Skip to content
Part 3 of 30 in the Series Fasaha Haimaniyya by Haiman Raees

DAGA ZUCIYATA

Da sunan Allah Rabba

Ba wa’azi zan yi muku ba

Ba nasiha zan muku ba

Ba damunku nake son yi ba

Zance ne daga zuciyata zan furta.

*****

Damuwa ta aure ni

Damuwa ta kama ni

Damuwa ta dame ni

Damuwa ta kayar da ni

Ta bi duk ta dagule zuciyata.

*****

Ban san fa me ya sa haka ba

Ban san fa me na yi musu ba

Ban san ya suke so ba

Ban san ya suke so na yi ba

Ban san menene yasa suke ƙina ba.

*****

Wai ni ba dogo ne ba

Wai ni ba siriri ba

Wai ni ai ban waye ba

Wai ni ban san komai ba

Wai shin sai yaushe ne za ku bar gaba?

*****

So suke wai in yi kaza

So suke wai in bar kaza

So suke in je wuri kaza

So suke in bar gu kaza

So suke dai in zamo kamar banza.

*****

Sun ce min ɓarawon kaza

Sun ce wai na saci reza

Sun ce wai ai na yi kaza

Sun ce wai ai na ce kaza

Sun ce wai ni na zamo kamar geza.

*****

Saboda na ƙi zama wawa

Saboda na gaza duƙawa

Saboda na gaza dainawa

Saboda na gaza kasawa

Saboda na zama wanda ya ƙi lalacewa.

*****

Shi yasa basa sona

Shi yasa fa suke ƙina

Shi yasa suke tsorona

Shi yasa suke ta guduna

Shi yasa suke min hassada a aikina.

*****

Ko da dai kun cuce ni

Ko da dai kun zalunce ni

Ko da dai kun tauye ni

Ko da dai kun fa tsane ni

Ko da ba kwa son ganina dai gani.

*****

Komai na yi ban burge ba

Komai na yi ban fa iya ba

Ko na yi ma ba za a yaba ba

Kuma ba za a koya min ba

Komai in dai nawa ne ba a so ba.

*****

Ya kuke so ne wai na yi?

Me kuke so ne wai na yi?

Ta yaya zan iya canja yanayi?

Shin ta yaya zan canja ra’ayi?

Bayan na san ni ne akan gaskiya?

*****

‘Yan uwa wasu na ƙina

Duk da dai wasu na sona

Abokai na ta guduna

‘Yan mata na shakka na

Duk kawai saboda wai ina son gaskiya.

*****

Jama’a sun sani gaba

Jama’a sun tasa ni gaba

Jama’a na nuna min gaba

Jama’a sun hanani ci gaba

Jama’a kar ku manta Allah ba zai ƙyale ku ba.

*****

Na zamo kamar mujiya

Wacce ta faɗa rijiya

Tana faman ninƙaya

Amma ta gaza kufcewa

Kuma an gaza cetonta wai don ana tsammanin ba ta da gaskiya.

*****

Duk wanda shi bai da ra’ayi

Wannan ku kira shi gawayi

Girki da shi kawai za’a yi

Bayan nan ba shi da amfani

Wannan shi ne zance na gaskiya.

*****

Ka zamo mai tausayi

Zalunci sam kar da ka yi

Hassada ita ma kar ka yi

Mugunta ma sam kar ka yi

In ko ka yi su tabbas ka kauce gaskiya.

*****

Kada ka yawaita inkari

Ka zamo mai yin nazari

Ka zamo mai yawan uzuri

Ka zamo mai kuzari

Idan har ka yi hakan kana kan hanyar gaskiya.

*****

Ka zamo jajirtacce

Ka zamo nagartacce

Ka zamo ingantacce

Ka zamo abin kwatance

In har ka yi hakan tabbas kana kan gaskiya.

*****

Ba lallai sai ka soni ba

Ba lallai sai kin soni ba

Ba lallai sai kun soni ba

Kuma ba lallai sai kun ƙini ba

Amma kun gaza fahimtata shi ya sa kuka kasa gano wa ke da gaskiya.

*****

Na san ni mai laifi ne

Ka san ni mai laifi ne

Kin san ni mai laifi ne

Kun san ni mai laifi ne

Kuma kowa na duniya yana laifi.

*****

Na san ni mai zunubi ne

Ka san kai mai zunubi ne

Kin san ke mai zunubi ne

Kun san ni mai zunubi ne

Kuma kowa na duniya yana zunubi.

*****

Na san na yi kuskure

Ka san ka yi kuskure

Kin san na yi kuskure

Kun san na yi kuskure

Kuma kowa na duniya yana kuskure.

*****

Kada duniya ta ruɗe ka

Kada abokai su ruɗe ka

Kada kuɗi su ruɗe ka

Kada zuciya ta ruɗe ka

Idan ko har ka yi hakan ka bar hanyar gaskiya.

*****

Ka yarda wani ya fi ka

Ki yarda wata ta fi ki

Ka yarda wasu sun fi ka

Ka bi duk wanda ya fi ka

Idan har ka yi hakan kana kan gaskiya.

*****

In har ba ka son kanka

Ta yaya za ka so waninka?

In har ba kya son kanki

Ta yaya za ki so wanin ki?

In har ba son kanmu ta yaya za mu so wasunmu?

*****

In kace ban fa iya ba

To ai sai ko ka koya min

In ko ba za ka iya ba

Ka ga dole ka ƙyale ni

Tun dai ita rayuwa sai da gwadawa.

*****

In kika ce ba kya sona

Sai ki bar ni da mai sona

In ko sam ba ki iyawa

Sai ki kuma daina to bina

Domin ita rayuwa sai da soyayya.

*****

Kowa dai na da ra’ayi

Na san kana da ra’ayi

Ke ma kina da ra’ayi

Kowa ma na da ra’ayi

To akan me za a ce kada in zamo mai ra’ayi?

*****

Nima jini ne a jikina

Jini ne ba ƙarfe ba

Zuciya ce a ƙirjina

Zuciya ba dalma ba

Domin nima ɗan Adam ne ba ƙarfe ba.

*****

Ko na yi ko kuma ban yo ba

Za ace ban yi dai-dai ba

Komai na yi wai na yi ƙwaɓa

Komai na yi wai ban caɓa ba

Sai kace ni ne na auri asara.

*****

Nima fa ɗa na Adam ne

Nima fa ina da idanu ne

Nima ina fa da hanci ne

Nima ina fa da ai kunne

Nima ina da duk abin da kowa yake taƙama da shi.

*****

Kamar yadda kake son kanka

Haka nima nake son kaina

Kamar yadda kike son kanki

Haka nima nake son kaina

Kamar kowa ni ma ina son kaina.

*****

Kana so kai ka ji daɗi

Kina so ke ki ji daɗi

Ku sha madara mai garɗi

Da ɗanɗanon duk wani daɗi

To menene yasa ni ban cancanci hakan ba?

*****

In har ma laifi ne na yi

Me ya sa za ku kyare ni?

Madadin ku nusar da ni

Shi ne sai kuma ku tsane ni

To menene ribar hakan don Allah?

*****

Iyaye duk ku yi nazari

Shugabanni ku yi nazari

Malamai ku yi nazari

Manyanmu duk ku yi nazari

Shin matsalar ta ina take a sassan mu?

*****

In Allah ya maka ni’ima

Burinka ka guji al’umma

In Allah ya jarrabe ka

Sai ka nufo gun Al’umma

Ta yaya ita al’ummar za ta ci gaba?

*****

Ka ce ni wai yaro ne

Aikin ga wai na manya ne

Manya a cikin dukka mutane

Wai ni na gaza in gane

Bayan kuma kullum duniya ni ake cuta.

*****

Ku sani Allah na nan

Ku sani tsufa na nan

Ku sani mutuwa na nan

Ku sani lahira na nan

Ku sani ranar tsayuwa ita ma na nan.

*****

Rabbana ka yafe mu

Rabbana ka kare mu

Rabbana ka shirye mu

Rabbana ka cece mu

Rabbana ka kawo mana ɗauki da gaggawa.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 4.9 / 5. Rating: 13

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fasaha Haimaniyya 2Fasaha Haimaniyya 4 >>

3 thoughts on “Fasaha Haimaniyya 3”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×