wp-content/uploads/2021/12/Kudi-Ko-Rai-by-Mustapha-Abbas.jpg

Kudi Ko Rai

Alhaji Ahmad Mukhtar na ta faman kashe kuɗi wajen ganin ya samar wa ɗansa guda ɗaya tilo wato Mashkur lafiya amma abu ya ci tura. Sai dai duk da haka ya sha alwashin ƙarar da dukiyarsa gaba ɗaya wajen nema wa ɗan nasa lafiya. Abinda bai sani ba shi ne, matarsa Zinatu na da hannu dumu-dumu bisa rashin lafiyar ɗan nasa.

wp-content/uploads/2021/12/Duniyar-El-Dorado-by-Abubakar-Abubakar.jpg

Duniyar El-Dorado

Bayan shuɗewar lokaci mai tsawo da rabuwarsu, Khadija Muhammad Lamiɗo, wadda aka fi sani da Deejah, ta kawo wa Abou Adem ziyarar bazata a gidan yarin Kirikiri Maximum Security Prison da ke Apapa, Lagos State, Nigeria. Wa ya faɗa mata an kama shi? Me ya kawo ta? Waɗannan na daga cikin tambayoyin da yake buƙatar sani a hanzarce.

wp-content/uploads/2024/03/20240311_142701_0000.jpg

Doctor Eysha

Kyakkyawar likita, wadda ake kira da Doctor Eysha ta shiga cikin ruɗani da tausayi mai girma sakamakon wani mummunan haɗari da ya faru wanda ya yi sanadiyar rasa rayuka masu yawa. Babban abin da ya fi tayar mata da hankali shi ne irin yadda wata yarinya ƙarama ke neman taimako amma mutane sun hana a taimaka mata. Kamar daga sama kuma sai ga Doctor Aryan ya bayyana a wurin, alhalin ta san da cewa an dakatar da shi daga aiki.

wp-content/uploads/2026/02/BintO-1.jpg

Binto

Zuciya ba ta da kashi, kuma ba ta shawara kafin ta zabi wanda take so. Amma me zai faru idan kaddara ta tazo miki da son mutumin da duniya ke miki kallon bai dace da ke ba? Wani lokaci, zuciyar dan Adam takan zama abin al’ajabi; tana iya guje wa abin da ke kusa da ita, wanda ke nuna mata tsantsar kauna ba tare da fuskantar wata fargaba ba kamar yadda zuciyar Binto ta kasa kallon Dan uwanta Isma’il da ke tsananin sonta.

Duk da bambancin da ke tsakanin su tamkar sama da ƙasa ne Binta ta zabi rayuwa da burin zuciyata, ta zabi komawa kauyen su Tsalha, sai dai kash tunanin ta ba ɗaya yake da rayuwar da ta gani ta zahiri a ƙauyen ba, rayuwa ce cike da kunci da fargaba, azaton Binta rayuwar kauye cike take da kwanciyar hankali, ashe kallon kitse takewa rogo duda kasancewar mijin ta ya zame mata Mijin marainiya rayuwar ta a garin tasanya ta fahinci rayuwar aure bawai kai da mijin bane kawai…

Shin soyayyar Tsalha za ta wadatar da Binto a lokacin da gata ya juye zuwa wahala? Ko kuwa za ta yi nadamar Zaɓar so kan gata da dukiya?.

wp-content/uploads/2026/04/Death-on-Motorbikes-by-Odumah-Lucky-2.jpg

Death on Motorbikes

A fourteen-year-old boy, haunted by news of bandit attacks on motorbikes in Northern Nigeria, questions his uncle about the root causes. His uncle reveals that banditry is a million-dollar business fueled by powerful financiers, politicians and businessmen who use violence to destabilize governments. The riders are mere pawns, including brainwashed children. The only solution, his uncle argues, is to imprison the financiers, though their immunity makes this nearly impossible.