Bangaren Hafsat kam tana komawa daki Mama ta kira hade da shaida mata an bar ta zuwa Ɓurma.
Cike da mamaki Mama ta ce" Lallai Hafsat na yarda ke yarinya ce, daga yi miki gatse, shi ne kika aikata, Allah Ya sa ba cewa kika yi na ce ki tambayi mijin ki ba"
Dariya ta ƙwacewa Hafsat saboda ba ta san gatse Mama ta yi mata, cikin dariya ta ce "Ni dai don Allah ku biyo ku dauke ni Mama, idan ma ba ku zo Allah tun safe zan sanya a kawo ni."
"Sai dai kam ki sanya a kawo. . .