Duka yakumbo tana kuka take rattaba wannan bayanin kafin ta juya kan Nadiya ta cacumo ta tana fadin
"Munafuka dama kinyi nufin kunyata ni ne a gaban yar uwa ta? A kawo min ke lami lafiya sai kawai aji kina shirin sauke dan dakan kuka a gaba na me kenan? to gara kawai ta kashe ki na kashe banza wofi in yaso nace kin mutu da dai iyayen ki suji abinda yake faruwa wallahi banda idon duban su na basu ba asi . .
Irin shakar da yakumbo halima tayiwa Nadiya irin wacce ke neman makasa ce don ga alama ta hau. . .