Skip to content
Part 22 of 58 in the Series Rai Da Kaddara by Lubna Sufyan

Yau da gobe abin tsoro, ba a yanda ranaku suke karewa zuwa daren da yake wayewa da safiya ba, ba kuma a yanda kowacce rana take kara kusanta dan Adam da kabari ba, rashin tabbas din da yake cikin yau da gobe yafi komai tsorata Dije da dan ta ya makalawa Daada yana sa sunan nata fara bacewa a bakunan mutane. Ko Julde ta kalla sai ta kara sallamawa da lamarin duniya. Sai taga kamar jiya ne Abu ta saka mata shi a hannun ta, amman yanzun gashi nan da shekaru uku cur a duniya. Ko wanka tayi mishi ta shirya shi sai taita kallon shi.

Allah me kyauta da kari, ko a mafarki bata taba hango zata haifi kyakkyawan yaro kamar shi ba, bata da muni, amman babu wanda zai sakata a layin kyawawa, hasken fatar dai zatace na Datti ne da nata, amman na Julde kalar shi daban ne, ga fatar shi a murje irin ta yan binni da take gani idan sun kawo ziyara kauyen nasu. Ga wata irin sumar fulani da take kan Julden, a nannade irin ta Datti, kuma kan a cike yake har kusan gaban goshin shi. Misalta kaunar da take ma tilon dan nata duk da irin kunya ta dan fari ba zata misaltu ba. Dan takan kasa yin kawaici a lokutta da dama a gaban mutane, ko idan taje gidan su.

Ko juma’ar da ta fita da taje, kiriniya irin ta yara yana wasa yayi tuntube ya fadi, bata san ta mike ba sai da taji babbar yayar su wato Hanne tana salallami.

“Dije…yau naga abin da yafi zare tsayi ni Hanne… To je ki dauke shi, ni bari in zauna.”

Tukunna ta koma ta zauna a kunyace, dan ma ta fara sabawa da surutun da akeyi mata akan yanda bata iya boye son da take masa, taya zata fara boyewa bayan tayi bari bayan samun shi? Idan kuma shine kwai daya da take da rabon gani a duniya fa? Ba zata bata lokacin da ta samu tare da shi wajen nuna kunyar dan fari taki jan shi a jikinta ba. To na Datti ma ya zarta na kowa, halayen shi babu wanda bata gama sani ba zuwa yanzun, don yau da gobe tafi karfin komai. Abin fada da bana fada ba a wajen Datti duka dayane, baka kuma isa kace zaka fahimtar da shi kan abinda ya rigada ya raya ma zuciyar shi ba.

Tun tana kuka harta fara dakewa kan wasu lamurran na shi, tunda ci da suttura Datti fitar da kudi yake yana mata kamar bai san ciwon su ba. Haka yan uwanta baya gajiya da hidimta musu, kawai dai hakan bai taba tserar da su daga tijarar shi idan sun shiga sabgogin shi ba. Yanda ta fahimci halin shi kusan suma tana tunanin sun fahimta, ko kuma alherin da yake musu ne ya kashe bakunan su, tunda in dai zaka kaskantar da kai ka nuna ma Datti girmamawar da yake so to zaka more shi, kuskuren dai da zaka yi shine kayi wani abu da zai nuna alamar cewa kana so ka fishi, ko da kuwa takalmi ne ka saka da yafi na shi haske a fuskar shi zaka fara ganin yanda baiji dadi ba, kafin alkhairin da yake giftawa a tsakanin ku ya dauke.

Duk wasu hanyoyin samun sabani a tsakanin ta da Datti ta san su, tana kokarin kiyaye su, hanyar da bata taba hangowa ba shine Julde. Bata taba hasaso cewa zasu dinga samun sabani akan tilon dan nasu ba. Tun yana jinjiri daya bude baki yasa kuka zai rufeta da fada kamar tasan dalilin kukan shi ko ma itace dalilin gabaki daya. Haka cikin dare zai ce sai ta goya shi ko zaiyi shiru. A gaban Datti idan har Julde ya saka kuka ranta saiya baci, barna ta yara idan yayi bata da damar tsawatar mishi saboda Datti zai rufeta da fada kamar zai daketa. Na rana daya bata taba furtama wani yanda fadan Datti yake tsaya mata a rai ba.

“Adda Abu bana so Julde ya taso a sangarce, bana so ya taso bai san meye kuskure ba”

Ta ce ma Abu cikin sanyi murya wani yammaci ta shiga gidan

“Amman Baban shi baya so, kina ganin bai kai shekarun da zan fara tsawatar mishi ba?”

Ta karasa maganar tana kallon Abu da ta bata dukkan hankalinta.

“Shi icce tun yana danye ake lankwasa shi ai, banajin akwai wani kayadadden lokaci da yaro zai kai kafin a fara nuna mishi yayi kuskure…”

Kai Dije ta jinjina.

“Tunani na dana Baban shi sunyi hannun riga a wannan bigiren, kukan rashin dalili idan Julde ya saka sai kin dauka lefina ne yanda zai rufeni da fada…”

Wannan karin da kwalla cikin idanuwan ta da alamar kukan dake son kwace mata a muryarta ta karasa maganar. Abinda Dije bata sani ba shine daga Abu har Hammadi sun kula da kaunar da Datti yake yiwa Julde gurguwar kauna ce, duk da ita Abu ta mishi uzuri da yanda kaddara ta zo mishi akan haihuwa.

“Dan ya samu basu zauna bane a baya shisa, ana kara haifar masa wani zakaga ya rage…”

Ta ce ma Hammadi da yayi mata magana ranar da Julde yayi bacci a gidan su, amman Datti yayi sallama yana shiga har ciki ya sabi dan shi a kafada yayi musu bankwana ya tafi. Ba shi bane na farko, ranar ne dai Hammadi yayi magana, ita kanta Abu ranar farko ranta ya sosu, har kuka tayi duk da ta nuna ma Hammadi abin bai taba zuciyar ta ba. Rashin da akwai ciwo, kaddara ce kuma da sai mai juriya ne yake iya karbarta da hannu biyu. Kome wani zaiyi maka akan yaro sai kaji tamkar yana goranta maka rashin samun naka rabon ne da bakayi ba.

“Bamu samu ba har yanzun Abu, amman kina hango zakiyi abinda Datti yakeyi akan Julde idan Allah ya bamu rabo?”

Dariya tayi, tsakanin yan uwa sai Allah, ita matar Hammadi ce, idan yau kaddarar rabuwa ta gifta musu ko a lahira sai in suna da hakkin juna ne zasu hada hanya tunda babu yaran da zasu hada su, amman shi da Datti har abada zasu kasance yan uwa, kuma tarin kaunar da yake mata ba zata kama kafar wanda yakewa dan uwan shi ba, tana kokarin kiyaye harshenta daga furta wani abu marar kyau daya dangancin Datti, ko da kuwa wannan abin halin shine, kai ko da ma ace a hirane irin wannan da sukeyi, idan Hammadi ya huce ya tauna zantukan nata ran shi zai iya sosuwa, a kasan zuciyar shi zaiji haushin ta.

“Kar dai mu cika baki kan abin da bai faru ba tukunna.”

Murmushi Hammadi ya yi.

“Ai shikenan, ba dai kyason in fadi laifin Datti.”

Dariya ta sakeyi tana kawo mishi wata hirar da zata kore wadda suka gama. Amman ba ranar kadai bane ya furta damuwar shi akan makauniyar kaunar da Datti yake nuna ma Julde.
“Nasan kina hakuri, zance ki kara hakuri ne Dije, watakila dan yana ganin Julden ne kawai a gaban shi yanzun…idan Allah ya kara kawo muku wani rabon zaki ga ya rage.”

Murmushin da Dije tayi mai ciwo ne.

“Idan kuma shi kadai ne rabon fa?”
Maganar ta taba Abu har zuciyar ta.

“Sai kiyi addu’a, komai zai tafi dai-dai… Idan baya nan yayi kuskure kiyi kokarin nuna masa…shima Dattin ki fahimtar da shi illolin dake cikin tasowar yaro babu kwaba…”

Murmushin dai Dije ta sake yi tana furta

“Hmmn…”
Saboda bata da kalaman da zata fara amfani da su wajen fada ma Abu cewa Datti baya cikin jerin mazan da zaku zauna kuyi magana ta fahimta da shi, ba irin Hammadi bane ba, bashi da lokacin da zai saurare ta, komin muhimmancin shawarar da take da ita kuwa. Ta jima da gane wannan, bai daina yi mata ciwo bane ba duk idan ta tuna, shima ta san lokaci zai koya mata sabawa da hakan. Safiyar ranar tun da ta tashi take jin ta wani iri, komai baya mata dadi, dakyar tayi wanke-wanke bayan fitar Datti, ta share gidan. Julde ma wajen Abu ta tura shi tasan zatayi mishi wanka acan. Ta koma ta kwanta, bata tashi ba sai azahar, sai kuma lokacin tayi wanka.

Tun lokacin ta hada wuta tana dora tuwon dare takan jima in ba taji marmarin wani abu ba bata dora girkin rana ba, sai dai ta shiga gidan Abu su dafa acan, tunda nan Hammadi yake aikowa a karbar musu abincin rana shi da Dattin. Da kyar kuwa ta karasa girkin, sai da tayi dana sanin dora shi bayan tayi talge, taji daman ta cewa Abu ta saka abincin dare da su. Ta so sake watsa ruwa gab da Magriba sai ta gujewa camfin cewa wankan yammaci likis na saka zazzabi, tunda daman ba dadin jikinta take ji ba. Ta fito bayi kenan tana daura alwala Julde ya shigo da gudu yana fadawa bayanta.

“Daada na ci nama, Nenne ta bani nama.”

Yake fadi cikin yaren fulatanci, yana kiran Abu da Nenne kamar yanda ta koya mishi. Itama ta taso mahaifiyar ta na yara musu a gida, amman basu cika mayarwa ba tunda hausa tafi karfi a cikin gidan. Zama da Julde dole yasa fulatancin nata kara gogewa saboda yakan yi kwanaki bai furta kalma guda daya da hausa ba, yana da kishin yaren shi na ban mamaki. Kuma yana mata fada idan yaji tana ma Julden hausa, in baya nan kuwa takan yi mishi saboda nata dangin bakowa yake jin fulatanci ba, kuma hausar itace yaren mahaifinta, idan akabi ta silsila ita bahaushiya ce, bata ga dalilin da za’a haramta mata koyawa danta yaren ta ba.

“Ta kyauta, kace mata ka gode? Daga mun baya…”

Sake kwanciya yayi a bayanta don tana tsugunne ne, da ta idar da alwalar ma da shi ta mike saboda ya zagaya hannuwan shi ya makale mata wuya, ta samu ta sauke shi yana neman saka mata kukan sangartar daya saba. In ka shigo gidan su daga soro katon tsakar gida zaka fara samu da aka shafe da sumuntin da sai gidajen wanda yaci ya tayar da kaine zaka samu da shafen sumunti a cikin kauyen. Dan Datti da yake bata labari yace a cikin garin Katsina ya aika aka siyo sumuntin da ana ginin gidan, amman kamar sauran gine-ginen kauyen nasu ma na kasa ne, sai dakuna guda hudu, cikon na biyar din kayan abincine ake ajiyewa, bayi, sai dan karamin daki da aka rufe daya zama wajen girki da inda take ajiye kwanoni, idan bama ana damuna ba, a bakin kofar take ajiye murhun, nan take girkin ta.

Daki biyu ma zata ce suna amfani da shi, nata sai kuma na Datti, sauran akwai ledar daki a ciki da katifu da Datti ne ya siya ya saka, amman in ba ta shiga ta share ba, ba zama takeyi a ciki ba. Dakinta ta nufa da Julde da yake biye da ita, ganin ta shimfida darduma ta dauki hijabi ta tayar da sallah yasa shi hayewa kan gadon karfenta da yake cikin dakin ya kwanta, lokacin da ta idar har yayi bacci, ta dan jima a zaune tana rasa abinda yake damun ta, ba zatace rashin lafiya takeyi ba, zuciyarta take ji a cunkushe. Tana nan zaunen dai har akayi isha’i ta tashi ta gabatar da tata. Ta mike ta ninke dardumarta, ta cire hijabin tana ninkewa ta hada ta rataye su jikin karfen gadon tana fita tsakar gida.

Tasan inda duk Datti yake yana hanyar gida, da yakan dade bai shigo ba, ko da ta juyo muryar Hammadi shi saiya kara jimawa kafin ta gan shi, zai zo mata da labaran da suke tabbatar mata da ya tsaya hira ne. Amman tun da ta haifi Julde rabon da yayi wannan dadewar, duk da lokutta da yawa idan ya dawo Julden yayi bacci, haka zai dauke shi ya kwantar kan cinya, tun tana magana idan zaici abinci daya ajiye shi har ta koyi saka masa ido in dai akan lamarin Julde ne. Kofi ta dauko ta dauraye saboda ta rigada ta saba dan gudun ko wani abu ya shiga ciki, musamman kananun kwari da kifewar da tayi ba zai hanasu samun hanyar shiga suyi bidiri a cikin kofin ba.

Ta bude randar da take tsakar gidan ta saka kofin a ciki ta dibo ruwan tana kaiwa bakinta, dai-dai lokacin da taji kamar an jeho wani abu, kafin wani irin gigitaccen kuka da Julde ya saki ya sata yadda kofin tana nufar daki ciki hanzari, da yake akwai hasken fitilar kwai a cikin dakin, batayi wahala ba wajen ganin fadowa Julden yayi daga kan gado, cikin rawar jiki ta karasa tana daga shi, tako yi karo da jinin da yake fita daga bakin shi da ya sa hanjin cikinta yamutsawa. Cike da zafin nama ta dauke shi tana karasawa ta dauko fitilar kwan tayo waje, gurin magudaji ta nufa da shi ta tsugunnar, kukan da yake da jinin dayaki tsayawa na haduwa suka kara gigitata.

Dakyar ta samu ta dauko buta ta fara wanke mishi bakin, tana dubawa taga wani irin rami a leben shi daga ciki kamar hakorin shi ya datsa a jiki, har harshen shi yanka ne, leben kuwa ta ciki da waje, jini gullama yake fita kamar ba wankewa takeyi ba, bata taba ganin tashin hankali irin wannan ba, haka tunanin ta yake fada mata kafin Datti ya shigo gidan yana fadin.

“Me ya faru Dije? Me ya same shi?”

Cikin fulatancin shi da yake fita daki-daki kamar don harshen shi kawai aka kirkiri yaren, yana karasawo yaga kalar jinin da yake zuba fisge shi yayi daga hannun ta yana daga shi zuwa jikin shi hadi da duba shi sosai, kukan nashi ya fara tsagaitawa, sai ajiyar zuciya da yake saukewa, jikin shi harya dauki dumi saboda azaba.

“Me ya same shi wai?”

Ya sake tambaya yana saka idanuwan shi cikin nata.

“Fadowa yayi daga kan gado yana bacci.”

Sai da Datti ya sake duba Julde da jini har lokacin bai daina fitowa daga bakin shi ba sannan ya sake kallon ta, wannan karin kallon na sa wani abu ya tsirga a cikin ta

“Na dauka nace in dai ba zaki zauna ki tsare shi ba karki sake dora mun yaro kan gado?”

Kai Dije ta jinjina mishi.

“Yanzun ma fitowa kawai na danyi…ka…”

Bai bari ta karasa ba ya katse ta.

“Ban isa ba kenan ko? Ban isa ba shisa kika bar mun yaro shi kadai…”

Idanuwanta ta sauke daga cikin nashi tana neman danne bacin ran daya taso mata, sai dai kamar ta dora shine akan wanda tayi shekaru tana hadiyewa, sam sai taji shi tsaye a makoshin ta har tana jin dandanon shi kan harshen ta, musamman daya cigaba da fada yana hargowa kamar Julden ba daga jikin ta ya fito ba.

“Watanni tara da kwana goma sha bakwai…”

Ta furta da nisantaccen yanayi a muryar ta tana dagowa ta saka idanuwan ta cikin na shi.

“Kwanakin da yaron nan yayi a cikina, ba zan rantse ba amman babu wata shakuwa da zakaji kayi da shi da zata kamo iya wannan lokacin.. Me yasa? Me yasa kullum kake nuna mun kamar kafi ni son shi? Kamar ni ban iya kula da shi ba?”

Fuskar shi bata boye mamakin da ya cika zuciyar shi ba, bai taba fada ta mayar mishi ba, balle harta dankara mishi magana haka. Da yawa zasu ce yau daya ya kamata ya kauda kai, amman shi ba kamar sauran maza bane ba, tun kafin ya san menene aure ya rigada ya hasaso babu macen da zai aura da ta isa tana karkashin shi yana fada tana mayarwa, duk a fadin duniyar shi a yanzun babu wannan macen. Shisa bacin ran shi ya ninku har wani jan haske ya gani ya gilma ta cikin idanuwan shi.

Daga Datti har Dije idan wani zai tsare su yace su maimaita maganganun da suka fada ma juna ba zasu iya ba, ita dai zata rantse a cikin fadan akwai inda ya fadi.

“Nayi dana sanin auren ki.”
Shi kuma zai rantse ta ce mishi.

“Idan ka haifu ka sawwake mun mana ka huta, auren naka ka dauka jin dadin shi nakeyi?”

Sai dai kowa a cikin su hanyar da zaibi a goyi da bayan shi yake nema, ko lokacin daya daga hannu yana marin ta, ya manta ma Julde na rike a hannun shi, haka lokacin da ya furta.

“Kije na sakeki saki uku! Ki barmun gida da yaro kiga idan ba zan iya kula da shi fiye dake ba.”

Kafin hawayen da suke cikin idanuwanta su zubo wani irin yanayi da ya girmi dana sani ya rufe shi kamar bargo, shirun daya biyo bayan kalmomin nashi na gauraye gabaki daya gidan har yana jin takun Dije cikin kunnuwan shi lokacin da ta juya tana nufar dakin ta. Kamar wanda aka dasa haka ya tsinci kan shi da kasa motsawa har ta fito da lullubi tana saka takalman ta, baiyi yunkurin hanata ba, duk kuwa da ihun da zuciyar shi take mishi, da idanuwan ya bita harta fice daga cikin gidan. Sai lokacin kafafuwan shi suka motsa yana bin bayanta, hannun riga sukayi, tayi dama inda zai sadata da gidan su, shikuma yayi haggu yana shiga gidan Hammadi babu ko sallama
“Datti…lafiya dai ko?”

Hammadi ya tambaya don suna zaune a tsakar gida ne kan tabarma, sun saka fitilar kwai a gaba saboda abu da take kokarin saka zare a cikin allura tana son dinke rigar Julden da bata san yanda akayi ya warware dinkin ba daga gefe, shikuma Hammadi yana mata dariyar tsufa ya kamata ganin ya fara ja da baya, zata mayar mishi da martani kenan Datti ya fado musu, tama riga Hammadi mikewa tana karasawa ta karbi Julde da yayi luf a kafadar Datti, baiyi musu ba ya mika mata yaron, salatin ta na isa kunnen shi da wani irin nisa saboda yanda yake ji.

“Na saki Dije… Hamma na sake ta.”

Ya fadi kamar wanda maganar take ba mamaki. Saboda jin shi yake kamar yana yawo saman iska.

“Bangane ka saki Dije ba, me tayi maka? Me ya faru?”

Hammadi ya jera mishi tambayoyin cikin tashin hankali da mamaki, dan Abu ma maganar taji ta dake ta, kan tabarma ta ajiye Julde tana kallon Datti tana jiran karin bayani.

“Fada muke yi, bansan ya akayi ba, kawai na sake ta.”

Numfashi Hammadi yaja yana sakin shi tare da fadin.

“Inalillahi wa ilaihi raji’un… Datti kaga irin illar zafin ran da nake guje maka ko?” Shiru yayi, daga cikin jikin shi yake jin wani abu yana tsirgawa da baisan yanda zai fara misalta shi ba.
“Ina Dijen yanzun?”

Cewar Hammadi.

“Ta tafi gidan su…”

Takalma Hammadi ya zira,

“Sai ka wuce muje ayi ma tufkar hanci tun yau.”

Kai Datti ya girgiza mishi, baiyi wani ilimin addini ba, amman yasan hukuncin saki uku a musulunci.

“Duka ne… Saki uku nayi mata.”

Saida Hammadi ya dafa bangon wajen tukunna ya iya komawa ya zauna, kafafuwan shi rawa sukeyi da danyen aikin da Dattin yayi, a gefe guda kuma zuciyar shi na hasaso mishi tarin kunyar mahaifin Dije da zai kwasa, saki uku, sakin tozarci, ba Dije kadai ba, har su ya tozarta tunda bai duba girman da yake tsakanin su ya nemi shawarar su ko suna da ta bayarwa wajen bullowa lamarin ba kafin ya yanke hukunci.

“Ka kyauta Datti…”

Hammadi ya fadi muryar shi na rawa ya juya ya kalli Abu da itama ta zauna, hawaye kawai ke zubar mata, Dije ba mai yawan magana bace ba, amman a cikin idanuwanta zaka iya karanta damuwar da take boyewa a cikin zuciyar ta, kowa kuma yasan halin Datti zai jinjina ma kokarin da takeyi na zama da shi, tunda aure ya girmi bayar da ci da sha, da kuma suttura, kana bukatar samun kwanciyar hankali daga wajen mijin ka. Amman rana daya Datti ya nuna mata wannan hakurin nata ba abakin komai yake ba, ita dinma bata da wani muhimmanci a rayuwar shi, zai iya datse igiyoyin daya hadu zama inuwa daya cikin kankanin lokaci.

“Zan dawo da ita, sai tayi wani aure in dawo da ita”

A karo na farko da Hammadi ya kalle shi bacin rai shimfide a idanuwan shi.

“Me ka dauki mutane? Me ka dauki auren gabaki dayan shi? Datti ka fitar mun daga gida wallahi kafin inyi abinda mu duka zamuyi dana sanin shi daga baya…”

Ganin da gaske Hammadi yake da kuma kasancewar rana ta farko daya tabajin ya daga murya sai jikin shi ya karayin sanyi. Juyawa yayi ya fita batare da ko Julde ya dauka ba. Yabar Hammadi da Abu suna jajanta danyen aikin da yayi, kafin Abu ta iya mikewa dakyar tana tona sauran garwashin daya rage cikin murhun da tayi abinci dare ta dora dan ruwan zafi a cikin tukunya a kai don ta gasa ma Julde bakin shi da yaji ciwo. Tana ta kallon yaron yana bacci batare da yasan abinda mahaifin shi yayi wa mahaifiyar shi ba. Ta kuma kasa daina sharar kwallar da take ta taruwa cikin idanuwan ta.
*****
Kamar wasa kwanaki suka dinga wucewa har Dije ta gama iddar ta, zuwa lokacin Datti yayi zuwa yafi goma wajen ta, amman tana kin fitowa ta saurare shi, har Abu yabi kan taje mishi wajen ta ko zai samu ta fito ta saurari me zaice.

“Ta ina zan fara hada idanuwa da ita in kawo mata zance ka? Idan kai baka jin kunya ni ina ji.”

Duka kowa ya juya mishi baya akan abinda ya karba a matsayin kuskuren shi, ya dauka zaman aure ne kawai a tsakanin su da Dije, sai yanzun da yake farkawa tsakiyar dare ya nemi duminta a gefen shi ya rasa, wata irin kewarta ce take damun shi hade da wasu abubuwa da yake tunanin sun girmi ya dora su kan kalmar so. Har mahaifinta ya bi yana bashi hakuri kan abinda ya faru ko zai samu sauki.

“Ba maganar hakuri bace ba Datti, tun kafin kazo Hammadi ya sameni, nasan kaddara, na kuma san kowanne mutum baya wuce kaddarar shi.. Kai da Dije dai Allah ya kadarta zaman ku bamai dorewa bane ba… Sai ku yafi juna kuyi wa juna fatan alkhairi kuma… Hakuri na ba zai sa ta koma gidan ka ba tunda saki uku kayi mata.”

Amman kalaman kara daga mishi hankali sukayi, baya son yaji ana fadin kaddarar zama ta kare a tsakanin shi da Dije. Bai kara shiga tashin hankali ba sai wanda ya biya dan su dinga bibiyar mishi motsin Dijen suka zo mishi da labarin ta fara tsayawa da wasu. Kishi yaji, kishin da bai taba sanin Allah ya halitta masa ba, musamman daren da yaje kofar gidan su ya shaida da idanuwan shi.

“Baka san matata bace ba Iroji? Baka sani ba?”

Ya karasa wajen su yana fadi kamar zautacce harda shako wuyan rigar Irojin,

“Ka sake shi Datti, ka sake shi nace maka… Wanne irin matar ka? Yaushe na zama matar ka kuma?”

Kallon ta yayi, kyallin farin wata na haska mishi farar fuskar ta, hasken shi na ratsa cikin idanuwan ta ya sauke nashi a ciki yana jin tsikar jikin shi na mikewa da wata irin soyayyar shi, har lokacin yana rike da wuyan rigar Iroji da ya samu ya kwace da kyar yana mayar da numfashi.

“Karka kara zuwa wajen ta, hada hanya dani bata da kyau, kar ka kara zuwa mun wajen mata.”

Ya karasa maganar batare daya kalli Iroji da ya sakai yana barin wajen ba, ko babu komai a karkashin Hammadi yake samun rufin asiri, ba zai so yayi ma kanshi sanadin rasa wannan hanyar ba. Amman tun kafin Datti ya auri Dije yake jinta a ran shi, yayi nauyin bakine a wancen lokacin shisa yanzun yazo ya gwada sa’ar shi.

“Meye kake nufi da korar shi? Kasan ko ba shi ba dole zanyi aure ko?”

Ta karasa muryarta na rawa.

“Na sani, zakiyi aure ki fito mu sake yin aure.”
Wani irin kallo take masa.
“Kar kuskuren da nayi yasa ki guje ni Dije… Karki guje mu…dan Allah ki dawomun mu rayu da dan mu, mu duka munyi kewar ki.”

Zuciyarta taji ta karye da kalaman shi da yanda yau ya kwantar da murya yana mata magana cikin yanayin da bai taba ba tun kafin auren su da bayan shi, hawaye masu zafi suka zubo mata, ita kanta bata san tana son shi ba sai bayan rabuwar su, kewar komai na gidan daya rabata dashi takeyi, kewar danta takeyi kamar babu gobe. Danma duk kwana juma’a Abu na zuwa mata da shi, sai ta bar mata shi har sai bayan la’asar ta hada shi da yaro a mayar da shi.
“Daada yaushe zaki dawo?”
Shima Julden yakan tambayeta sai tayi mishi dabara tunda bata da amsar bashi. Tana kewar har Abu ma da hirarrakin su, don sun shaku da juna.

“Ba da kan ka kawai ka rabani ba Datti, harda abubuwa da yawa dana saba da su.”
Ta fadi cikin dacin rai.

“Na sani, kiyi hakuri ki bani dama in gyara kuskuren da nayi…”

Bata amsa ba, baya kuma bukata, a wajen shi shirunta amincewa ne, kalamai ya cigaba da yi mata da baisan daga ibda suke fitowa ba shi kan shi har saida tace,

“Wa kake ganin zai aureni ya sakeni bayan wata daya?”
Murmushin nasara ya yi.

“Wanda zan ba shanu biyar idan ya amince.”

Itama murmushin ne ya kwace mata, su duka biyun suna rasa dalilin rabuwar su in har suna jin haka akan juna.

Basu sani ba
Basu san rabo ne ya fito da Dije ba.
Rabo mai ciwo.

*****

Idan littafi na yayi muku dadi, ku taimakeni ta hanyar bude account da Bakandamiya don hakanne kadai zai baku damar yin like na shafin duk da zan saka da kuma yin comment ko da na fatan alkhairi ne. Hakan zaisa website din Bakandamiya su biyani.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 3.5 / 5. Rating: 19

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Rai Da Kaddara 21Rai Da Kaddara 23 >>

1 thought on “Rai Da Kaddara 22”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×