Skip to content
Part 1 of 23 in the Series Kuskuren Wasu by Sanah Matazu

Shimfida

Fatima Aliyu Shira

Sam ta kasa fahimtar dalilin da zai sa a kira mutum miji amma ace sai matarsa ta shata layuka tsakanin su idan tana son zamanta da shi.

A zatonta aure amintacciyar tarayya ce tsakanin mace da namiji. Amma abin da take gani yana faruwa da al’ummata yafi kama da mulkin mallaka. Kullum koken mata a kan maza ne. Kullum tana tambayar kanta. Haka rayuwar mata za ta kasance? Kullum su ne koma baya? Ta sha jin ance aure shi ne mutuntakar su, abin tambayar shin aljannah ba ta samuwa ga ɗiya mace ne sai dole ta hanyar aure?

Idan mace ba ta yi aure ba ita ce lallataciya, amma kuma yayinda ta karɓi alamtuwar martabar auren sai ta zamo baiwa? Baiwar ma ba irin wadda za ta amsa sunan baiwa mai bauta ba, sai ta zamo baiwar da za ta karɓi kowa ce ƙasƙantaciyar rayuwa saboda kawai an maƙala mata kalmar nan ta mace matar aure?

Ba ta manta huɗubar malaminsu ba kan cewar sani Allah ubangiji da kansa ya ɗaga darajar maza akan mata, amma hakan ba yana nufin mace ta zama tabarmar zaman su ba. Ko kuma dogoran su ba wurin cutar da ita.

Komai namiji ya yi sai a kira shi ado? Bayan kuma idan aka yi masa duban tsanaki dodon adone ga rayuwar ɗiyar mace. Wannan wace irin rayuwa ce da farinciki da nutsuwar mace ba su da mahimmanci a gidan aure? Wace irin al’ada ce dake mantawa da cewa mace ma abar halitta ce mai zuciya a cikin ƙirjinta? Anya akwai mafi cancantar dacewa da a tausayawa sama da rayuwar ɗiya mace!?

Maryam Tukur Malumfashi

Ta rasa dalilin da zai haifar da ƙasƙantaciyar rayuwa a duniyar ma’abota sadaukarwa domin rungumar ‘yancin rayuwa. Ta so kwatanta dagiya domin tabbatuwar ƙimar ahalinta sai da kuma kash, wannan tambarin mai ɗauke da sarewa ya dankwafar da duk wani motsi nata.

Masu salon magana na cewa uwa dajin ɗanta. Kasantuwarta dajin ‘ya’yanta biyar ya sarayar da duk wani muradanta. Ya gurguntar da tunanin gobenta. Ta sha tambayar kanta, shi mene ne laifin yaran da a ka saki mahaifan su? Wane dalili ne zai sa a wofintar da ta su rayuwar zuwa matakan rugujewa? A zuciyarta tana da yaƙinin da mahaifinyata ba ta yasar da ita a jujin gidan mahaifinta ba, da bata samu rayuwarta kaso saba’in cikin matsalolin da na fuskanta ba. Bare har hakan ya bibiyi rayuwar abin da ta haifa.

A tsamaninta ‘ya’ya rabin farin ciki ne ga rayuwar iyayen su. Farin cikin su kan ruɓaya na su komai rintsin da za su fuskanta ashe ba haka ba ne? Ta ɗauki kwagiri a kainta domin kyautata muradinta, ta tura ruwa a kura domin goben ‘ya’yanta. Zuciyartavna tambayarta me ya sa tata uwar ta wofintar da ita?

Ta kan ji ance uwa uwa ce koda ta buzuzu ce. Amma me ya sa ta ta ta kasa amsa sunan? Ina karin maganar da hausawa suke cewa uwa dajin ɗanta? Tabbas ita kam be yi mata rana ba.

Bata da masaniyar yaushe ne zata daina kukan rasa mijin marainiya. Ba ta da yaƙinin inda za ta nemo asalinsa amma tana ji a ƙasan rainta wata rana za su dara.

Zuciyarta ta bushe yayin da idanunta suka ƙeƙashe, ba ta duban kowa a yanzu bayan ‘ya’yanta, su ta maida madubi kuma fitilarta. Domin ta lura kowa kansa da rayuwarsa ya sani. Sai dai bata taɓa tsamanin akwai ƙaddarrar da take sanɗo tana bibiyar rayuwar ɗa ɗayan da ta ƙwalafa wa rai ya zamo tamkar ruhinta ba.

Alawiyya Wada Alfa

Kasantuwarta sakakiyar baiwa wadda ta haƙiƙance kan cewar lallai sai yanzu ne ta faɗa duniyar da ta da ce da ita. Rayuwata ta gauraya da duhun da makantar zuciya ta sanya take wa kallon haske.

A gurbattacen tunaninta a baya rayuwa take mara alfanu. Haɗuwarta da ‘yantaciyar baiwa ya ba ta lasisin da take ganin ta wanke duk wata tsatsa da ta kewaye zuciyata.
Ta tanadi muradai da yawa da sai yanzu na hango himatuwar cikar su. Ta yi wa kantaa alƙawarin ruwa da iska babu mai yi mata waigi da kusancinta da wannan baiwa ciki kuwa hadda abin sonta kuma alfaharinta Dr Aliyu Ibrahim Maitama.

Domin zuciyarta ta gama tabbatar matada shi ne tsanin da ya kaita ga rungumar kundin zunubantaa.Wanda duhun rai ya sanya ra gasgata cewar shi ya runtomini su cikin duniyata. Doan haka tare za su yi haddar karatun. Tare za su kwashi zunuban, haka kuma tare ne za su koka ko da hakan zai kawo ƙarshan numfasawar su.

*****
To masoya, gamu akan hanyar tafiya ce tsakanin duhu da haske. Ban sani ba ko ya zo dai-dai da muradanku ko kuma akasinsa ni dai fatana yayinda shatuwar layin uzuri ya gindaya a tsakaninmu ku zamo masu fahimtata. Zamu fuskanci rayuwar waɗanan jaruman matan guda uku.

Kadda ku yi ƙasa a guiwa wurin ɗaga mutuntakar junanmu, kadda ku manta mu ɗin abu guda ne da ɗaya ba ya iya tafiya idan babu tallafin ɗaya.

Sanahrku ce!

Babi Na Daya

“Fatima wai me ya sa ba ki da mutunci ne, ke kullum cikin ƙorafi ki ke? Ke wace irin mace ce ne? Haka ki ka ga sauran mata na rayuwar auransu?”

“Samir ka kirani da duk sunan da ranka yake so, amma wallahi ka ji na rantse ba zan juri wannan cin fuskarba. Ka faɗamin wanne haƙƙi ne naka bana saukewa? Kawai saboda son rai irin naka ba siɗi ba saɗaɗa sai ka ƙirƙiri fitinar da ba ta da tushiya domin ka ɗagamin hankali? Wai me ya sa baka da imani ne? Baka tausayina ko kaɗan wallahi”

Duka ya kawo mata da bahagon hannunsa, a sukwane ta goce tana karewa da sirirraran hannunta. Ta kai kallonta kan dogon yatsunta, waɗanda su ka ƙawatu da jan lallen da ta shafe lokaci tana manna salatif kawai domin ta faranta masa. Amma kuma dawowarsa ba ta amfana mata komai ba sai kayan takaici. Wanda da a bayane yana shigowa da kuzanta ƙunshin zai soma kafin komai. Ja baya ta yi tana girgiza kai,
“ka yi komai Samir, amma kadda ka kuskura hannunka ya kai jikina da sunan duka! Zan baka mamaki fiye da…”

Tau! Ta ji saukar mari a kuncinta, wanda ya haddasa mata yin a hantsile bakinta ya bugu da kujera, kallonsa take, sai diri ya ke yi kamar mahaukacin kare. Gadan-gadan ya yo kanta kamar mayunwcin zaki, yana nufarfashi kamar matashin ɓauna.

“Bara na gwada miki tawa kalar tarbiyar kafin ki nuna min taku, wai ku kuna taƙama da boko da anyi magana ku kira ƴanci ko? Gaskiya sai yanzu na amince da batun Samir amma zan nuna miki kuskurenki. Ni ba sauna ba ne ba zan ɗauki cin kashin da ƴan gidanku ke yi wa maza ba!”

“Samir!”

Ta yi furucin tana ja baya, laɓɓanta na motsawa da wani irin karsashi, a saitin idanunsa ta ke ajiye masa kallo cike da tuhuma. Tabbas sai yanzu ta ƙara ganin wautarta na yanke auren Samir. Kuskurenta na farko shi ne rashin sanin waye asalin Samir ɗin, kawai ta na yi masa kallon da takewa tarbiyar ahalin su ne kasancewarsa ɗan babban gida.

Shi ya sa babu wani jinkirtawa ta amince da shi. Ashe kallon kitse ne take yi wa rogo. Amma abu na farko da ya kamata ace ta duba shi ne, waye abokinsa? Zuciyarta ta tunatar da ita cikin raɗa,

‘Jabir!’

Runtse idanu ta yi tana tuna waye Jabir ɗin? Wani matashi ne d duk unguwarsu babu mai rashin jin sa. Iyaye da yawa sun yi wa yaransu shamaki da shi ciki kuwa har da yayunta mata. Babu yadda ba ayi ba ganin an rabasu amma ƙi jin magana. Dalilin zaɓarsa me mahaifanta suka shata mata layi kan ahalinta, kuma tace ta ji ta gani. Sai ga shi tana girbar shukarta tun kafin aje ko’in. Rabon da ta tak gidansu tun ranar da ta je Samir ya je ɗaukota amma ga shi ga mahaifinta ya kasa gaishe shi, tunƙahonsa shi ne ai ba shi ne ya ba shi aurenta ba ƙaninsa ne. Kuma ba ya sonsa.

Karo na farko da ta soma nadamar aurensa, mahaifinta murmushi kawai ya yi yana barin wurin domin abin da ya gudar mata ke nan.

Satinta biyu a gidansa ya soma kawo mata ‘yan mata. A gabanta zai shigo da duk macen da ya yi niyya da sunan ƙawa haka m waya. Gidanta ya zama kamar dandalin ‘yan iska. Ya kawo abokai su sha shisha ta yi magana ya naɗa mata dukan kawo wuƙa kuma ba zai hana shi y sanyata aiki ba kuma dole ta yi.

Tana jin kunyar kai ƙara gida, domin ƙiri-ƙiri mahaifanta suka kasa tanƙwarata a kansa wanda sanadin hakan igiyar auren mahaifiyarta guda ta girgiza. Sanadin da ya sa hata dangin mahaifiyarta suka ƙaura daga lamarin auranta.

Danginsa ma ba zuwa suke yi gidan ba, domin shi ne ya fita zakka a gidansu, mahaifinsa mutumin kirki ne amma sai da ya kasance dalilin Samir ana zuwa har gida aci mutuncinsa saboda bin ‘ya’yan mutane da hure musu kunne. Ita kanta rabon zama ƙarƙashin inuwar aure ne ya gindaya alaƙa tsakaninsu. Amma duk ‘yan matansa na baya sai dai ya wanke su ya gudu ya sauya wata da kin gama amfani wurinsa.

A hankali ta buɗe idanunta ta sauke su akansa. Sun kaɗa sun yi jajjur. Murmushin tsakiyar laɓɓa ya saki, yana aje kallonsa a saitinta. Kallon tsakiyar ido ya yi mata, a wannan karon ya yi nasarar ganin muradinsa, wato rauni a tare da ita. Yana kallon yadda kowace gaɓa ke amsar saƙonsa, zagayeta ya yi na sakan biyu. Ya ƙyasta hannuwansa ƙyas! Ƙyass!! Ƙyasss!!! A lokaci guda cike da karkashi ya furta,

“Haba Fatima me ya sa ki ka kasa fuskantar mu maza dangin gujiya ne?”

Murmushi ta yi mai sauti, ƙwallar da ta ke adanawa tsayin lokuta ta sami zubowa, yau ɗaya ta ji karsashi da muradin son maida masa martani.

“Tabbas Samir Ka zamo min dungu acikin rayuwata, sai dai kasani ba kowa ce ba ce take zama…”

“Ƙarasa mana ba kowace mace ke zama namiji yana takata ba ko? Ai ban yi mamaki ba. tambarin ahalinku ne wannan”

“Samir ya isheka. Kana faɗin ahali! Ahali!! Shin kai kana da..!”

Ba ta sami zarafin ƙarasa abin da take san faɗa ba, ya kaɗa kai ya yi ficewarsa. Dubansa take, kowane motsi nasa yana ajiye mata tabo mai girma a ranta. Karo na barkatai ta sake kai idanunta, yana gab da fita, tafiyarsa yake hankali kwance, yana aje taku kan duga-dugansa cike da sarauta. Sautin muryarsa ke fitar da waƙar da ke nuna zallar nishaɗinsa, a hankali ta fashe da kuka mai cin rai. Lumshe idanu ta yi tana ayyana,

‘lallai maza suna su ka tara’

Ta shafe mintuna uku a zaune ta ji sallamar Mama Khadij. Hakan bai sa ta maida hawayenta ba, domin abokin kuka ake faɗawa mutuwa. Da sassarfa ta ƙarasa tana rungumarta. Kuka ta ɓale da shi kawai kanta yana wata irin sarawa,

“Ko ban faɗa ba Allah zai saka min wallahi!”

Da hanzari ta kalleta, bakinta har rawa yake yi,

“Me ya sa ki ke haka ne ɗiyata? Kin san kuwa illar mace ta nemi sakayya akan zalluncin da mijinta ya aikata mata? Hmm! Ba fa komai ki ke yi ba face daɓawa kanki wuƙa!”

Taune gefan bakinta ta yi karo na barkatai, ta ɗora hannunta akan ɗan matashin cikinta da ya soma girma, wanda har gobe wanda ya yi sillar samuwarsa bai san da zamansa ba.

“kinga wannan abin da ki ke tare da shi”, ba ta bari ta amsa ba ta ci gaba, “ko badaɗe ko bajima shi ki ke nema wa makoma matuƙar za ki nemi sakayya. Ai abin cikin ƙwan ya fi ƙwan daɗi, kina roƙon ubangiji ya saka maki akan abin da ya akaita miki, sakayya kuma kan ahalinsa za ta tabba ta domin abin da ya taɓasu shi ya taɓa. Kina san ki haifi ɗiya ta tashi a irin rayuwar da ki ke ciki?”

Da hanzari ta girgiza kanta, ƙaunar abin da ke cikin nata na ƙara zagaya lungu da saƙo na zuciyarta. Kanta ta ɗora bisa kafaɗar ƴar uwarta. Wani kuka mara sauti na neman ƙwace mata.

“Mama sam na kasa fahimtar dalilin da zai sa a kira mutum miji amma mutaakan ba yana nufin mace ta zama tabarmar zamansu ba. Komai namiji ya yi sai akirashi ado Yaya? Bayan kuma idan aka yi masa duban tsanaki dodon adone ga rayuwar ɗiyar mace. Wannan wace irin rayuwa ce da farinciki da nutsuwar mace basu da mahimmanci a gidan aure? Wace irin al’ada ce ke mantawa da cewa mace ma abar halitta ce mai zuciya a cikin ƙirjinta?”

Jijjigata ta shiga yi, tana jin wani irin karsashi a ƙasan ranta. Wai yaushe ne ɗiya mace da rayuwarta za su huta a doron ƙasa? ‘sai sun mutu’

Wani sashi na zuciyarta ya ba ta amsa. Da hanzari ta girgiza kanta tana ƙoƙarin ɗago da ƙumajinta gudun raunannar ƴar uwarta. Bayanta ta ci gaba da bubugawa, murya a tausashe ta furta,

“Rayuwa ba komai ba ce, kowa ce mace da ki ka gani da irin nata ƙalubalan. Duk macen da ta ce miki ba ta da matsala a gidan auranta ƙarya take miki, yaudararki take yi. Rayuwa ce da lissafi baya haɗata, rayuwa ce da ta bambanta da kintacen zuƙatan masu shiryata. Kadda ki yi yaƙinin farata da matsala, haka kuma kadda ka yi ganganci ginata akan turbar da za ki yi danasani…”

Kai ta kaɗa kamar marayan ɗata, ta taune gefen bakinta har sai da ta soma jin gishiri-gishiri na bin tsakiyar wushiryarta,

“Me ya sa ? Haka rayuwar mata za ta kasance? Kullum su ne koma baya? Na ji aure shi ne mutuntakarmu, shin aljannah ba ta samuwa ga ɗiya mace ne sai dole ta hanyar aure? Idan ba ki yi aure ba ke ce lallataciya, amma kuma yayinda kika karɓi alamtuwar martabar auren sai ki zamo baiwa? Baiwarma ba irin wadda za ta amsa sunan Baiwa mai bauta ba, sai ki zamo baiwar da za ta karɓi kowace ƙasƙantaciyar rayuwa saboda kawai an maƙala miki kalmar nan ta mace matar aure…?”

Zuwa lokacin kuka ya ci ƙarfinta, ta zame daga riƙon da ta yi mata tana sassheƙa da girgiza kai,

“Gaba ɗaya rayuwar wata macen abar tausayi ce, ita ɗin ba ta tsinanawa kanta komai. Wata irin bishiya ce ga rayuwar na raɓe da ita da rassanta basa amfanar da ita sai dai wasunta. Ƙwarai ina tausayin rayuwarmu domin tattare take da masu buƙatuwarta da yawa. Bishiya ce guda ɗaya amma ƙarƙashinta zaka riski tarin masu buƙatuwar kusanci da shan inuwarta. Ba dan komai ba sai dan dukansu rayuwarsu na buƙatarta. Gata dai da rauni wanda ita tafi cancanta da a tausayawa amma kuma kash!…

Sau tari zaki riski ɗiya mace yayinda take yarinta mahaifiya ke kulawa da ita, idan ta girma ta tasa kuma burinta shi ne ya zan kwatantawa mahaifiyata kulawar da take gwadamin? Wanda a wannan lokacin ita kanta mahaifiyar burinta kenan, ɗiyarta ta tasa itama ta samu abokiyar taya hidimar rayuwa.

Tafi-tafi ƙannanta na buƙatarta wajan hidimarsu. Yau da gobe sha’awa da burinta kan sauka akan ni ya kamata in ɗauki hidimar gidanmu ta fannin aikace-aikace badan komai ba sai dan yadda aka gindaya tunaninta akan hakan. A kwana a tashi a sada ta da ɗakin aure, sannu-sannu sai girma ya hauta. Hidimar gida da ta maigida, kwanci tashi kuma hidimar ‘ya’ya rainonsu tarbiyarsu har zuwa girmansu.
Yayinda su ka tasa fargabarta kulawa da rayuwarsu, idan ta aurar da su kuwa inba dace akai ba tsugono ba ta karewa gareta. ‘Yayanta na buƙatarta, maigidanta na buƙatarta ƙannanta na buƙatarta. Shin Aunty ita kuma wa za ta buƙata? Duk wannan bai isa ɗarsa tausayi da ƙaruwar mutuntakar mace a idanun wasu mazan ba? Sai ma zamowarta abar wofintarwa.Anya akwai mafi cancantar dacewa da a tausayawa sama da rayuwarmu.?”

“Fatima!”

Ta faɗa da murya mai zurfi, ido ta saka cikin nata na wasu daƙiƙu su ka yi kallon ƙuda.
“Nasan ke ake zallunta, amma hakan ba zai sa in ƙi baki haƙuri ba, wata rana sai labari. Duk wani yunƙuri da zaki yi yanzu ba shi da wani alfanu.”

Kai ta kaɗa tare da lumshe idanunta. Sosai take jin tsanar hallayar mijinta har cikin ranta tare da soyayyar Mama Khadija har tsakiyar ranta. Sake dafa kafaɗar Fatima ta yi, amma kuma ta kasa furta komai. Idanu ta runtse komai na wulga mata daki-daki.
Da wani irin karsashi zuciyarta take matsewa. Karo na ba adadi take jin kewar kusanci irin na ƴan uwantaka. Ƙasan ranta tata rayuwar take haskowa. Tana jin ina ma tana da me ƙwarara mata guiwa kamar yadda take ƙarfafawa Fatima. Ina ma tana da wanda za ta ɗora kanta aka kafaɗarsa ta yi kuka! Ya Allah koda ba ta sami mafita, koda bai share mata hawaye ba ya furta mata cewar,

‘Ki yi haƙuri ɗiyarki za ta dawo gareki. Za ta yafe miki kuma za ta yi miki uzuri’
Duk da ta shan jin kalaman daga umarnin zuciyarta, amma tana muradin mai furta mata su cike da ƙarfin guiwa. Tana son a faɗa mata komai zai wuce kuma yaushe. Tana buƙatar nauyin da ƙirjinta ya yi ya sauƙaƙa. Tabbas tana buƙatar wannan. Tana tsoron ranar da haƙƙin Maryam zai soma walagigi da rayuwarta.

Kaddara

Sauri take kamar mai niyyar tashi sama, burinta kawai ta kai wajen da zuciyarta ke muradi. Wata mota ce ta tsaya a ƙusa da ita, da sauri ta ƙarasa jikin motar,
“Hajiya don Allah ki taimaka mini yarana ba su ci….”

Glass ɗin motar ne ya buɗe, ta zaro ido cike da mamaki, fuskar da ta gani ta yi matuƙar ɗaga hankalinta,

‘Kada ki bari wani cikin ahalinku ya yi ido huɗu da it ko wani nata’
Kalaman bokanta suka yi mat dirar mikiya, da hanzari ta zuge glass ɗin motar, yadd fuskar Khadij take zane a fuskar Maryam wane ganganci zai barta ta bari Mama ta ganta. Bayan babu bin da Mamar take buri a ɗan tsakanin tun da ta fahimci aikin da ka yi wa Mamar ya ware.

Sake kallon Mamar ta yi, ta ga hankalinta na wani wuri ta saki ajiyr zuciya,
‘amma me ya kawo Maryam garin Katsina?’

Ta ayyan a ranta. Ganin kanta na neman fara ciwo ya sanya ta haƙura, amma ta ƙudurce dole ta ɗauki mataki. Domin kere n yawo zabo na yawo wata rana za a iya haɗuwa. Tana hango yadda Maryam take kallon motarta cike da buƙatuwa. Wani abu ta ji ya matse zuciyarta kamar ta taimaka mata,

‘Kadda ki soma’

Wata zuciyar tace da ita. Danja n saki ta bula mata ƙura tare da harba motar kan titi tana godiy ga ubangiji. Jiki a mace ta juy wani ɗaci na cin ranta. Yau rana ce da ba za ta manta da ita ba, rana ce mafi muni a rayuwarta rana ɗay da ta soma bara don samawa ‘ya’yanta abinci.

Rana ɗaya da ta yi gamo da wani da za ta iya ɗaga yats ta ce danginta ne sai dai kuma hakan ya kasa zama alfarma agareta. Ranta babu daɗi sam ta juya ta koma gida. Tafiya take tana tunanin fuskar Yaya Kulu da kuma irin kallon da ta yi mata mai cike da tsana. Har ba ta san inda take saka ƙafafunta ba.

A zafafe ta ɗaga ƙafarta ta nufi tsallaka wawakekiyar kwatar, data raba tsakanin layinsu. Wani irin juyawa ƙoƙon gwuiwarta ya yi ya lanƙwasa take ta durƙushe. Wasu hawaye ne su ka zubo mata, ba ta damu ta goge ba ta miƙe cike da ci-da-zuci ta cigaba da tafiya.

Ɗai ɗai kun mutanen da ke zaune a wajen su ka bi ta da kallon tausayi, wasu kuma na ganin bekenta da ganin ita ta jefa kanta a duk yanayin da take ciki. Ƙofar wani nakasasshen gida ta ja burki, kallo ɗaya za ka yi masa ka tabbatar ya ɗauki shekaru.

Ƙwaƙƙwarar tsawa mai ƙarfi za ta iya kai shi kushewa. Tura ƙyaure ta yi wanda ya kasance na langa-langa, ta shiga. Wasu yara ne guda uku su ka nufo ta da gudu su ka ruƙunƙume ta.

A karo na biyu ƙwalla ta sake biyo kuncinta. Ledar hannunta ta kunto ta miƙa musu su ka soma cin abincin hannu baka hannu ƙwarya. Tana gefe tana dubansu. Yunwa take ji amma ganin halin da yaran suke ya sa gaba ɗaya ta ji komi ya fita a ranta. Kukan ƙaramar ta tsinkayo tana faɗin

“Mamma ki ce shu bai,min.”

Da muryar tsamin baki irin na ƙananan yara masu ƙarancin shekaru. Share hawayen ta yi tana murmushi,ta ce, “ku bar mata kun ji!” Kallonta su ka yi kamar masu neman ƙarin bayani, sai su ka saki ledar suna ja baya duk su ka raɓe a bango kamar ƙadangaru. Ɗaya bayan ɗaya take sauke idanunta a kansu, wani na taɓa zuciyarta mai zafi.

Zuciyarta ta dinga tuna shuɗaɗun al’amuran da su ka cakuɗa duniyarta da launin zafi irin na alƙalamin ƙaddara, wasu taurari masu ƙuna ne suke giftawa a idanunta.

Abubuwan da su ka gudana cikin rayuwarta sun bar mata tabo mara gogewa tamkar yau faifan yake gara mata.

Sosai take ajiye shi a wani gurbi da take ganin ita kaɗai ta cancanci jin ɗacinsa, komai na yawo cikin kanta yana ƙuntata duniyarta tana kallon yadda al’amarin ya fara daga rubutu irin na alƙalamin ƙaddararta, ya dinga juyin waina da rayuwarta duk da ƙanƙantarta.

Ta gamsu ƙwarai idan ya tashi rubutunsa ba girma ko cancanta yake dubawa ba. Ba zaɓi ake badawa ba bare ta ware kanta daga masu rungumo kundin da ke ɗauke da shafuka masu tsauri.

Ta yi amanna kan cewa kowa da irin shafin da yake buɗewa kuma dole ya karanta, tana mamakin masu nuna yatsa kan rubutun da babu magogi a kansa. Komai nata ya zo mata a sabuntaccen al’amari. Takan ji an ce wai gidan aure shi ne mutuncin mace da duk wata martaba tata, amma nata gidan auren shi ne silar dagula rayuwarta.

Ta zaɓi aure matsayin mafitarta ko don cigaban marayun ƴaƴanta amma ya maisheta maƙiyiyarsa. Ba ta san me ya sa san zuƙata ya gindaya tsakanin mu’amalar ahalinta ba sama da zumunta.

Sai dai tana da yaƙinin komai na da nasaba ne da shu’umancin mata. A wannan gaɓar tana buƙatar wanda zai sabunta rayuwarta fiye da tsumayinta. Ko ba komai tana buƙatar wanda za ta ɗora kanta a kafaɗarsa ta faɗa masa damuwarta. Ta na mamaki da sau tari al’umma kan manta cewa kowane giɓi ga rayuwarka yana da sanadi.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 4.3 / 5. Rating: 7

As you found it interesting...

Follow us to see more!

Kuskuren Wasu 2 >>

1 thought on “Kuskuren Wasu 1”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×