Skip to content
Part 27 of 39 in the Series Ummu Hani by Fadimafayau

Kukan da Ummu tasa ne yasa dukkan su kallon bakin kofa ba wanda ya tsanmaci ganin ta ba ɗakin ta shiga kai tsaye gun Faruk ta nufa tama mance cewar iyayan sa fa sirikan ta ne hannun sa ta kamo tana kuka,

“Dan Allah Faruk ka jikaina karka sake ni wallahi bazan iya rayuwa ba auren ka ba, sakin da zaka min shi ne zai zamto cutarwa a gare ni bawai zama da kai ba dan Allah ka dubi rayuwa ta in har ba son gina kiyayya maras yankewa tsakani na da kai ba kar kayi sakin nan bazan taɓa yafe ma ba.” Zuru kawai ya yi yana kallon ta ran sa yana ƙuna yana ji yake ina ma zai iya ɗauga koda hannun sa ne ya goge mata hawaye sai dai ina bazai iya ba.

Mami ce ta taso ta rungomo Ummun yi shiru kinji Hani karki damu nima ban goyi da bayan sakin nan ba koda kuwa hakan na nufin zaki kalleni a matsayin wadda ta so ɗan ta amma bazan so abin ya masa ba ga jinyar jiki ga na zuciya indai har ina raye bazaki ƙara kuka kan bakyason saki ba in kinga kin rabu da Faruk to keda kanki kika buƙaci ku rabun a wannan lokacin ne ko da ina so bazan iya tauye miki hakkin ki ba.

Girgiza kai Ummu ta hau yi “Indai ni ce bazan taɓa neman rabuwa da Faruk ba har abada. Na gode Mami da kika goyi da baya na.”

Dady bai ce komai ba ya fice daga ɗakin inda Mami ta bi bayan sa a lokacin ne Faruk ya juyar da kansa gami da rufe idanun sa kamar me barci, Murmushi Ummu ta yi dan ta gano fishi ya yi matsawa kusa da shi ta yi cikin da shasshiyar muryar ta da tasha kuka ta ce haba Mijin Ummu bama fishi da juna fa dan Allah kayi hakuri a hankula ya kalle ta ni ba fishi nake da ke ba kawai haushin kaina nake ji kina zaman zamanki nazo na fara sonki ba dora miki wahala yanzu da ban san ki ba da duk hakan bazai yiwu ba.

Kuka tasa ni na ce maka kai ɗin wahala in kamin haka baka kyauta min ba, kai ɗin har abada rahama ne a gareni, naji daina kukan and give me a hug matsawa ta yi ta rungume shi.

*****

Shi ko Ayatullah mikewa ya yi yabar gub bayan bacewa ganin sa da Ummu ta yi kai tsaye ɗakin kwanan su ya nufa dan ya gama duty dinsa, bai cewa kowa komai ba ya faɗa gadon sa ko yunwar da yake ji tuni ta bar shi yama rasa mai zaiyi tunani jin sa yake tamkar wani sabon arne wai ya rasa waye zai so sai matar wani da ya tuna haka sai ransa ya baci Astagfirullah kawai yake aransa.

Muryar Abraham ya ji na faɗin mai ya faru zaka sha tea din je in miko ma, No bazan sha ba ya ce taɓe baki Abraham ya yi kawa kanka ya ce sannan ya juya ya ci gaba da duba littafin medical din da ya ke dubawa.

Na gano ta Ayatullah ya ce bayan ɗan shiru da sukai a hanzar ce Abraham ya juyo kuma ba aljana ba ce ko? Ya tambaya eh Ayatullah ya ce kawai, I knew it mutun ce, kwafa Ayatullah ya yi but she’s married with kids, what Abraham ya zaro ido.

Kaima ka yi mamaki ko ban san me zan ba just how can I be in love with somebody’s woman that fact I annoyed me na rasa mai zanyi.

Dariya Abraham ya yi sai me dan tana da miji kawai kaje ka kwatota win her love and make her yours let her make another choice, you most be mad Ayatullah kawaj ya ce kafin yabar ɗakin ransa ba daɗi duk da chan wani ɓarin na ransa na faɗa masa shi ba Zina zai ba Abraham yana da gaskiya ji yake a ransa in har zai iya jawo hankalin ta ta nemi saki ta dawo tasa nothing matters.

********

Fatima kam hankalin ta duk baya jikin ta tun tafiyar su Faruk danma tun batun auren Farun ɗin da ta janyo Abban ta ke fishi da ita duk dauriyar ta ta kare ta yanke shawara kawai zata je ta samu Abban ta rokeshi ya bar ta taje ta dubo Faruk ɗin dan bata son ya warke ya dawo bata je ba bacin haka ma tasan hankalun ta sai ya fi kwanciya in har tana ganin ta.

Abban na ɗaki ta same shi ba yabo ba fallasa suka gaisa kasa ta zube tana kuka nan da nan hankalin sa ya tashi ya taso inda ta ke haba babin Abbanta mai kuma aka miki, ɗagowa ta yi cikin hawaye ta ce ba kai ne Abba ka ke fishi dani ba, share mata hawaye ya yi a’a ni kam baba fishi da baby na ke ce dai baki fahin cen ba.

To Abba ka hakura faɗa a shagwabance murmushi ya yi dama baki mun komai ba, itama Murmushin ta yi tom nagode Abba kuma dan Allah yau she zanje duba Faruk pls don’t say No dan Allah Abba ta faɗa tana riƙe da hannun sa.

Dama gobe nake son muje dukan mu na samar mana jurgi zamu bi na safe, rungume shi ta yi nagode Allah dariya yayi ki cigaba da masa addu’a ki je ki haɗa kayan da zaki ta fi su ɗin, Tom Abba Nagode ta ce kafin ta bar falon.

Fatima na barin ɗakin kai tsaye ɗakin ta nufa inda ta hau haɗa abin da zata buƙata in sunje can, duda ranta babu daɗi kusan tun haɗarin Faruk anma yau sai ta ji sa’ida a ranta sakamakon yafe mata da Abban ta ya yi da kuma yadda da ya yi taje duba Faruk ɗin. Sai can dare ta samu ta runtsa ji take tamkar ta jawo goben ta je ta ga Faruk yadda ta tsara aranta shi ne in har suka je da sunyi kwana kaɗan zata takurawa Dadin su Faruk a ɗaura musu aure dan tasan in har ya warke sarar to tabbas Faruk zai iya cigaba da hutsewa.

Washe gari da Sassafe suka nufu filin jirgi dan tashin safe zasuyi ilai kuwa kan tara sun tashi ayanzu hango kanta kawai ta ke a matsayin matar Faruk.

Da rana sosai suka sauka a garin Abba yai yai Fatima ta tsaya su huta zuwa dare su karasa asibitin taƙi dole ya bita sukai asibitin.

Yau Mami bata zo ba tana masaukin su Ummu ce kawai ta zo ko Muhammad ɗin ma bata tawo da shi ba tana zaune suna hira da Faruk gwanin ban sha’awa bakin sa tar yake yadda suke hirar bama zakai tunanin mai muryar bai da lafiya ba, dariya yake sosai yadda yaga Ummu ta taɓe fuska dan ya zaulaye ta.

Shigowar su Fatima ne ya katsewa Faruk dariya daga shi har Ummu ɗin ba suyi tsanmanin ganin Fatiman ba, ya yin da ita ma Fatimah ɗin jin muryar Faruk daga waje bai sa ta yi tsanmanin zata ganshi a kwance cikin taimakon inji ba.

Yadda taga Faruk ɗin ya tada mata da hankali gefen sa ta je ta zauna ya yin da Abba ya zauna bisa doguwar kujerar dake ɗakin, cikin girmamawa Faruk ya gai da Abba haka ma Ummu hani ta gai da shi yayin da suka gaisa da Fatima ba yabo ba fallasa, Faruk Ummu ta tsurawa ido yana son gano ko taji haushin ganin Fatiman sai dai bai iya gano komai ba.

Bayan fitar Abba ɗakin ya yi shiru kowa cikin su da akwai abinda ya ke saƙawa ckin ransa Fatima ce ta miƙe ta ɗauko towel ta hau goge masa goshin sa tana faɗin ko a kunna fanka ne naga kamar kana jin zafi, karki kara taɓa ni ya ce cikin muryar da take nuna da ace zai iya ɗaga hannun sa tas zai shareta da Mari.

Sun sun Ummu ta miƙe barin sa da robar bayan gidan sa ke jone ta cire ta yi waje tama man ce ɗakin akwai tolet, tsaki Fatima ta ja haba malam ya zaka dinga dizgani gaban wannan kucakar matar taka.

Hararar ta yayi sannan ya ce da zaki ma kanki gata da kin goge sha’awar da kike mun kin kama mai son ki na gaskiya Mansur shi ya da ce da ke, taɓe baki ta yi ni kuma da kai na da ce dan haka dole ka aure ni, dariya yasa kina kyan kyamin nawa ne kike jin zaki iya zama dani.

Kallon sa ta yi cike da tsoro a zahiri ta ce kyankyami kuma, eh kyankyami ina kallon ki tunda kika zauna anan ya nuna inda ta tashi da bakin sa sannan ta karasa da faɗin tunda kika zauna ki kaga robar da Ummy ta ɗauke kike ta ya mutsa fuska hankalun ki bai kwanta ba sai da kikaga ta ɗauke.

Tsaki ta yi kaji da shi koma mai zaka ce aure ne kana jin sauki za’a ɗaura dariya yasa dan ya fahinci yarin yar nan bata sanma wanne irin ciwo ya ke ba kawai ita kwaɗayin zuciyar ta take son biyewa girgiza kai kawai ya yi bai ce komai ba, da ya fahinci ma zata ɓata  masa rai rife idanun sa kawai ya yi ransa a jagule tausayin ummun sa ne kawai ke kai kawo aransa.

Ummu kuwa koda ta fito daga toilet ɗin da ta shiga inda ta saba zama ta nufa yau ba mutane sosai ko dan ba yan ma ba ce oho ranta babu daɗi kwata dan azahirin gaskiya in ta ce bata jin haushin Fatima to ko ta yi karya hasali ma ta tsane ta ji ta ke tamkar ta je ta fito da ita daga ɗakin Faruk ya daina ganin ta.

Ya hange ta lokacin yana kokarin shiga lifter da hanzari ya fito ya bi bayan ta daga ɗan nesa yaja ya tsaya yana nazarin ta da alamu yau damuwar ta da ɗan yawa samun kansa ya yi da ƙarasawa gun da ta ke zaune sallama ya mata kusan ta ɗauku murya sai ta fuskar ta ta yi ta ɗago ta kalle shi sannu ko ya ce da ita, ya ke ta yi sannu Dr yawwa ya ce ayayin da yake kokarin zams kusa da ita.

Ya mai jikin da sauki kawai ta iya cewa dan yau ɗinma kukan take ji ba kuma ta son yi dan ta fahinci kwana biyu zuciyar ta na son zama raguwa, sun jima azaune Ayatullah na dan sata magana lokaci lokaci kafin ta miƙe ni zan wu ce Nagode sosai murmushi ya yi karki damu insha Allahu zai samu sauki Allah ya amsa kawai ta ce tabar gun.

Ya jima agun ransa cike da tunanin mafita a kullun zucuyar sa ƙara son yarin yar ta ke yayin da ya fahinci ita ɗin kullum damuwar ta ita ce mijin ta.

Ummu kuwa samun kanta ta yi da ɗan samun sanyi cikin ranta yar hirar da sukayi da mutumin kusan tun randa suka fara magana haka kawai take tuna shi ba tare da sanin dalili ba duk da kuwa tunanin Faruk ɗin ta kusan shi ke mamaye komai na burnin zuciyar ta.

Inda ta tashi ta tarar da Fatima zaune tana goge masa gumi da alamu bacci ya ke sai dai tana shiga ya buɗe idanun sa gami da faɗin Ummu ba kin dawo murmushi ta yi eh na dawo mijina ta faɗa a lokacin da ta matso kusa dashi gogen fuska ta kinga gumi nake ba kuma na son a kunna fankar nan da an kunna sai inji duk jikina ba daɗi.

Haushi ne ya cika Fatima wai mutumin nan mai ya ke nufi wato ita dutse ce ko me duk gumin da take goge masa baima sani ba kenan ita zaton ta duk bacci ya ke ɗazun ashe idon sa biyu to wallahi ko mai zaiyi aure da ita ne ba fashi.

Miƙewa ta yi ta bar ɗakin zuwa toilet ɗin da ke ɗakin tsaki Faruk yaja ya dubi Ummu sannan ya ce dan Allah Ummu ki yi haƙuri da ko me yarin yar can zata miki ni ke kaɗai ce buri na tun da lafiya ta bare yanzu da zama da macen ma bai zame mun tilas ba face lalura.

Murmushi ta yi karka damu nasan me kake so ni ce basai ka damu ba wurin ƙaramin bayani.

Kusan kwanan su Fatima biyar a garin ta bi ta takurawa Ummu hani tun Faruk sai Fatiman bata nan yake  bama Ummun haƙurin har ta kai ta kawo gaban kowa yake ma Fatima tsawa  ya fahinci yarinyar bata ma fahinci meke damun sa ba ya fahimci kawai san zuciyar ta shi ya rufe mata ido so yake kawai ya samu lokaci ya su zama du biyu ya ƙara tabbatar da abinda yake zato kafin ya ɗauki mataki.

Ummu hani duk ta kuma ramewa ga jikin ta da bata jin daɗin sa daurewa kawai take damma ta samu yawan zaman Muhammad gun mami yasa ya yaye kansa rashin lafiyar Faruk kawai ita ta hanata kwanciya anma kasalar da take damun ta Allah ya yi yawa da ita bakin ta kwata kwata ba ɗadi abu mai yaji kawai ke mata ɗadi shima ba komai ba.

Kusan yanzu in Faruk ba su kaɗai bane wato daga ita sai shi ji take gun nasa tamkar kurkuku sanida zaman Fatiman a gun wannan yasa zaman ta gurin Faruk ɗin yayi ƙaranci duda ta kasa zama a inda yake masaukin su dan ko ta zauna tunanin Faruk ke cika ta dole take tawowa asibitin ta ganshi ta dawo harabar asibitin ta zauna wannan ya ƙara sabon ta da Ayatullah sosai suka saba dan wataran in ta zo kan ya ƙaraso har ji take gun shima duk ya mata rashin daɗi…

Kuna ganin Ummu zata iya haƙura ta barwa Fatima Faruk kuwa ko kuwa Fatiman ce zata janye da alamu sai ɗaya ya faru?

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 3.5 / 5. Rating: 2

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Ummu Hani 26Ummu Hani 28 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×