Skip to content
Part 62 of 62 in the Series Hawaye by Hadiza Gidan Iko

“Daddy me kayiwa Mai Kano a matsayin shi na dan ka Dan abokin ka? Ka bani amsa ta Daddy.

Wani matsiyacin Mari Muhsin yaji ya sauka Akan fuskar shi Wanda har wata walkiyar da Babu hadari ya gani. Da sauri kuwa ya dafe kumatu Yana kallon yadda Daddyn Yake cika da batsewa tsabar fushi.

“Duk zanci Kan abun ubanku Kai da Mai kanon idan ya Isa ya fada maka abinda Yake ikirarin nayi mishi don uban shi shine ka Zo ka sakani gaba tana tuhuma ta Kai ubana? Wato bakaji kashedin da nayi maka na tsame kanka daga lamarin Husna ba ko? Na bada umarnin kulleka kotu tayi belin ka shine kake neman Hawa kaina saboda ku Yan iska ne Kai da wancan shegen yaron ko? To kaje duk abinda yace maka anyi mishi anyi din sai me?

“A a Daddy Kar kace haka nifa bana son sunan ka yayi datti nafi son na wanke maka shi yayi fari a matsayi na na lauya Ina tsoron abinda kayiwa Mai kano ya Zo ganan kotu don a yanzu ne nake da abin yi in ya wuce Nan Banda abin yi

Ya Kuma tarste shi da wani Marin Yana fadin, “Don ubanka in yazo gaban kotun kana zaton Ni shari a tana da wani muhallin ajeni ne? Duk wani Alkali a garin Nan Ina da kudin siyeshi ko waye shi in ma da Haka ka fake to Zan kuwa CI ubanka in Kuma uwar ka ce ta turoka to duk zanyi maganin ku na kula kaima in ba firgita ka NASA ayi ba bazaka kiyaye Ni ba Husna Kuma da hannun ka zaka kawo min ita don haka tashi kaje Ina jiran duk abinda zaka Zo min dashi.

Haka ya Mike jiki amace ya fice har ya kusa fita ya kirashi ya dawo.

“Wannan yarinyar Safina ka dauketa ka tafi da abarka don na gaji da ciyar maka da ita ladar ta isa Haka.

“Kayi hakuri Daddy dama ai ban Rufe ka ba Akan yadda nake kallon ta so in ka gaji Daddy ka mayar da ita inda ka amso ta don gaskiya bana Jin Zan iya Rayuwa da ita don Babu ita a zuciya ta Daddy in kaso kan ajeta in Kuma ta gaji ko ka gaji ka sakar min ita tunda dama Kai ka amso min Auren ta. Bai tsaya Jin komai ba ya fice ya bar Alh Aminu da binshi da kallo. Ya Mike a fusace ya na Shirin ficewa gidan lauje don yadda yakeji din Nan in ba kassara Rayuwar muhsin yayi ba ba zai taba Zama lafiya ba.

Ya fito zai SHIGA mota kenan Amal ta shigo gidan tana fitowa da sauri ta Riske shi.

“Daddy fita zakayi ne?

“Wani Abu ne? Ya tambaye ta tamkar ya kifa Mata Mari.

“Daddy dama tambayar ka zanyi Akan Mai Kano da Yake ikirarin kayi mishi wani Abu.

“Wani abu yace Miki nayi mishi? Ta kada kanta..

“To ban San abinda Yake son cewa nayi mishi ba Amma yanzu Yana Ina? “Yana Asibiti bashi da lafiya.
Wace Asibiti Yake ? Ya tambaye ta don ita Kam baya son ta fahimci komai shiyasa Yake Bata amsa
Ta fada mishi Asibitin har da lambar dakin yace Mata zaije yaji abinda Yake nufin yayi mishi da Haka ya fice ya bar Amal da yi mishi Rakiya da ido tanajin ba gaskiya ya fada Mata ba Amma sai ta SHIGA laluben hanyar da zata gano abinda ake boye Mata

Hajiya da ta samu labarin da Alh Aminu ya fada Mata na Mai Kano da Yake kwance Asibiti har da Husna acan din sai kawai ta zari gyalenta ta nufi Asibitin inda Mai Kano ke kwance ana saka mishi drif Husna na zaune gefen gadon ta zabga tagumi damuwa goma da ashirin ga batan mahaifiyar ta ga tarnakin Mai Kano ga muhsin Wanda yaki sanar da ita abinda Yake fadar anyi musu Wanda in taji ita da kanta zata dauki mataki ita Kam Bataga matakin da zata dauka Akan muhsin ba kome kuwa zaiyi Mata.

Sai ganin hajiya sukayi tamkar wadda aka wurgo ta shigo tana yiwa Mai kano wani banzan kallo
“Uban marasa mutunci dama Nan ka fake ? To abinda baka son ne zai faru in yaso ka Fadi ka mutu
Ta cabi hannun Husna.

“Ke Kuma yau sai kin fadawa Yan garin ku Yar banza wadda bata San ciwon kanta ba.

Tun anan ta Soma jibgar ta ta Kuma jawo hannunta suka shigo napep inda Mai Kano ya fincike wayar drif din ya fito Amma ko sama ko kasa Bai gan su ba

Haka ya dawo cikin Asibitin Yana cizon lebe.

Zuciyar shi ce ke sanar dashi ya fice kawai daga Asibitin ya Isa gidan hajiya su kone ne kawai sai kuma yaga Bari yaga gudun Ruwan ta.

Suna Isa gida hajiya ta Rufe Husna da duka tamkar ba zata barta ba . “Wato kema Nan Haka dake kin iya wannan Rashin mutuncin kin kwasa kin bi Dan uwan ki don ku nuna min nice bare a cikin ku to ki sani kinyi gudun gara ne kin fada na zago don Ina me tabbatar Miki da gobe goben Nan za a daura Auren ki da Alh Aminu in yaso kin Dade bakiyi Aman zuciyar ki ba shi kuwa Mai Kano Ni dashi ne tunda ya Zama Dan iska to ko hannun fanka ya Zama zai Gane a cikin tandu ma Akwai gabas.

Husna da taji abinda hajiya ke Fadi na Wai gobe za a daura Auren su da Daddyn ta dubi haj

“Wai hajiya wahayi akayi Miki da lallai sai na Auri mutumin Nan?

Ta Yaya da Auren Dan shi akaina kuma kice Zaki Kara Dora min wata igiyar?

“Ai Auren ku da muhsin Babu shi koma akwai shi za a sake shi wallahi don not Babu Ni a layin butulci ku Kam kun Zama shegu da Baku kallon ALHERIN da akayi muku kuke butulci.

“Wallahi tallahi hajiya ba Zan taba Auren mutumin Nan ba ko Babu igiyar Auren wani akaina idan kuwa kikayi gigin Aura min shi na Rantse Miki da Allah sai nayi karar ki akan Dora min igiyar Aure Akan Aure.

“To kiyi karar tun yanzu don Babu abinda Zan fasa ki kaimu kotun koli inda ba zamu sake shakar numfashi ba.

Alh Aminu dake gaban lauje Yana fadin sai an taba mishi lafiyar muhsin don ya zauna gefe Daya tunda ya Fara zuwa da Raini.

Lauje ya gaggabe da Dariya Yana Fadin, “Yau Kuma kake son kassara lafiyar Dan naka?

“Yazo da Raini ne tunda na kulle shi Amma kotun su tayi belin shi har yazo Yana tuhuma ta Wai me nayiwa Mai Kano.

“To hada shi da Zubaina ko dimuwa ta shekara Daya ta bashi don uban shi.

“Da dai ka sauya tunani Aminu Kar ka hada shi da Zubaina.

“To wane tunani zanyi bayan yaron ya Zo min da Raini? Ko jinin shi Zubainar take bukata na yarje mata Wallahi don inajin kwanan Nan zanyiwa Zubaina gwanjon jinin mutane.

Wayar shi tayi Kara ya zarota Yana dubawa inda yayi Arba da lambar hajiya wadda ke fada mishi ga Husna ta samo a Asibiti wurin Mai Kano yazo maza su shirya yadda Auren zai dauru a gobe ya wuce da Husnar..to to to haj gani Nan Zuwa ya fada Yana hade murya, Ya Mike tsaye Yana murmushi ya dubi lauje Yana fadin

“Ai nesa tazo kusa lauje ga Husna can ta bayyana gobe ne Auren zai tabbata Ina gayyatar ka.

Bai tsaya sauraren abinda Laujen zai Fadi ba ya fice Kai tsaye ya Isa masanawa suka gama shirya komai take ya hau shiri aka tanadi komai na daurin Aure hidima irin ta manya inda Husna ke ta kallon ikon Allah Wai Auren ta da Daddy.

Washe gari ta Kama Ranar daurin Auren Wanda za ayi karfe Tara na safe Husna da taga da gaske lamarin ke Shirin tabbata ta nemi wayar da zata sanar da muhsin halin da take ciki ta Rasa ta so ficewa zuwa gidan su Salma Amma hajiya ta kasa ta tsare har ma tana saka wasu taikon gadi

Wayar hajiyar tayi nasarar daukowa ta saka lambar Yaya muhsin ta doka mishi Kira tana fada mishi abinda ke faruwa Wanda yayi daidai da kwarara muryar wani maroki da ya tabbatar da dauruwar auren su Wanda Wai Yake fadin lakadan ba ajalan ba inda muhsin ya jiyo komai ta cikin wayar.

“Yaya muhsin don Allah kazo yanzu.

“Ki bawa hajiyar waya Zan fada Mata da Auren ki take kokarin aura Miki ubana.

“Ba zata fahimce Ni ba Ni dai don Allah kazo.

Taji hajiya ta fincike wayar tana fadin, “Me Kano Kika Kira min ko? To yazo Mana Ina tsoron shine.

“Ba Mai Kano na Kira ba mijina na Kira Miki don wallahi Kara zai shigar.

<< Hawaye 61

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×