Skip to content
Part 20 of 37 in the Series Fadime by Fulani Bingel

Ko da ta isa cikin tashar zuru ta yi tana ƙarewa motocin kallo, sunayen garuruwa kawai kake ji na tashi, Lagos, Gombe, Bauchi, Kebbi, Jos.. ga suñan dai kala-kala. Lumshe idanuwanta  ta yi sa’ilin da ta tuna hirarta da Mamuda “Babana Balarabe ne, muna zaune a Lagos, cikin…” Sai kawai ta saki murmushi ita ɗaya tana dosar motar lagos din. Gwara kam ta tafi garinsu masoyin nata, ko banza ta din gajin ƙamshin ƙasar da ya taka.

Da ikon Allah ko mutum guda suke jira, nan da nan ta biya abinda suka caje ta, in da banda Naira dubu babu abinda ya saura mata.  Ta yi mamakin yadda dubu goman ta ƙare a yini guda kawai. “ALLAH KAREEM” Ta furta sa’ilin da ta zauna cikin motar. 

Sai da suka kwana suka yini sannan suka isa, nan fa kowa ya sauko masu gurin zuwa suka fara nufar inda suka zo, ire-iren su Faɗime kuwa suka fara zagaya tashar cikin rashin abinyi.

Rana na gafda faɗi Abbati ya fara mata kukan yunwa, ɗan abin da ya saurar mata shi suka cinye a hanya, wannan fa shi ne idan ba ka da shi, mai baka baya da shi, to rannan fa kai da ɓarawo shawararku guda ce. Fitowa ta yi daga tashar tana bin gefen titi cikin ƙarewa garin kallo. 

Allah da ikon sa kuwa ta hangi wani (Restaurant)nan da nan ta tsallaka ɓarin da yake, gwara ko bara ne ko tattara wanda aka ci ne tayi a wajen ta samu abinda zata bama Abbati.

Da gudu Abbati ya kwace hannunsa daga nata ya nufi gurin wata budurwa da ke zaune tana cin Abinci. Kallonta yake yi , sai ya juyo ya kalli uwar tasa kamar mai neman izinin ya saka hannu. To itama budurwar ɗagowa ta yi tana kallon yaron, sai kuma ta kai kallonta ga wacce yake kallo. Murmushi ta saki gami da tura masa abincin gabansa, ta na mai ya fito Faɗime da ta tsaya tana kallonsu.

Iso wa ta yi gurinsu ta ja kujera ta zauna tana kallon Abbati da ya kafa mata ido yana kallo. 

“Ka ci mana.” Ta furta tana mai da dubunta ga budurwar.

“Na gode” 

Murmushi ta yi tana ƙare mata kallo.

“Amman ke baƙuwa ce a nan ko?” Ba ta jira amsarta ba ta ci gaba.

“Naga alama, sai dai kyakkyawa kamarki roƙo bai kama ta ba, kome ya fiddoki daga garinku, bai kamata ki yi bara da wannan ƙaramin yaro ba. Ni ba jin labarinki zanyi, na san babu wani alheri, ba kuma zai kai munin nawa abin da ya raba ni da gidan ba. Kawai dai zan so ki biyo ni na

sanyaki cikin irin kasuwanci na dan kema ki samu abinda a zaki kula da kanki da kuma yaronki. Taimakone, Ba kuma wata mummunan harka ba ce. In fito miki a mutum gabaɗaya dan ban iya munafurci ba, kar kuma ki yi zaton taɓin hankali gare Ni dan daga ganinki na fara furta miki sirrina.” Ta furta da murmushi tana sassauta muryarta.

“Safarar cocaine ne daga wannan kasa zuwa waccar. Ki yarda da Ni, ba ƙaramin kudi zaki riƙe ba maganin talauci da baƙin cikin duniya. Sunana Linda.” Ta ƙarasa tana miƙa mata hannu.

Ba kalamanta ba ne suka bawa Faɗime mamaki, a’a shigar dake jikinta irin ta fitsara da hausar da taji ta ‘na rattabowa ne suka saka ta sakin baki tana kallonta.

“Ya na ki sunan?” Ta sake jin maganarta wacce ta dawo da ita In da ta nausa.

“Fatima.” Ta furta tana ƙarewa ƙatuwar kwalbar Beer ɗin dake gabanta kallo.

Kaɗa kai kawai ta yi kafin kuma ta jawo kwalin Taba, ta ƙyasta lighter gami da ɗora ta saman laɓbanta ta hau zuƙa tana kallon Fati.

“To, baki ce kome game da zance na ba?”

Fadi kam ta nausa kallon yadda mata ke shan Taba.

Ganin haka ya sakata murmushi tana kallon abinda take kalla, kafin kuma ta miƙa mata ta hannunta. 

“Karɓi ki sha, ko da ƙaryane, amma da gaske ni tana rage mini damuwa, ta yiwu abin ‘Believe’ ne.”

Jin hakan ya saka ta miƙa  hannu a hankali ta karɓq gami da kaiwa bakintà yadda ta ga tana yi. Ja ydaya ta yi ta kware, hakan bai sa ta ƙi ja a karo na biyu ba.

A hankali ta fesar da hayaƙin tana mai sauke idanuwanta kan Abbati da ya tsura mata ido yana kallo.

“Na yarda zan bi ki.”

Ko da ta isa cikin tashar zuru ta yi tana ƙarewa motocin kallo, sunayen garuruwa kawai kake ji na tashi, Lagos, Gombe, Bauchi, Kebbi, Jos. ga suñan dai kala-kala. Lumshe idanuwanta ta yi sa’ilin da ta tuna hirarta da Mamuda “Babana Balarabe ne, muna zaune a Lagos, cikin.” Sai kawai ta saki murmushi ita ɗaya tana dosar motar lagos din. Gwara kam ta tafi garinsu masoyin nata, ko banza ta din gajin ƙamshin ƙasar da ya taka.

Da ikon Allah ko mutum guda suke jira, nan da nan ta biya abinda suka caje ta, in da banda Naira dubu babu abinda ya saura mata.  Ta yi mamakin yadda dubu goman ta ƙare a yini guda kawai. “ALLAH KAREEM” Ta furta sa’ilin da ta zauna cikin motar. 

Sai da suka kwana suka yini sannan suka isa, nan fa kowa ya sauko masu gurin zuwa suka fara nufar inda suka zo, ire-iren su Faɗime kuwa suka fara zagaya tashar cikin rashin abinyi.

Rana na gafda faɗi Abbati ya fara mata kukan yunwa, ɗan abin da ya saurar mata shi suka cinye a hanya, wannan fa shi ne idan ba ka da shi, mai baka baya da shi, to rannan fa kai da ɓarawo shawararku guda ce. Fitowa ta yi daga tashar tana bin gefen titi cikin ƙarewa garin kallo. 

Allah da ikon sa kuwa ta hangi wani restaurant nan da nan ta tsallaka ɓarin da yake, gwara ko bara ne ko tattara wanda aka ci ne tayi a wajen ta samu abinda zata bama Abbati.

Da gudu Abbati ya kwace hannunsa daga nata ya nufi gurin wata budurwa da ke zaune tana cin Abinci. Kallonta yake yi , sai ya juyo ya kalli uwar tasa kamar mai neman izinin ya saka hannu. To itama budurwar ɗagowa ta yi tana kallon yaron, sai kuma ta kai kallonta ga wacce yake kallo. Murmushi ta saki gami da tura masa abincin gabansa, ta na mai ya fito Faɗime da ta tsaya tana kallonsu.

Iso wa ta yi gurinsu ta ja kujera ta zauna tana kallon Abbati da ya kafa mata ido yana kallo. 

“Ka ci mana.” Ta furta tana mai da dubunta ga budurwar.

“Na gode” 

Murmushi ta yi tana ƙare mata kallo.

“Amman ke baƙuwa ce a nan ko?” Ba ta jira amsarta ba ta ci gaba.

“Naga alama, sai dai kyakkyawa kamarki roƙo bai kama ta ba, kome ya fiddoki daga garinku, bai kamata ki yi bara da wannan ƙaramin yaro ba. Ni ba jin labarinki zanyi, na san babu wani alheri, ba kuma zai kai munin nawa abin da ya raba ni da gidan ba. Kawai dai zan so ki biyo ni na

sanyaki cikin irin kasuwanci na dan kema ki samu abinda a zaki kula da kanki da kuma yaronki. Taimakone, Ba kuma wata mummunan harka ba ce. In fito miki a mutum gabaɗaya dan ban iya munafurci ba, kar kuma ki yi zaton taɓin hankali gare Ni dan daga ganinki na fara furta miki sirrina.” Ta furta da murmushi tana sassauta muryarta.

“Safarar cocaine ne daga wannan kasa zuwa waccar. Ki yarda da Ni, ba ƙaramin kudi zaki riƙe ba maganin talauci da baƙin cikin duniya. Sunana Linda.” Ta ƙarasa tana miƙa mata hannu.

Ba kalamanta ba ne suka bawa Faɗime mamaki, a’a shigar dake jikinta irin ta fitsara da hausar da taji ta ‘na rattabowa ne suka saka ta sakin baki tana kallonta.

“Ya na ki sunan?” Ta sake jin maganarta wacce ta dawo da ita In da ta nausa.

“Fatima.” Ta furta tana ƙarewa ƙatuwar kwalbar Beer ɗin dake gabanta kallo.

Kaɗa kai kawai ta yi kafin kuma ta jawo kwalin Taba, ta ƙyasta lighter gami da ɗora ta saman laɓbanta ta hau zuƙa tana kallon Fati.

“To, baki ce kome game da zance na ba?”

Fadi kam ta nausa kallon yadda mata ke shan Taba.

Ganin haka ya sakata murmushi tana kallon abinda take kalla, kafin kuma ta miƙa mata ta hannunta. 

“Karɓi ki sha, ko da ƙaryane, amma da gaske ni tana rage mini damuwa, ta yiwu abin ‘Believe’ ne.”

Jin hakan ya saka ta miƙa  hannu a hankali ta karɓq gami da kaiwa bakintà yadda ta ga tana yi. Ja ydaya ta yi ta kware, hakan bai sa ta ƙi ja a karo na biyu ba.

A hankali ta fesar da hayaƙin tana mai sauke idanuwanta kan Abbati da ya tsura mata ido yana kallo.

“Na yarda zan bi ki.”

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 3

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fadime 19Fadime 21 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×