u0257i ne zai shigar da ke gidanshi, ba matsala ba ne su a wajen shi. Ki tabbatar kin cika account \u0257inki kafin ki dawo min.&#8221; (Babi na 25)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Ki tabbatar kin kwashi rabonki kafin ya gaji da ke. Ku\u0257i ne zai shigar dake gidanshi, ba matsala bane su a wajen shi. Ki tabbatar kin cika account \u0257inki kafin ki dawo min.&#8221; (Babi na 25)<\/p>\n\n\n\n<p>Da kuma inda ta ce,<br>What? Shi \u0257in banza, aure zaman kurkuku ne da zai kafa miki sharu\u0257\u0257a haka. Waye El-Maska \u0257in? Me ya tara? Ki tafi makaranta abinki. Kin ji ni, sai ka ce ba jinina ba za ki zauna kina ma namiji kuka.&#8221; (Babi na 26)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Soyayya a tsakanin &#8216;yan uwa ta taka muhimmiyar rawa wajen ginin wannan labari. Misali, an nuna yadda \u0257an uwa kan ji canjin yanayi a jikinshi yayin da wani abu ya faru da makusancin shi.<br>&#8220;Innalillahi wa inna ilaihir raji&#8217;un.&#8221;<br>Ta fa\u0257i da ya maida hankalin Ishaq kanta.<br>&#8220;Lafiya Zainab?&#8221;<br>Idanuwanta cike da hawaye ta ce,<br>&#8220;Nima ban sani ba&#8230; Wani abu ya faru&#8230; Don Allah ka kaini gida&#8230;&#8221; 36 nuni da girman kusancin &#8216;yan uwa.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna burin da iyaye kan ci wajen ganin &#8216;ya&#8217;yansu sun zama wani abu. Misali,<br>&#8220;Kasan yawan ku\u0257in da ke account \u0257inka kuwa? Kasan garuruwan da fina-finanka suke zagayawa? Kana da fans all over Nigeria, wa ya sani ko harda wajenta ma.&#8221; (Babi na 21)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An nuna muhimmancin aure da irin nutsuwar da ake samu a cikinsa. Dubi yadda marubuciyar ta bayyana wannan batu a cikin zance mai sau\u0199in fahimta, &#8216;Har mamakin kalar control \u0257in da ya samu yake yi. Ya \u0257auka aure ba zai ta\u0253a zamar mishi mafita ba sai yanzun ya ga banbancin hakan. (Babi na 26)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Wula\u0199anci ba shi da kyau, kuma marubuciyar ta nuna irin yadda rayuwa kan juya ka koma neman wani abu a wurin wanda ka wula\u0199antata. Kamar dai yadda marubuciyar ta ce, &#8220;Ba sai na fa\u0257a maka ba, kasan yadda na raina &#8216;yan \u0199auye. Ciki har da wasu daga dangin Mamana, kasan yadda nake wula\u0199anta duk wani da ke \u0199asa da ni. Nice yau zuciyata take dokawa \u0257an Maigadi. &#8221; (Babi na 33)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Mutuwa da darasin da ke biyo bayanta sun taka muhimmiyar rawa a cikin wannan labari. Duniya yadda marubuciyar ta bayyana halin da Labeeb ya shiga bayan mutuwar Sajda, &#8216;tun bayan rasuwar Sajda sai da ya kusan kwana arba&#8217;in bai sha komai na maye ba. Inda duk yasan zai iya zuwa ya samu temptation baya zuwa. (Babi na 27)<\/p>\n\n\n\n<p>Da kuma inda yake cewa, &#8216;Kamar wasa na rasa Arif&#8230; Ba zai dawo ba. Bazan sake asarar lokaci na ina fa\u0257a da wani ba&#8230; Bamu da su da yawa&#8230; Babu&#8230; Babu lokaci mai yawa a rayuwarmu.&#8221; (Babi na 37)<\/p>\n\n\n\n<p>Dubi kuma yadda Mummy ta shiga cikin tashin hankali bisa mutuwar Arif, &#8216;Ya za a yi ya ce mata Arif ya rasu. Ta yaya? Me ya same shi? Babu yadda za a yi ya rasu. Duka lokacin rayuwar shi nawa ta samu? Bata ma san abincin da ya fi so ba, ba za ta tuna sa&#8217;adda suka yi maganar awa \u0257aya da Arif ba. Ba ta gama sanin \u0257anta ba. Ba ta ko samu lokacin da za ta so shi yadda ya kamata ba. Ba yanzun ba, Arif ba zai barta yanzun ba ta nuna mishi kalar \u0199aunar da take mishi ba. (Babi na 36)<\/p>\n\n\n\n<p>Sai kuma inda marubuciyar ta ce, Arif yake kallo a kwance da idanuwanshi, a zuciyarshi yanayin shi yake kallo da rayuwar shi.<br>Shiru-shirun shi, murmushin shi, yanayin maganar shi. Cikin kunnuwan shi yake jin yadda yakan kira sunan shi, yanayin yadda yakan saka su dariya in har yai magana. (Babi na 36)<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Salo da Sarrafa Harshe<\/h2>\n\n\n\n<p>Marubuciyar ta baje basira \u0199warai da gaske wajen ba da labarin wannan littafi. Saboda ta yi amfani da salo iri-iri kuma duk masu jan hankali ne da burgewa wajen isar da sa\u0199on labarin a sau\u0199a\u0199e.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Salon Koyarwa da Nuni: Marubuciyar ta yi amfani da wannan salo sosai a cikin wannan littafi domin isar da sa\u0199onta. Ga ka\u0257an daga ciki,<br>&#8216;Wajen bakinta ta kai kofin ruwan shi tana yin addu&#8217;a a ciki kafin ta ajiye a \u0199asa, ta saka hannunta cikin kofin tare da yin Bismillah ta \u0257ibo. Murza shi ta yi tana shafa wa Sajda a saman kanta, sannan ta \u0199ara \u0257ibowa ta shafa mata a fuska, da hannu \u0257aya ta ri\u0199e kan Sajda, ta \u0257ibo ruwan ta bu\u0257e bakinta ta \u0257ura mata shi.<br>Furzo shi waje Sajda tayi, saitin kanta ta tsugunna. Cikin kunne take mata addu&#8217;o&#8217;i har jikinta ya soma sanyi. A hankali ta bar ihun da take yi.<br>Sake \u0257iban ruwan tayi ta shafa mata tun daga kanta har wuyanta, sannan ta kar\u0253eta daga hannun Dawud \u0257in. (Babi na 13)<\/p>\n\n\n\n<p>Da kuma inda ta ce, &#8216;Dutsen da Anees ya samo wa Mamdud ya yi taimama da shi ya mi\u0199a mishi, ya tsaya ya yi ya ja gadon yana juya shi yanda zai fuskanci gabas kamar yadda suka yi mishi \u0257azu tunda babu dama ya motsa \u0199afarshi. (Babi na 45)<\/p>\n\n\n\n<p>Salon Barkwanci\/ Nisha\u0257i: &#8220;Mami kinsan jiya da na biyo kasuwa sai da na ga wajen da kike cefane.&#8221;<br>&#8220;Halan ka biyo ta layin &#8216;yan doya.&#8221;<br>Dawud ya fa\u0257i yana kallonshi. Sai da ya ha\u0257iye abincin da ke bakinshi ya \u0199ara wani sannan ya juya ya \u0257an kalli Dawud \u0257in.<br>&#8220;Wallahi kamar ka sani, ta nan na biyo da zan dawo&#8230;..&#8221; (Babi na 14)<\/p>\n\n\n\n<p>Da kuma inda marubuciyar ta ce,<br>&#8220;Kinsan Allah Aljanu fa, kin ga an wanke kayan wanke wanken dana \u0253ata, jiya kuma na ga wata yarinya a gidan da&#8230;&#8221;<br>Dariya Labeeb ya ji data sa shi juyawa, Asad ne a tsaye.<br>&#8220;Aljanun ne suka wanke kwanoni&#8230;&#8221; (Babi na 27)<\/p>\n\n\n\n<p>Salon Tafiyar Kura: An yi amfani da salon tafiyar kura ne a cikin wannan littafi, inda marubuciyar ta fara ba da labarin daga tsakiya sannan ta ci gaba da warware shi a hankali a hankali ta hanyar komawa baya ta kawo wani batu sannan ta dawo ta ci gaba daga baya kuma ta sake komawa ta kwance wani a baya kafin ta kuma dawowa ta ci gaba. A iya cewa ma ta kwashe kusan rabin littafin ne wajen warware matsalolin da ke \u0199unshe cikin labarin ta wannan hanya ko salo. Kuma hakan ya taimaka wajen fayyace wa mai karatu wasu abubuwan masu sar\u0199a\u0199iya ba tare da bayyana yadda \u0199arshen littafin zai kasance ba.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Sarrafa Harshe: Marubuciyar ta yi amfani da Karin Magana da kuma kalmomin azanci, hikima, tsima jiki, sa tausayi, kwantar da hankali da kuma gyaran tunani duk a cikin wannan littafi. Wani lokaci ma sai mai karatu ya ji kamar zaunar da shi aka yi ana mishi nasiha game da yadda ya kamata ya tunkari rayuwa da \u0199alubalen da ke cikinta. Ga ka\u0257an daga ciki,<\/p>\n\n\n\n<p>Sauka ba ya nufin \u0199arshen karatunka na Islama, yana nufin ka dai samu ci gaba ne babba a hanyarka ta neman ilimi, don kogi ne, yana da fa\u0257i, sai dai ka yi iya yinka. (Babi na 14)<\/p>\n\n\n\n<p>Allah ba ya barin wani don wani. (Babi na 50)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Me na fa\u0257a maka? Tsintacciyar mage ba ta mage dama&#8230; Wanda ka tsamo daga rana zuwa inuwa gashi nan ya turaka tsakiyar rana har wuta ya kunna maka!&#8221; (Babi na 42)<\/p>\n\n\n\n<p>Kowanne \u0257an Adam a rayuwarshi ba zai rasa abu \u0257aya mummuna ba. Ba zai rasa wani laifi ko aibu babba ba. Saboda me za ka danne naka ka nuna wa wani \u0257an yatsa?<br>(Babi na 41)<\/p>\n\n\n\n<p>Damuwa na \u0257aya daga cikin abubuwan da rayuwa ta \u0199unsa, babu wani farin ciki da yake dawwamamme kamar yadda babu damuwar da take dawwamammiya.<br>(Babi na 45)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Ba muna zama da juna ba ne don mun manta laifukan da muka yi wa juna. Muna zama da juna ne don mun yafe&#8230; In babu yafiya duka za mu rasa kanmu ne.<br>Akwai laifukan da za mu aikata wa\u0257anda da babu yafiya ba zamu iya kallon kawunanmu a mudubi ba. Akwai sau\u0199i mai girma a cikin yafiya&#8230;ka yafe duk sa&#8217;adda ka samu damar hakan.&#8221;<br>(Babi na 50)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Idan har ba ka daina jin tsoron me mutane za su ce akan abin da ya wuce a bayanka ba, zai ci gaba da zama barazana a tare da kai . Abinda ya faru da kai naka ne&#8230; Akanka ya faru&#8230; Ka kar\u0253e shi. Zai daina tsorata ka.&#8221;<br>(Babi na 51)<\/p>\n\n\n\n<p>&#8220;Ba komai da ka ke so ba ne ka ke samu a rayuwarka Sajda. Lokuta da dama abubuwa suna faruwa da ba ka sanin dalilin su.<br>(Babi na 13)<\/p>\n\n\n\n<p>A \u0199ar\u0199ashin duk wa\u0257annan kuma, marubuciyar ta yi amfani da sassau\u0199ar Hausa wajen rubuta wannan labari. Sai dai kamar yadda mai karatu zai gani, ta yi amfani da kalmomin turanci sosai a cikin labarin wa\u0257anda duba da yanayin Taurarin Labarin da irin rayuwarsu ba a ce kai tsaye suna da matsala ba sai dai akwai \u0199ofofin gyara.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Zubi da Tsari<\/h2>\n\n\n\n<p>Labarin Rayuwarmu cike yake da sar\u0199a\u0199iya da fa\u0257i tashi. Ba wai kuma don rashin salo ko tsaurinsa ba. Sai don yadda yake cike da \u0199warewa ta yadda komai hasashen mai karatu ba zai iya hasaso abinda zai faru a gaba ba.<\/p>\n\n\n\n<p>Marubuciyar ta gabatar da zubi da tsarin littafin &#8216;Rayuwarmu&#8217; daidai yadda ya dace da yanayin halayyar taurarin littafin ta yadda mai karatu zai \u0199agara ya ga yadda za ta kaya, tare da jefo ba-zata a wasu lokutan. Ta kuma yi amfani da nau\u2019o\u2019in mutuwa wajen kawar da wasu taurarin wa\u0257anda ci gaba da kasancewarsu, za ta haramta warware sar\u0199a\u0199iya cikin littafin. Misali, an kashe taurari irin su Ummi, Sajda da kuma Arif.<\/p>\n\n\n\n<p>Marubuciyar ta zayyana labarin Rayuwarmu ne a cikin littafi \u0257aya duk da cewa ya \u0257an yi tsayi. Sai dai irin yadda labarin ke da shiga zuciya da kama tunanin mai karatu, kana iya shafe tsawon lokaci ba tare da ka ankare ba. Sannan an nuno yadda rayuwar jaruman ta fara a lokacin da babu wayar hannu irin ta zamani har zuwa lokacin da akwai.<\/p>\n\n\n\n<p>An kuma yi tsallaken lokaci a cikin labarin domin bayyana abin da ya faru a wasu lokuta na rayuwar taurarin labarin.<\/p>\n\n\n\n<p><em>Misali<\/em><\/p>\n\n\n\n<p>Bayan shekaru uku (Babi na 21)<br>Bayan Wata \u018aaya (Babi na 03)<br>Bayan Wata Biyu (Babi na 04)<br>BAYAN WATA BAKWAI (Babi na 08)<br>BAYAN SHEKARA BAKWAI (Babi na 13)<\/p>\n\n\n\n<p>Gaba \u0257aya labarin ya faru ne a cikin garin Kaduna. Sai kuma wani \u0253angare da ba kasafai aka cika bayani akai ba, shi ne wuraren da Labeeb ke tafiya domin gudanar da ayyukan shi.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Ba\u0257oki Na gaske: &#8220;A gidanmu na kar\u0253o, zam zam ne da addu&#8217;oi. Komai ya kusan zuwa \u0199arshe In sha Allah.&#8221; (Babi na 35)<br>Kuma lallai bayan wani lokaci al&#8217;amuran duk sun faru.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Ba\u0257oki Na Giri: An nuna gabatowar tashin hankali bisa soyayyar Mardiyya da Danish amma ba a yi wani bayani gamsasshe ba. An kuma nuna matsalar da Yumna take ciki babba ce amma ba a fa\u0257a\u0257a bayanin ba.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 \u018aarsau Na Mamaki: &#8220;I was so so stupid&#8230;ya aka yi ban gane ba?&#8221;(Babi na 48)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 \u018aarsau Na Tausayi: Zafin da yake ji yanzun ya girmi hassadar da ta baibaye zuciyarshi har ta kawo shi inda yake tsaye yanzun. Ya kasa \u0257aga idanuwan shi ya kalli Labeeb. (Babi na 35)<\/p>\n\n\n\n<p>Kallon su yake da wani yanayi a \u0199irjinshi. Dukkansu suna jin \u0199aunar junansu, suna jin yadda suka ha\u0257a jini.<br>Ko sau \u0257aya, ko sau \u0257aya a rayuwarshi yake so ya ji ya kalar sha\u0199uwa irin wannan take. Ya za ka ji ka kalli mutum kasan jini iri \u0257aya ne a jikinku. (Babi na 28)<\/p>\n\n\n\n<p>Wasu hawaye ne masu \u0257umi suka tarar wa Mamdud a idanuwa, da ka ga yanayin da Arif yake maganar kasan a wahalce yake yinta. Abinda yake ji bai hana shi ro\u0199ar mishi gafarar su Labeeb ba.<br>Bayan baisan me ya yi ba, wannan \u0199aunar son zuciya ya ja mishi rasawa. \u0198aunar da yake da ya\u0199inin ko &#8216;yan uwan da suka ha\u0257a jini da shi ba kowa zai so shi kamar Arif ba. (Babi na 35)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 \u018aarsau Na Tsoro: Yana zama ya ji ya zauna kan wani abu kamar mutum. \u0198ara ya saki yana mi\u0199ewa. Ya tsorata ba ka\u0257an ba. Ba arzi\u0199i ya lalubi switch \u0257in \u0257akin ya kunna. (Babi na 28)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 \u018aarsau Na Murna: &#8220;Tsarki ya tabbata ga Ubangijin da ke da Iko akan komai da kowa. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin da yake kyauta ga wanda Ya so. Tsarki ya tabbata ga Ubangiji&#8230;&#8221; (Babi na 51)<\/p>\n\n\n\n<h3 class=\"wp-block-heading\">Hoton Zuci<\/h3>\n\n\n\n<p>Kusan kowane shafi ko babi na littafin ka bu\u0257e kana karantawa sai ka dinga gani tare da jin kamar a gabanka abin ke faruwa saboda irin yadda marubuciyar ke bayani filla-filla.<\/p>\n\n\n\n<p><em>Misali;<\/em><\/p>\n\n\n\n<p>\u0198wan\u0199wasawa suka ji ana yi, tun kafin Dawud yai magana Zulfa ta tashi da gudu ta bu\u0257e tana \u0199an\u0199ame shi. \u018aaga ta ya yi da fa\u0257in,<br>&#8220;Zulfa ta ba ta kowa ba.&#8221;<br>Dariya ta kama yi tana \u0253oye kanta a jikin wuyanshi. A dole kunya take ji.<br>&#8220;Yaya ka sauke ni.&#8221;<br>Sake ri\u0199eta dam Labeeb yayi.<br>&#8220;Kin girma yanzun ko. Na \u0199i in sauke ki \u0257in.&#8221;<br>Harbe-harben \u0199afa ta dinga yi. Jin tana neman kayar da su yasa Labeeb ya sauke ta yana ja mata kunnuwa.<br>&#8220;Shikenan yanzun Zulfan nan ba tawa bace ni ka\u0257ai.&#8221;<br>Turo baki tayi.<br>&#8220;Taka ce mana.&#8221;<br>Ya girgiza mata kai yana ha\u0257e fuska. Shirin kuka ta fara.<br>&#8220;Da wasa nake fa. Waye ma zai ce zulfan shi gani.&#8221; (Babi na 13)<\/p>\n\n\n\n<p>Tana ficewa daga \u0257akin ya ga ta ja \u0199ofar ya diro daga kan kujerar ya \u0257auki kayanshi da ke watse a \u0199asa, dogon wandon kawai ya saka da singlet, rigarshi a hannu ko takalmi bai saka wa \u0199afarshi ba ya bita. (Babi na 23)<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Taurarin Labari<\/h2>\n\n\n\n<p>Rayuwarmu littafi ne da ke \u0257auke da taurari masu tarin yawa, wasu manya, wasu kuma masu take musu baya. Akwai taurari guda uku da suka fi fice, wa\u0257anda ana iya cewa ma gaba \u0257aya su suka \u0257auki nauyin labarin a kafa\u0257un su. Wa\u0257annan taurari kuwa su ne Labeeb Ibrahim Maska, Dawud Auwal da Kuma Mamdud. Sai dai duk da wannan, Labeeb ya fi Dawud taka rawar gani a cikin labarin, duk kuwa da cewa Dawud shiga gwagwarmaya da rikici mai yawa. Kuma \u0199alubalen da Labeeb ya fuskanta ya fi na kowa a cikin labarin, domin shi ya \u0257auki kusan nauyin kowa da laifin kowa a cikin labarin. Akwai taurari da yawa a cikin labarin bayan su da suka ha\u0257a da Sajda, Mami, Yumna, Asad, Anees, Huzai da dai sauran su.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Halayen Taurarin Labari<\/h2>\n\n\n\n<p>\u2022 Dawud: Matashin likita ne wanda ke matu\u0199ar son &#8216;yan uwanshi. Jarabawar rayuwa ta sa tun da sauran \u0199uruciyar shi ya zama babba a hankali da zuciya. Yana da zafin rai sosai, kuma yana da tausayi da taimako. Kamar yadda marubuciyar ta bayyana shi da cewa, &#8220;Ban ta\u0253a ganin mai \u0199arfin zuciya irin shi ba.&#8221; in ji zainab a babi na 32. Da kuma in da ta ce, &#8220;Tun barin mu gida na fara haka. Sai rasuwar Ummi&#8230; Ga Khateeb&#8230;.Ga Sajda. Ina jin tsoro&#8230; Ina ganin kamar da na rufe idanuwana wani abun zai same ni babu wanda zai kula da su. Kamar in na yi bacci wani abu zai same su su ma. (Babi na48)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 El Labeeb: Matashin jarumin fim ne. Yana shaye-shaye da bin mata, sai dai kuma yana da kyauta, tausayi da kuma \u0199aunar &#8216;yan uwansa fiye da komai. A wurare da dama marubuciyar ta bayyana shi a matsayin mutumin da zai iya yin komai saboda &#8216;yan uwanshi. Kamar yadda marubuciyar ta bayyana irin halin shi. &#8216;Kallonta Labeeb ya yi yana da\u0199una fuska. Da ka ga yanayinta kasan tana cikin halin rayuwa. In tana da iyali bai ga me dubu ashirin za ta yi mata ba.<br>&#8220;Nasan ba hurumina ba ne&#8230; Amma shin kina da yara?&#8221;<br>Kai ta \u0257an \u0257aga.<br>&#8220;Yarana shida&#8230;&#8221;<br>Sauke numfashi ya yi.<br>&#8220;In kin tashi dafa abinci kullum ki yi da yawa sosai, wanda zai isa har da su. Zan baki dubu hamsin duk wata&#8230; Ya miki?&#8221; (Babi na 41)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Mamdud Maraya ne da ya taso a gidan marayu. \u0198addarar rayuwa ta ha\u0257a shi da Labeeb har ya samu &#8216;yan uwa a tattare da ahalin shi. Yana da buri sosai a rayuwa wanda hakan ya ba hassada damar shigar shi. &#8220;Karki yanke min hukunci baki ji nawa ba. Bu\u0257e ido nayi na ganni a gidan marayu. Daga labarina da na sani yar da ni aka yi wani ya tsinta ya kai ni can.<br>Bansan asalina ba, bansan me yasa baibarni nan na mutu ba. Akwai lokuta da dama da na yi ro\u0199on in mutu da kaina saboda rayuwa ta yi min wuya.<br>Kowa na gani a titi kallonshi nake, kallonshi nake ko zan ga kamanni, in ka cika kallona zuciyata zata fara ro\u0199o da fatan za ka gane ni ka ce kasan &#8216;yan uwana.<br>Banda kowa a duniya da zan kalla in ce jinina ne Ateefa. Karki yanke hukunci kan abinda baki sani ba&#8230;&#8221; (Babi na 28)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Zulfa: &#8216;Ya ce a wurin Auwal da Ummi, kuma \u0199anwa ce ga Dawud. Ita da Labeeb &#8216;ya&#8217;yan yaya da \u0199ani ne, kuma tun tana \u0199arama suka sha\u0199u da juna. Kowa ya \u0257auka soyayya suke yi da Labeeb \u0257in. Hatta matar Labeeb \u0257in sai da ya zamana tana tantama, dubi yadda marubuciyar ta bayyana hakan da ce, &#8220;Na rasa gane tsakaninku da Zulfa. Kuma a haka ka ce min ba sonta kake ba. Komai a kanta daban ka ke yi, kullum da safe da ita kake fara waya. Ba ka kwanciya baka yi mata bankwana ba&#8230; Text sai ku yi wa juna sau nawa&#8230;&#8221; (Babi na 42)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Hajiya Beeba: Tsohuwar &#8216;yar bariki ce wacce ta ga jiya ta ga yau a harkar bariki. Ba ta da kunya kuma ba ta da tsoron Allah. Za ta iya yin komai domin ta cimma abinda ta sa a gabanta.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Auwal: Mutumin kirki ne mai son iyalanshi da kuma kyautata musu. \u0198addara ta ha\u0257a shi da Hajiya Beeba wadda ta asirce ce shi har sai da ta ga ta raba shi da iyalanshi.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Ummi: Asalin sunanta Aisha, mace ce mai matu\u0199ar kula da addini tare da biyayya ga mijinta. Tana da tausayi tare da sanin yakamata.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Mummy: ita ce Mahaifiyar su Labeeb. Macece da ta fito daga gidan ku\u0257i kuma ta auri mai ku\u0257i sannan ta ci gaba da kasuwancin ta bayan ta yi aure, wannan ya sa ba ta da lokacin &#8216;ya&#8217;yanta. Ba ta damu da tarbiyyar su ba, ganin \u0257anta na fari watau Labeeb ya zamo wani abu shi ne a gabanta.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Ateefa &#8211; Mace ce kyakkyawa sosai. An haife ta ta hanyar fya\u0257e ne da aka yi wa mahaifiyarta. Hakan ya sa ta taso cikin tsangwama a gidansu. Tana da kishi, kishin da ko sujjada ta yi sai ta ro\u0199i Allah da ya sau\u0199a\u0199a mata shi, (Babi na 32)<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Kurakurai<\/h2>\n\n\n\n<p>Kamar komai na rayuwa, labarin Rayuwarmu shi ma yana \u0257auke da wasu &#8216;yan kurakurai wa\u0257anda duk da fitowarsu, hakan bai hana labarin fita yadda ya kamata ba kuma bai yi wa sa\u0199on tasgaro ba.<\/p>\n\n\n\n<p>Ga su kamar haka:<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An yi amfani da kalmomin da basu dace ba irin su:<\/p>\n\n\n\n<p>Crap<br>Shit<br>Damn it<br>&#8220;Kutuma&#8230;.&#8221;<\/p>\n\n\n\n<p>Da dai sauran su.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Wasu wuraren ana sa sunan Aseem madadin Anees. (Babi na 21\/22)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Ba a fa\u0257a\u0257a bayani akan Ateefa ba kamar yadda aka fa\u0257a\u0257a akan sauran taurarin.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 An yi wani bayani wanda ka iya koyawa masu karatu mummunar \u0257abi&#8217;a, &#8216;Ganin unguwar shiru yasa ta kama ta dira da niyyar zama ta huta, sai dai ba zata manta video \u0257in da suka kalla da Yaya Musty gab da rasuwarshi ba.<br>\u018aankunnenta ta cire ta lan\u0199wasa da wani irin bugun zuciya ta zira shi cikin lock \u0257in sai dai ga mamakinta bu\u0257e gidan ta yi lafiya \u0199alau. Har ta shiga gabanta na fa\u0257uwa. (Babi na 29)<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Abin zai matu\u0199ar ba ka mamaki ace mace mai kyau irin na Ateefa wacce take cikin irin rayuwa kamar yadda aka bayyana ace kuma tana zuwa gidaje irin na su Labeeb domin samun wajen kwana kuma ace babu wata matsala da ta ta\u0253a fuskabta?<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 A \u0199arshen babi na 36 an nuna Mamdud ya yi hatsari har an kai shi asibiti, kuma bisa yanayin bayanin da likitan ya yi har an duba shi kafin wani nashi ya zo. Wannan ya sa\u0253a da irin yadda ake gudanar da aiyuka irin wannan a asibitocin \u0199asar nan. Sannan likitan ya ce sun ga lambar labeeb a cikin wayar Mamdud amma ta yi lalacewar da ba za ta yi kira ba. Alhali kuma a babi na 42 an nuna irin yadda da \u0199yar masu asibitin suka amshi Hajiya Beeba a emergency duba da cewa ba ahalinta ba ne suka kawota.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 A \u0199alla marubuciyar ta ambaci sunan littafin (Rayuwarmu) sau 35 a cikin labarin a wurare daban-daban wanda hakan kamar wani yun\u0199uri ne na tursasa wa mai karatu tare da \u0199o\u0199arin cusa mishi wata ma&#8217;ana madadin a barshi ya fahimta da kanshi.<\/p>\n\n\n\n<p>\u2022 Anya kuwa Nurse \u0257in da ta san aikinta yadda ya kamata za ta daka wa mara lafiyar da ke jinya irin na Hajiya Beeba tsawa ko da ba ta da ku\u0257in biyan magani? Balle fa har da cewa za ta sa securities su jefa ta cikin incinerator. Bana tunanin akwai wata Nurse da za ta nuna irin wannan halin ko in kula da rayuwar \u0257an Adam matu\u0199ar dai ta san aikinta. (Babi na 42) Ko da yake Hajiya Beeba ba mutuniyar kirki bace, hakan ba ya nufin za a yi amfani da duk wata hanya wajen ganin an yi maganinta. Musamman in ya zamana hanyar ta ci karo da abinda hankali ya yarda da shi.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Abin Yabawa<\/h2>\n\n\n\n<p>Rayuwarmu littafi ne da abubuwan yabawa da ke cikinsa ba za su \u0199irgu ba kuma za a iya gabatar da shi ga kowanne irin makaranci saboda akwai darussa masu yawa a cikinsa. Babban darasin da cikin wannan labari shi ne, babu wani abu da ke da tabbas a cikin wannan rayuwar, kuma kowa da irin \u0199alubalen da yake fuskanta a cikin tashi rayuwar.<\/p>\n\n\n\n<p>Haka kuma Littafin ya dace da matasa, magidanta, ma&#8217;aurata da ma sauran al&#8217;umma baki \u0257aya. Dalili kuwa shi ne, jigon labarin zai iya shiga kowane lungu da sa\u0199o na rayuwar kowa.<\/p>\n\n\n\n<p>Ko ba a fa\u0257a ba, kun san cewa marubuciyar ta cancanci a yaba mata bisa irin \u0199o\u0199arin da ta yi wajen \u0199ir\u0199iro wannan labari da kuma tsara shi ta yadda ya dace. Wani abu muhimmi da zan so in yabi marubuciyar musamman game da shi shi ne, irin yadda ta bayyana Labeeb a matsayin mai bin mata ba tare da yin batsa ba kamar wasu marubutan wannan zamani wa\u0257anda da zarar ka \u0257auki littafinsu za ka fara ganin batsa ta ko&#8217;ina. Wannan ya nuna kenan za a iya gina labari akan jigo na rayuwar aure ko makamantansu ba tare da an wuce gona da iri ba kamar yadda wasu marubutan ke yi.<\/p>\n\n\n\n<p>Dubi dai yadda marubuciyar ta koyar da wani muhimmin darasi cikin harshe mai sau\u0199in fahimta, Ita da Mami suka ha\u0257o ruwa suka \u0257auko, Mami ta auna Arif da farin zawwatin da ta yanka ta fita ta ba wa Dawud don a ha\u0199a kabari, ta dawo \u0257akin. (Babi na 36)<\/p>\n\n\n\n<p>Da kuma yadda ta isar da wani sa\u0199o shi ma mai muhimmanci da cewa,<\/p>\n\n\n\n<p>ya saki hannunta ya zaro mukullan gidan, ya saka da bismillah yana bu\u0257ewa.<br>Hannunta ya kama yana fa\u0257in,<br>&#8220;Bismillahi walajna wa bismillahi kharajna wa alallahi rabbina tawakkalna.&#8221; (Babi na 40)<\/p>\n\n\n\n<p>Suna idarwa ya juya ya \u0257ora hannunshi na dama a saman kanta yana karanta,<br>&#8220;Allahumma inni as&#8217;aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi&#8230; Wa&#8217;auzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi.&#8221; (Babi na 40)<\/p>\n\n\n\n<p>Wani \u0199arin yabo da ya zama dole a yi wa wannan littafi shi ne irin yadda Labarin ya banka\u0257o mummunan halin da marayu ke ciki a gidan rainonsu, babbar matsala daga ciki kuwa ita ce jahilcin ilimin addini. Kenan wannan ya zama izna ga masu ido a wannan fanni domin su tashi tsaye wajen ganin sun kawo canji akan hakan.<\/p>\n\n\n\n<p>Abu na \u0199arshe da zan \u0199ara jinjinawa marubuciyar akai shi ne, irin yadda ta bayyana matsalolin da rashin samun kular iyaye ke haifarwa ga &#8216;ya&#8217;yansu. Lallai wannan darasi ne da ke da matu\u0199ar amfani, musamman in muka yi duba da yadda wannan \u0257abi&#8217;a ke \u0199ara yawaita a cikin al&#8217;ummarmu.<br>Kuma irin wa\u0257annan darussa da marubuciyar ke haskawa ta tsaftataccen harshe a cikin litattafanta ya sa ta zama \u0257aya daga cikin shahararrun marubutan Hausa da ake alfahari da su a wannan zamani.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Shawarwari<\/h2>\n\n\n\n<p>A har kullum shi marubuci wani babban jigo ne a cikin al&#8217;umma wanda dubunnan mutane ke kallo su yi koyi da shi ko abinda ya rubuta. Ina ba wa marubuciyar shawara da ta ci gaba da yin rubuce-rubuce irin wannan domin al&#8217;ummar mu su amfana daga tarin ilimi da kuma fasahar da take da ita. Kuma ina na ta shawarar da ta ci gaba da zage damtse wajen yin bincike sosai domin gano matsalolin rayuwar mutanenmu na birni da \u0199auye tana rubutu akansu domin wayar da kan al&#8217;umma.<\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Kammalawa<\/h2>\n\n\n\n<p>Bana tunanin akwai wani mahalu\u0199i da zai karanta littafin Rayuwarmu ya ce bai amfana da tarin darussan rayuwa da ke cikin labarin ba. Domin sa\u0199onnin da ke cikin littafin sun fi \u0199arfin a yasar da su gefe, kuma suna da \u0199arfin tasirin da za su iya canza wa mutum tunaninsa game da wannan rayuwa da muke ciki ta duniya.<\/p>\n\n\n\n<p>Baya ga haka, littafin ya \u0199unshi duk abinda mai karatu zai iya tsammani da ma wanda bai ta\u0253a tsammani ba. Za ka ci dariya, za ka shiga cikin shau\u0199i, zuciyarka za ta yi rawa kuma za ka wa&#8217;azantu matu\u0199a da wannan labari. Akwai wuraren da ni kaina sai da na \u0257an dakata na yi wa marubuciyar tafi tukunna daga baya na ci gaba da karatun. A wasu wuraren kuma ba za ka san lokacin da za ka ri\u0199e baki ba saboda tsananin mamakin abinda ke faruwa a cikin labarin Wa\u0257annan da ma wasu abubuwa da dama wa\u0257anda ban ambata ba su ne suka sa kai tsaye zan iya cewa &#8216;Kada ka sake ka wuce wannan labari ba tare da ka karanta shi ba.&#8217;<\/p>\n\n\n\n<p>Kuna iya karanta <a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/rayuwarmu-1\/\">littafin Rayuwarmu<\/a> a Bakandamiya Hikaya. <\/p>\n\n\n\n<h2 class=\"wp-block-heading\">Manazarta<\/h2>\n\n\n\n<p>\u018aangambo, A. (1990) \u201cGadon Fe\u0257e Adabin Hausa (Ba a Buga ba).<\/p>\n\n\n\n<p>\u018aangambo, A. (1984) <em>Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa<\/em>. Kano: Triumph<\/p>\n\n\n\n<p>Junaidu, I. da Yar\u2019aduwa, T. M. (2007) <em>Harshe da Adabin Hausa a Sau\u0199a\u0199e don Manyan Makarantun Sakandare<\/em>, Ibadan: Spectrum Books Limited<\/p>\n\n\n\n<p>Junaidu, I. da \u2018Yar\u2019Aduwa T.M. (2002). Harshen da Adabin Hausa a Kammale, Don Manyan Makarantun Sakandire. Ibadan: Spectrum Books Limited<\/p>\n\n\n\n<p>Sani, M.A.Z., Muhammad A., da Rabeh B. (2000). Exam Focus Hausa Language Don Masu Rubuta Jarabawar WASSCE da SSCE. Ibadan: University Press Plc<\/p>\n\n\n\n<p>Umar, M.B. (1984) <em>Dangantakar Adabin Baka da Al\u2019adun Gargajiya na Hausa<\/em>. Kano: Triumph Publishing Company<\/p>\n\n\n\n<p>Yahaya, I. Y. (1981) \u201cAdabin Gargajiya a Makarantun Sakandare. Lacca da ya gabatar a Makarantar \u2018Yammata ta Dala<\/p>\n\n\n\n<p>Yahaya, I. Y. da \u018aangambo, A. (1986) <em>Jagoran Nazarin Hausa<\/em>. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Limited<\/p>\n\n\n\n<p>Yahaya, I. Y., Zaria M. S., Gusau M.S., da &#8216;Yar Aduwa T.M. (1992) <em>Darussan Hausa don Manyan Makarantun Sakandire 1<\/em>. Ibadan: University Press Plc <\/p>\n\n\n\n<p>Zarru\u0199, R.M., Kafin Hausa A. A. da Alhassan B.S.Y. (1987). <em>Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa Don \u0198ananan Makarantun Sakandire, Littafi na Uku<\/em>. Ibadan: University Press Plc<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Sunan Littafi: Rayuwarmu Marubuciya: Lubna Sufyan Inda Aka Buga Littafi: Bakandamiya Hikaya Shekarar Bugu: 2022\/23 Yawan Babi: 51 Mai Sharhi: Jamilu Abdulrahman (Haiman Raees) Manufar Sharhi: Bun\u0199asa Harshen Hausa da ciyar da adabi gaba. Gabatarwa Rayuwar duniyar nan cike take da \u0199alubale iri-iri. Yadda duk mu ke tunanin mun gama ganin kowane shafi na rayuwa,&hellip;&nbsp;<\/p>\n<div class=\"read-more-wrapper\"><a href=\"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/sharhin-littafin-rayuwarmu-na-lubna-sufyan\/\" class=\"button button-secondary\" rel=\"bookmark\">Read More &raquo;<span class=\"screen-reader-text\">Sharhin littafin &#8216;Rayuwarmu&#8217; na Lubna Sufyan<\/span><\/a><\/div>\n","protected":false},"author":6,"featured_media":4053,"comment_status":"open","ping_status":"open","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"neve_meta_sidebar":"","neve_meta_container":"","neve_meta_enable_content_width":"","neve_meta_content_width":0,"neve_meta_title_alignment":"","neve_meta_author_avatar":"","neve_post_elements_order":"","neve_meta_disable_header":"","neve_meta_disable_footer":"","neve_meta_disable_title":"","neve_meta_reading_time":"","_jetpack_memberships_contains_paid_content":false,"footnotes":""},"categories":[28,58],"tags":[43,94,41],"class_list":["post-4052","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-book-reviews","category-hausa","tag-lubna-sufyan","tag-rayuwarmu","tag-sharhin-littafi"],"jetpack_featured_media_url":"https:\/\/efd8kbkoisy.exactdn.com\/blog\/wp-content\/uploads\/2023\/12\/Sharhin-littafin-Rayuwarmu-na-Lubna-Sufyan.jpeg?strip=all","jetpack_sharing_enabled":true,"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/4052","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/users\/6"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/comments?post=4052"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/4052\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/media\/4053"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/media?parent=4052"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/categories?post=4052"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/hikaya.bakandamiya.com\/blog\/wp-json\/wp\/v2\/tags?post=4052"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}