Na fara da sunan Allah mai Rahama mai jin ƙai. Tsira da aminci su ƙara tabbata ga Fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.
A komai nawa cikin kazar-kazar nake yinsa, ban cika yin abu da sanyin jiki ba ko yanƙwana, hakan yasa da yawan ƙawaye koma ƴan gidanmu, kai hattama da Gwaggona lokuta da dama su kance min mai jikin maza.
A durƙushe nake ƙofar dakalin ɗakin Inna Amarya ina gyara tsinkakken silifas ɗina, wanda yasha jiki ya gaji da duniya, dan yanzu ma da baƙar leda nake ɗaure shi, ina gama gyara shi na. . .