Skip to content
Part 11 of 30 in the Series Fasaha Haimaniyya by Haiman Raees

WAKAR BAKANDAMIYA

Da sunan sarki rabbana mai duniya

Al-kaliƙu wanda ya yo duniya

Ya yi ƙorama har da teku na maliya

Al-maliku kai ke mulkin duka duniya

Sunanka ne farkon faɗi kowace safiya

Kuma kai nake kira da yamma sakaliya.

*****

Na yi yabo gurin Annabi Muhammadu

Da ya fi kowa bauta Annabi Hamidu

Ma’aikin Allah Sahibinmu Mahmudu

Shalelen Ubangijina ya Ahmadu

Allah ka ninka salatai a wurin Ahidu

Manzonmu sha-kundum Mahmudu.

*****

Waƙa ce zan rera wa Bakandamiya

Shafin yanar gizon ga na duniya

Da ya zamo abin son mutanen Ifirikiyya

Kuma sha ziyartar mutanen Nijeriya

Yau shafin ya shiga dukkan nahiya

Fatanmu ya zamo na ɗaya duka duniya.

*****

Matattarar fasaha ce Bakandamiya

Tsangayar marubuta ce Bakandamiya

Sulkumin manazarta ce Bakandamiya

Kajar ɗalibai ce Bakandamiya

Shirinyar Facebook ce Bakandamiya

Kinin Google ce Bakandamiya.

*****

Akwai malumma a shafin Bakandamiya

Mafakar ɗalibai ce Bakandamiya

Muna sada zumunci a Bakandamiya

Muna koyon ilimi a Bakandamiya

Akwai fa nishaɗi a shafin Bakandamiya

Komai an taskace kamar Wikipedia

*****

Jama’a na yi kiranku maza ku garzaya

Shafin al’ajabin nan maza ku antaya

Ko gida ko ofis ko akan hanya

Kuna iya buɗe shafin Bakandamiya

Sauƙi ne ya zo wa Hausawan duniya

Fatan alheri na ke yi wa Bakandamiya.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 10

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fasaha Haimaniyya 10Fasaha Haimaniyya 12 >>

4 thoughts on “Fasaha Haimaniyya 11”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×