Skip to content
Part 10 of 17 in the Series Bakar Tafiya by Amina Abubakar Yandoma

A guje sukayo wurin Basma domin ceton rayuwarta.

Sunyi iya ƙoƙarinsu wurin fiddo Basma a cikin ruwan amma abun yaci tura, saboda ruƙon da Mandiya tayi mata bana wasa ne.

Ƙarfi suka haɗa suka fizgota daga cikin ruwan.

Tare da Mandiya da ta yi mata mugun ruƙo suka fiddota.

Ganin yadda Mandiya ta koma yasa sauran abokan tafiyar ja da baya in banda Jafar da yake naiman hanyar da zai taimaki Basma.

Tamkar yunwataccen zaki haka Mandiya tayi wurgi da Basma tayo kan Jafar gadan-gadan.

Da nufin cizonshi ta iso takamashi da kokawa sukayi ƙasa.

“A’uzubillah! Subhanallah!.”
Jafar ya furta ganin mace wadda ba muharramarshi ba ta ta6i jikinshi suna kokawa a ƙasa.

Tunyana kare kanshi daga muggan hare_hare da take kawo mashi harya fara mai da mata martani.

Su Jamcy ba kata6us tsaye suke sun haɗe wuri ɗaya ita da Tk suna surutan da ko su basu san mi suke faɗaba.

Ƙoƙarin yakiceta Jafar yayi ya wurgar da ita can gefe.

Abinda ya lura da waɗannan Horror ɗin basu taba mutuwa sai dai suyi doguwar suma inkayi nasarar luma masu wani makami ta bayansu.

Dube_dube ya fara naiman inda suka yada itatuwanda suke kamun kifi da su.

Can nesa da inda suke ya hango su.

Da gudu ya nufi inda suke, yana gaf da ida isa yaji an warto ƙafarshi ba shiri yayi ƙasa.

Ganin Mandiya na ƙoƙarin kawo mashi hari ta kowace hanya ya sanyashi kai mata harbi da ƙafafunshi cikin zuciyarshi yana karanto duk wata addu’a data zo mashi, yana ƙara ƙaimi wurin isa ga iccen da yake ƙoƙarin kaiwa.

Yayi nasarar ɗauko icce inda yayi nasarar luma matashi a tsakiyar baya, wata firgitacciyar ƙara ta kwala ta faɗa cikin ruwan ta 6ace 6at.

Wurin Basma dake kwance magashiyan dafe da wuyanta suka yo aguje.

Jamcy ta yagi rigarta ta ɗaure mata raunin Jafar ya tofa mata addu’o’in suna mata sannu.

Basu ɗauki lokaci ba Jamcy ta kamo Basma suka bar wurin saboda ganin abinda ya faru.

Tafiya suke batare da sanin inda suke nufa ba.

Ga wata ƙishirwa da ta addabesu kamar su zube.

Wata inuwa suka samu domin su huta saboda zafin ranar da ake zubawa.

Tunaninsu ɗaya shine imna zasu sami abinda zasu ci dazai Gusar masu ƙishin da suke ji.

Ƙarar faɗuwar wani Abu sukaji a bayansu, Suna juyawa sukaga bishiyar kwakwa ce gasunan sun nuna manya sun Zubo ƙasa birjik.

Kallon_kallo suke an rasa wazai je ya kwaso masu suci.

Jafar ne yayi ƙarfin hali yayi addu’a ya duƙa ya fara tsinta yana tarawa.

Sai da ya tsinto masu mai yawa ya fara fasawa sukayi Basmala suna shanye ruwan ciki.

Sai da suka gama shanye ruwan sannan suka fara cin kwakwar.

Sunci sun ƙoshi lokaci ɗaya sukaji wani irin bacci na ɗibarsu, kwanciya sukayi domin su huta Jafar yayi Basmala tare da kwanciya.

Tunkafin baccin ya ida ɗaukarsu sukaji iska mai ƙarfi tana iso inda suke, kafin su ankara wata irin guguwa mai matuƙar ƙarfi ta kwashesu tayi sama dasu.

Abinda suka gani shi yakusa sanadiyyar datsewar numfashinsu.

Tsintar kansu sukayi a saman wani ƙaton tsauni wanda ƙasanshi ya kasance wasu irin itatuwane masu tsawo naban mamaki, itatuwan sune zaka kama ganyayensu masu tsananin faɗi da ƙauri da suka rufe saman tsaunin In kana da sa’a ka isa ƙasan tsanin da rayuwarka.

Gashi duk iyakar hangensu sun duba amma basuga Wata hanyaba saidai wannan.

Tafiya sukaji tamkar irinta ƙwaro in ya doso inda kake.

Amatuƙar firgice suka juyo danganema idanunsu mike faru.

Wasu irin ƙwarine masu kama da gizogizo.

Idanunsu jajur tamkar garwashin wuta, ga jikinsu duk wani irin gashi abun kwanin ban bantsoro.

Wani yawu suka haɗe atare ƙuutt!, Salma da Rabson tuni suka rungume juna suna salallami kamar basu bane suka gama gwabza faɗa ɗazu.

Ƙwari gudu suke suna ƙoƙarin isowa wurinsu Biba, ganin haka ya sanya su Biba ja da baya har suka iso ƙarshen ramin, ganin basuda wata mafita lokaci ɗaya tamkar sun haɗa baku suduka suka daka tsalle sukayi ƙasan ramin.

Ganin haka ƙwarin suka mara masu baya.

Saman ganye ɗaya suka faɗa su dukan su suna rarraba ido da tsananin mamakin wannan wane irin ganyen bishiyane?.

Basu ankara ba sukaji dirowar ƙwarin saman ganyen.

Suna son miƙewa amma tsoron in suka tashi tsaye tabbas sil6in ganyen zai kayar dasu.

Rabson da dai yaga bashakka in suka tsaya mutuwa zasuyi, wuf! Yayi ya miƙe “Ku miƙe muyi ta kanmu, bashakka in muka tsaya ƙwarin can zasu zuƙe jinin jikinmu abanza.”

“Kai kam bakada tunani arayuwar, yanzu in bayaga kanada tunani irin na bunsurunka ta ina zamu gudu bakaga ƙasa rami bane?.”
Salma ta ida maganar tana aikoma Rabson da kallon raini.

“Hhh, sai shegen surutu kamar aku, ja’ira mai zubin muciya baki kamar na agwagwa, nan gabafa nine mijinki kuma Oga awurinki kisan irin maganar da zaki riƙa furta mani.”
Ya ƙarashe maganar yana dariyar mugunta dan yasan ya gama tunzura Salma.

Ashar ta mulmula ta dura mashi tana Allah ya tsareta da auren faƙiri talaka irinshi.

Biba da taga faɗan nasu bamai ƙarewa bane tsalle ta daka tayi ƙasan ramin.

Bayanta suka bi suma, saman ganyayyaki suka riƙa faɗawa kafinsu ida isa saman wani ganyen sul6i ya kwashesu sunyi ƙasa, haka aka riƙa tilli_tilli dasu.

Masu ihu nayi masu addu’a nayi.

Rabson daya bugu kanshi ya fara juyawa idanunshi suka fara hango mashi mutane suna komawa bibbiyu.
“Ƙalu innalillahi, la’ilaha’illallahu, shikenan namakance nalalace wayyoh busurulle wayyoh kaka uwata,Salma masoyiyi bibbiyu nike ganinku, lokacina yayi wayyon nazama makaho, yau Rabi’u nike ba Rabson ba namakance nadaina gani shikenan nayi Expired Salma ko auren mukayi saidai ki riƙa yimani jagora, inkuma namutu inkin koma gida kice ɗan busurulle Nabarma kakata ta yanka ta cinama ta ƙoshi, wayyoh nazama makaho.”

Duk da har yanzu gwarasu ake sunayin ƙasa masifar dake cin Salma saida ta tanka.
“Allah ya ida makantar da kai, bakinka yasari ɗanyen kashi, mai muguwar fata,kaga ɗan bunsunru can inka mutu.”
Bugata da akayi ta bugu da reshen wani icce ya sanyata yin shiru ta sume a take.

Sai da aka kawosu ƙarshen ramin suka faɗo tim! Batare da sanin inda kansu yake ba.

Wata guguwa mai masifar ƙarfi ta kwashesu tayi sararin samaniya dasu.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Bakar Tafiya 9Bakar Tafiya 11 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×