Skip to content
Part 4 of 30 in the Series Fasaha Haimaniyya by Haiman Raees

KAICO

Bissmillah da sunan ilahi

Wanda ya aiko ɗan Abdullahi

Zan yi batu da tambihi

Bani dama sarkina ilahi.

*****

Mu yaran zamani yau

Ba mu jin magana ayau

Iyaye na ta fama

Mu kuma muna ta fankama.

*****

Ba mu tsoron ɓaci na ransu

Ba mu yin ladabi garesu

Ba ma biyayya garesu

Amma in buƙata ta tashi mu je wurinsu.

*****

Ra’ayinmu kawai muke bi

Ko mara kyau ne shi za mu bi

Ra’ayinsu ko ba ma bi

Ko da mai kyau ne ba ma bi.

*****

A hakan muke so wai mu ci gaba

Alhali da uwarmu muke gaba

Mun ce mu ne za mu shige gaba

Wai shugabancin ya fi ƙarfin uba.

*****

To yaya ma za mu ga haske?

Bayan albarkar mun make?

Mun aje uwarmu a gefe

Mun ɓoye ubanmu a shinge.

*****

Kaico! Wannan lamari da gyara

Shi ya sa ma har na ɓara

Ku ka ji ni ina ta ƙara

Sai ka ce wanda sago ya sara.

*****

To wallahi mu yi hankali

An ce duniya ɗamarar jangali

Dole sai an bita a hankali

Ko kuma mu faɗa baƙin hali.

*****

Allah ka ƙara wa iyaye lafiya

Ka sa mu gama da su lafiya

Mu zamo masu ƙaunar tarbiya

Ga manyanmu mu zam masu biyayya.

*****

Sarki ka shiryar da mu

Da abokai da ahalinmu

Da dukkan ‘yan danginmu

Ka sa shiriya a zukatanmu.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 7

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fasaha Haimaniyya 3Fasaha Haimaniyya 5 >>

3 thoughts on “Fasaha Haimaniyya 4”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×