Skip to content
Part 18 of 31 in the Series Auren Wata Bakwai by Xayyeesharthul-Humaerath

Taxi ya tare da sauri ya shige Adnan ma ya shiga, cikin tashin hankali Adeel ke magana, “ka yi sauri, Don Allah ka yi sauri mu karasa asibitin nan,in wannan yarinyar ta rasa rayuwarta nima zan rasa tawa.” Yana maganar yana kara jijjigata.

Duk da cewa Adnan ma na cikin damuwa amman ganin yadda Adeel ke bayyanar da damuwarsa ƙarara ga halin da Gaaji ke ciki ya basa mamakin da ya kasa dauke idanunsa da kallonshi.

Har suka isa asibiti Gaaji na jikin Adeel, kasa jure sakewa nurses din ita ya yi sai da ya bisu suka shige Dakin tare.

Nan take aka fara kokarin bata taimakon gaggawa, da kyar suka samu suka samu Adeel ya fita adakin.

Kusan Awa guda dukannin suna kai kawo, daga can wannan ya yi nan, sun kasa samun Nutsuwa bare su zauna.

Wani likita ne ya fito da sauri dukkanin su suka karasa gabansa.

Doctor ta farka? Tana lafiya dai ko?”

Dukkaninsu abun da suka fada kenan a tare suka kalli juna sai kuma suka kawar da kai Adnan ya ce, “Zamu iya ganinta?”

Doctor ya ce, “Calm Down Please! Cikinku wane ne mijinta?”

Kallon kallo suka tsaya yi yi sai kuma suka kara haɗa baki a tare , “Ni ne.”

Cike da Mamaki Doctor ya ce, “Mijinta na ce, anywhere dukanku ma dai ku biyoni Office yanzu.” Ya fada yana yin gaba.

Da sauri suka bi bayansa.

Suna shiga Doctor ya ce, “Have a Sit.”

Ya fada yana nuna masu wasu kujeru.

Sai da suka zauna kafin ya ce, “Patient dinku ta shiga firgicin da zai iya kawo mata matsala wanda zai iya kaiwa ga har ta rasa cikin da ke jikinta ba don Allah ya tsare ba, kuma ya kasance cikin ya fara girma ya doshi wata hudu a yanzu, kun san da hakan ai ko?”

Wani irin bugu zuciyar Adnan ta fara yana tambayar kansa shi da bai taba kusantar Gaaji ba taya za a yi ace ciki gareta har wata hudu? Kasancewar su tare ma bai zarce wata guda ba.”

Adeel ne ya yi karfin halin fadin, “Amman dai yanzu cikin bai zube ba ko? Kuma ta samu lafiya?”

Doctor ya ce, “cikin jikinta na nan ba bu abun da ya sameshi amman gaskiya a kiyaye abubuwan da zasu firgitata ko da cikin bai zube ba, in hakan ya ci gaba da faruwa zata iya samun hawan jini ko wata lalurar daban, mussaman da ta kasance karamar yarinya mai karancin shekaru, tana matuƙar buƙatar kulawa da tarairaya And yanzu zaku iya zuwa ku ganta in an gama kawo magungunan da zatayi amfani da shi zaku iya tafiya ma.”

Adnan ne ya fara fita da sauri yana shiga ya ganta zaune, “Waya miki ciki? Kar dai dalilin da yasa kika ƙi bari na kusanceki kenan? Ki fadamun gaskiya cikin wanene a jikinki?”

Nawane, ni ne na mata, cikin jikinta mallakina ne.” Adeel ya fada yana shiga cikin dakin.

Adnan ya ce, “What? Kasan me kake fada kuwa Prince.”

“Eheen na sani sarai cikin jikinta mallakina ne kamar yadda na fada a farko ni na yi shi, na kasance da ita ba tare da sanin kowa ba kuma na umarceta da kada ta kuskura ta sanar da kowa.”

Adnan ya kalli Gaaji, “Da gaske abu ya shiga tsakaninku baki fada ba?”

Gaaji kanta na kasa ta ce, “Eh cewa ya yi inna fada zai kashe mun Baffana.”

Wani irin sarawa kan Adnan ya fara ,cikin lokaci kankani ya fara jin wani irin azazzaben ciwon kai, dafe kansa ya yi, kusan Second Uku sannan ya dago ya kalli Adeel ya ce, “Don Allah ka yi mun gafara! Ban yi komai da niya ba, kuma da na san da cewa Akwai abun da ya taba shiga tsakaninku da Zainab ba zan taba gigin aurenta cikin karamin lokaci ba, duk da cewa batun auren ma da niyar tarayyah na aureta araina ina jin cewa dole zaka sota kuma zaka ji bukatarta duk rintsi kamar yadda Uwar Goyonka ta sanar mun cewa Gaaji ce mafi cancantar kasancewa Fulani a masarautar Benoni gudun afkuwar wata matsala ko ta subucema yasa nayi tunanin nuna ma ina sonta da kuma aurenta shine kawai mafita, And Alhmdu Lillah ban taba kusantarta ba matarka mallakinka ce har yanzu kuma ni na sauwake mata saki uku, Ni Amininka ne duk rintsi kuma ina tare da duk wani abu na alkairi dake tattare da kai kamar yadda nake gujewa dukkanin sharri, kuma mahaifinta yasan komai bana da Matsala da shi In Sha Allah.

Gaaji tamkar kanwa take a gareni kuma ina jinta har cikin raina sannan ina matukar jin tausayinta wannan shine silar shakuwarmu, yanzu kawai zamu koma Nigeria a samu Uwar Soro mu tattauna tukunna amman naji matukar dadi da har yanzu ka fahimci cewa tana da mahimmanci kuma kana bukatar ta cikin rayuwarka.”

Adeel dai kam bai ce komai ba kawai kallon Gaaji yake.

Ita kuwa zumbur ta miki Adnan na gama magana ta je ta rikesa tana fadin, “Yaayah ni bazan bisa ba, don Allah kar ka ce in bisa ni bana son komawa Masarauta dukana zai ci gaba da yi bana sonsa nikam karka rabu dani ka ji.”

Adnan ya ce, “Kin ga gun Baabarki zamu je ai ko ba kya kewarta?”

Gaaji ta girgiza kai alamar ta na yi.

Adnan ya ce, “Yawwa to zamu je ne saboda baki da lafiya .”

Amman cewa kayi ka sakeni ni matarsa ce fa.” Ta karasa maganar hawaye na zuba daga idanunta.

Adnan ya ce, “Eheen ki daina kuka zamuyi fada fa, ni ba Yayanki bane? Kuma kin min alƙawarin komai nace zakina yi so kar in kara jin wani batu.”

Adeel dai kam tamkar gunki binsu da kallo yake kawai.

Suna kammala karban magunguna suka kara hawa private jet domin komawa Nigeria.

Gaaji na kame da Adnan ko kallon Adeel bata son yi suna hada ido take saurin kawar da kai.

Nigeria.

Suna Isa ta kofar Part din Adeel da suka saba shiga suka bi, kai tsaye suka shiga, suna shiga Adnan yasa Shamaki ya kira Liman bayan liman yazo Adnan ya fara jawabin komai dukkanin abun da ya faru tafiyar su da dawowarsu da kuma dalilin da yasa ya auri Gaaji.

Liman ne ya yi gyara murya kafin ya ce, “To batu na gaskiya tun a karon farko anyi kuskure ko da a ce ansan cewa ba abun da ya shiga tsakanin miji da mata muddin an daura aure a masallaci to ya wajaba a bari ta yi iddar wata uku domin tabbatar da wankuwar komai dake jikinta, to amman kaga bayyanar wannan cikin kuma ka ce babu abun da ya shiga tsakanin ku to AlhmduLillah zaka saketa saki Uku, sannan sai ta haihu tukunna in zata koma ga mijinta sai a kara daura wani auren.”

A zuciyarsa Adnan yake Hamdala da kwadayin da zuciyarsa ta kwadaita masa na son kasancewa da Gaaji bai tabbata ba domin da hakan ya faru da ya yi babban nadama garin neman kiba azo asamu rama.

Liman na gama jawabinsa ya tafi Uwar Soro ta ce, “tun farko abun da nake gudunmawa Yareema kenan amman fir yaƙi fahimta yanzu Gaaji zata zauna anan har sai ta haihu amman kasani da cewa baza a taɓa tirsasa mata kasancewa da kai ba, koda kuwa Adnan ta zaɓa bayan haihuwarta babu shakka shi ne zai zam mijinta.

Fadan hakan da Uwar Soro tayi ya matukar batawa Prince Adeel rai wanda hakan sai da ya bayyana a fuskarsa duk da cewa baiyi magana ba, tashi ya yi yana fadin, “What Ever she’s My Wife.” Yana fada ya fice.

Uwar Soro ta kalli Gaaji da idanunta sunyi kananu tsabar barcin da take ji, riketa tayi tana, “Tashi muje dakinki ki kwanta.”

Sai da taje ta kwantar da ita sannan ta dawo ta sami Baffa da Adnan zaune a parlourn.

Adnan ya ce, “Ranki Ya Dade amman ina tunanin kamar da baki furta kalmar cewa in bata son shi ba wanda take so za aurawa, na ga tsantsar soyayyar Gaaji a idanun Adeel wacce ban taba zato ko tunanin zai iya yiwa wata ‘Ya mace ba.”

Murmushi ta yi kafin ta ce, “ina sane, so nake ya koyi bayyanar da soyayyar shi gareta domin in ba haka ba zaman masarautar nan sai yafi karfin Gaaji, dole ne ya fara nuna mata soyayyar zahiri, yasa ta saba da shi kuma su zamto bangon jingina ga junansu yadda kowa a cikinsu zai iya kare kowanne a kowani hali kuma a ko wani lokaci yadda zai iya bayyanar da ita matsayin mata cikin Masarautar nan ba tare da shakka da izza ko jin cewa ita kaskantarciya ce ba, kuma ka ga cikin nan ya kamata ace na fahimta tun tana nan kafin ka dauketa ikon Allah kuma sai yasa cikin ya kwanta bai bayyana ba sai yanzu, lokacin da taketa kananun ciwon nan duk ba a gane ba saboda ba wanda ya kawo hakan arai, Allah mai iko, tabbacin cewa dai duk rintsi ita ce mallakin nasa kenan.” 

Adnan ya ce, “Gaskiya kam da wannan kuma, Allah yasa mu dace yanzu ni da Baffa zamu koma can Gida NASARAWA zan rubuta takkaddar sakin in zan dawo inzo da ita.”

Daga nan suka yi sallama suka tafi.

*****

Safina ta gama duburbucewa ta rasa gane shin wacce irin duniya aka kawo ta wacce tafi tata hatsari, duk wani Bala’i, tashin, rashin imani da makirci ya tattara cikin wannan masarauta kowa fa kudirinsa kuma da shirinsa mai muni.

Mussaman yanzu da aka zuwa mata da wata barazanar cewa duk rintsi kada ta kuskura ta karyata cewa cikin da ke jikinta bana Yareema bane, wanda sabanin hakan za ayi mata sharrin da sai Mai Martaba yasa an Ratayeta.

Gagara karasa karanta takardar tayi cikin kuka hannu na rawa ta dauki waya tana magana, “Ni kam na shiga uku na siyawa kaina tikitin mutuwa da kudine ashe fal haka Masarautar nan take zagaye da azzalumai kowa da kudirinsa? Kasheni zasuyi wallahi kasheni zasuyi nikam ban san mafita ba, kazo ka fidda ni cikin Masarautar nan,na hakura da komai wallahi na hakura koda zan mutu a matsaya ciya yafi mun ci gaba da rayuwa cikin Masarautar nan ko da kuwa na second guda ne.” Tana magana tana shiɗewa.

“Ki yi hakuri, ki kwantar da hankalinki ni nasan me zanyi kan hakan duk da cewa banyi tunanin faruwar abu makamancin hakan ba amman kuma wannan dinma zan dakile, ki kwantar da hankalinki Don Allah, za asa tsaro a inda kike babu mai kara shiga ba tare da kwakkwaran dalili ba.” Ya fada yana katse kiran.

Ita kam ta gagara samun nutsuwa tunda kafafunta suka taka wannan masauratar take cikin Bala’i da masifun da bata taba tsammanin kasancewar su ba a cikin rayuwarta.

Barci take ji sosai idanunta har suna rurrufewa, kamar a mafarki taji an shaƙe mata wuya, bude idon da zata yi, bata ganin komai sai duhu ga dukkan alamu an kashe wutar bangaren duka.

Kokawa suka fara yi cikin duhun tana kokarin kwatar kanta, abun ya gagara da kyar ta samu damar sakin wata irin ƙara, cikin sauri masu gadin kofar Part din suka shiga tare da kunna wutar.

Ga alamun shaƙa a wuyanta amman bata ga kowa ba, 

Ranki Ya Dade lafiya dai ko?

Wata irin ajiyar zuciya tayi kawai ba tare da ta iya cewa uffan ba, ba ma zata iya maganar ba koda taso yi din.

Haka ta zauna idanu a bude har safiya tana waige-waige ciki fal tsoro da fargaba.

*****

Tunani mai dauke da Farin ciki Adeel yake har cikin ransa amman kuma ta wani bangaren ya kasa samun sukuni wanda har ya kai ga ya gagara rintsawa, tuna cewa Gaaji tsoronsa take ji bata ma son ganinsa gashi Uwar Soro ta ce dole zabinta za a bi, sam bai san ta inda zai bullowa hakan ba, bai ma san taya zaiyi yasa Gaaji ta daina tsoron shi har ta so shi ba.

Gari na wayewa yana tsaye a window sai da ya tabbatar Uwar Soro ta tafi Fada sannan ya shiga Part dinta.

Gaaji na kwance tana barci ga dukkan alamu barcin da take ya yi mata dadi sosai wanda azahiri murmushi ke bayyana a fuskarta, a hankali ya karasa ya zauna daf da ita, sannan ya daga hannunsa yana shafa mata fuska.

Ya kalli karamin cikinta da ya faro tasowa wanda in ba wai an fada ba kam babu wanda zaiyi tunanin cewa akwai ajiya cikin wannan dan karamin cikin.

Dayan hannunsa yasa ya daga mata riga yana shafa cikin a hankali.

Kamar a mafarki taji ana taɓata, a firgice ta farka tana janye jikinta suna hada ido da shi da kankame jikinta da hannu tana.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Auren Wata Bakwai 18Auren Wata Bakwai 20 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×