Skip to content
Part 7 of 7 in the Series Barrister by Maryam Ibrahim

Driving yakeyi cikin nutsuwa da kwarewa har suka isa wani makeken shoprite irin na masu kudi masu ji da kansu talaka baya zuwa irin wanna hurin!

Parking yayi a gurin da kowa yake ijiye motonshi idan yazo gurin 6uďewa murfin moton yayi yafita. Yana jiranta yakai 3 minutes bega fitowan ta ba 6uďe inda take yayi yaga tazaune hankalinta a kwance wani irin tsawa yadaka mata wanda taji shi har cikin kwanyanta

“Ni direban kine da kike jira na 6uďe miki kofa kifita? Ko ni dan ankine? Duka wanna tambaya a lokaci guda yake mata b’angaren Zahra kuwa duk ba haka bane bata iya buďewa bane shiyasa kuma ta ďauka jiransa zatayi hiyasa;

“Tambayanki nake kinyi shiru.”

“Aa yaya ba haka bane kawai day…… “
yakatseta.

“Kawai dai kin raina nine to kisani kowani minti ďaya da nayi saikin biyani shi sbd ni ba yaro bane da zaki rainamin wayo dan….
saikuma ya yafara tafiya da sauri ta fita ta fara binshi a baya tafiya sukeyi har suka isa wani tsaran ran guri shiga suka wani karamin guri sai taga abin ya rufe su shiru tayi amma cikin zuciyanta Allah-Allah take su fita kawai sai taga kamar walkiya abin ya buďe fita sukayi wani haďaďen gurin kaya tagani babu abin da babu na sawa.

“Ki za6a duk abinda kike buk’ata.”

Cikin wani sanyayen murya yayi maganan wanda idan ba kana kusa dashi ba bazaka ji me yake cewaba!

D’aga ido yayi yakale ta yaga ko matsawa batayi daga inda take ba, kusan 5 minutes.

“Bakiji me nace bane hmm idan munkoma gida zakiyi bayani.”

“Kayi hkri ban ďauka dani kakeyi ba.”

“Ok nazama mahaukaci kenan dazan na surutu ni Kaďe.”

“Aa ba haka bane kayi hkri.”

“Ok” to yayane inajinki.”

Shiru tayi bata ce komai ba
wasu yanmata ne guda biyu suka iso inda yake,

“Hey”

Wata yarinyan ce matashiya amma iyayenta masu gudi ne tun daga nesa ta hangesu dama tun ba yau takeson wanna haďaďen gayen sbd idan ba ta manta ba ta ta6a ganin hotonshi a wayan Nadiya ta tambayeta tace mata yayanta ne!

Shiru taga yayi be ce mata komai ba sai tayi sallama murya can kasan mak’oshi ya amsa Zahra ce ta amsa mata da murmushi
ita amra tadauka Zahra k’anwan yazid ne
Amra “zamu iya ďaukan hoto da yayanki.”

Daga musu kai tayi batare da ta ankara ba
hoto Amrah tayi sosai da Yazid kawanta leesha ma tayi daga baya sukayi da Zahra saikuma tayi musu su huďu duka Kafin suka bari kama hanun Zahra Amrah tayi suka je gurin sayayya kaman tasan abinda suka zo saya.

Kaya taza 6amata kala-kala babu abinda basu saba shoe, gown, material,abaya jallabiya na mata sarka, etc
(tsayawa faďa 6ata lokacine) komai harda kayan ciye -ciye kar6an ATM nasa tayi taje suka cire kaya ne yagani sosai a hanunsu a cikin shop leda aka sa musu har leda biyar
mamakine yaka masa karan message yaji yaduba yaga debit alert 700k.


“Zamu iya karasa can nayi mana order snaks sai mu huce “cewan Amra da ido kawai yake binsu.

Shi mutun ne me wani irin hali idan ka zauna da Yazid sai yayi ainun kagane halinshi yanada sauk’i wani lokaci bashi da shi isa sukayi gurin basu fi 20 minute ba suka kammala suka fita daga cikin shoprite ďin suna tafiya suna hira tun Zahra Tana ďari _ďari harta sake jiki suna hira sama _sama har suka isa daidai inda sukayi parking moto a wajen ne suka sallame juna Amra taso Zahra tabata number ta saita ce mata bata da waya itadai bata yar daba ta ďauka bataso ta bata ne sai ta ciro wani white pepper ta rubuta mata number ta da address nata.

k’ar6a tayi kowa yashiga car nashi cike da farin ciki banda Yazid saboda shi haushi ma suka bashi daga ganin juna basu san suba amma tana abu kamar sun ta6a sanin juna lallai zata yi bayani……

Jan moto yayi da wani irin gudu sai gida.

*****

Germany

Likita me suna ishaq musulmine Umman Fatima ce ke zaune a ďaya daga cikin kujera da ke gefensa gaisawa sukayi kafin daga bisani yabata wani file tayi sign kar6a tayi tasa hanu

“Kinsan wanna idan za ayi a cikin biyu dole ďaya zaifaru na farko idan anyi a cikin sa a tafito da rai na biyu kuma za, a iya yi tarasa ranta wanna shine.”

Bugawa kirjinta yayi amma sai bata nuna “Allah yabata lfy yasa ayi a sa’a”

Da Ameen ya amsa mata.

2:30 na rana aka shiga da ita ďakin da za ayi mata aiki da adu a Umman Fatima ta bita har tana kuka. komawa tayi ta zauna tana tama yar uwanta adua

Nigeria

Yazid ne da Zahra ya rike hannunta suna takawa zuwa masauk’insu inda za a gudanar da walima tunda suka fara takawa ake musu tafi sunyi matukar yin kyau bakaďanba. Tsaya faďa inda couple ďin nan sukayi kyau 6ata lokacine kudai kawai ku kiyasta

Zama sukayi a wani kayatacen kujera inda aka tanada sbd su.

An cika sosai a gurin kawaye sun zauna a kusa da angoye ďaya gefen iyayene ciki harda mommyn Nadiya da kawanta Larai sai umma Zainab su Nadiya amra meenat duk anzo gulma da sauran jama a jawabi aka fara kafin daga bisani aka fara mgn akan mahimmancin aure da yadda yake sosai akayi da jawabi akai Zahra kam shiru tayi tana tunanin dama haka auren yake lalai Allah ya bamu zaman lfy ( na amsa da Ameen).

S ai karfe 6:00 aka tashi a gurin walima inda. Masu komawa gida nayi masu jiran kai amarya sunayi da su Nadiya ya”n bin kwakwaf

9:00 daidai moton angwaye suka don ďaukan amarya zuwa katafaren Gidan su ba a tsaya 6ata lokaciba suka ďauke sai gidan da isan su basuwani jima ba suka huce gidajen su aka bar Zahra da yazid a gida tashi yayi daga inda suka barshi ya huce ďakinsa ya fađa toilet ya sakar ma kansa ruwa yakai 40 minutes kafin ya fito ya shirya cikin wani sleeping dress mai taushi ya feshe jikin sa da turaruka sunkai kala goma sha biyu.

Tashi yayi yaďauka ďaya daga cikin ledan da suka shigo dashi direct ďakin Zahra ya shige inda ya same ta har ta kwanta da kayan jikinta miqa mata ledan.

“kitashi ki cire wanna kaya kisauya zuwa wani sbd wanna zai dameki “yana gama fađa ya fice be jira me zata ceba!

Ita kuwa Zahra da ido ta bisa

Bayan Sati Biyu

Wata matashiyar mata ce nagani tana saukowa daga stairs na jikin sama bayan ta kuma wata ce amma tafita yarinta basu wani ďaukan lokaci suka sauko kare mata kallo nayi tundaga sama har qasa wow mahaifiyar Zahra ce kana ganinta kasan tasamu lfy ta qara haske da kyau wani kayattacen moto ne ya tsaya a daidai in da suka karasa shiga zukayi.

London

Fareesat ce durkushe a gaban mahaifiyar ta tana kuka ita kuma rarrashinta.

“Kiyi hkri in sha Allah zan yi kokari naga na kwata miki yancinki na ya Mace duk da nasan cewa yafi mu qarfi amma befi karfin Allah ba a gobe zamu je Nigeria sbd akwai wani kotu da naji ake magana akai kotun adalci da gsky da karfan yan cin ďan Adam basa karfan kuďi dan cin hanci “

“Dan Allah Mom muje sbd inaso kamar yadda ya 6atamin rayuwa shima a 6ata masa nasa “

“In sha Allah yan nan “

Nigeria

Tun ranar da aka kawo Zahra cikin Gidan nan bata sake sa Yazid a idon ta6a ita kam ma haka yafi mata rayuwar ta takeyi ita kaďai sai ďe in su Neehal sun zo shine zasu ta hira

To yau ma kamar kullum ta tashi daga barci karfe 7:30 ta huce toilet tayi brush ta fito hijab nata tasa har qasa ta fito wani ďaki ne wanda yake nesa da nata tashige dube dube tafara yi bata ga kowa ya takusa kai har bed room gyara wa tafara tana sake sauya ma wani abin guri cikin minti kalilan ta kammala ta shige privancy! shima gyara wa tayi taga wasu riguna da boxer ta kwashe ta wanke ya bushe ta ninke dawowa tayi falo ta cire hijab nata ta ďauko kasko tafara turare ďakin.

Komawa tayi bedroom tasake turareshi tana cikin taji motsin mutum abayanta juya tayi suka haďa ido bata san lokacin da ta sake kaskon a kasa tana shirin ficewa da gudu taji a kamo hannunta

“Da.. n. Allah. ka..yi. h. k.. ri”tana mgn tana in ina kamar mara gsky
“hkri me zaki ban sbd makirci harda shiga min ďaki sbd kinga na kyaleki na barki shine kikeso na haďa jiki dake harda sa wanna kayan da ake ganin jikin mutun ko kinzo kina turaren min ďaki da turaren yan bori to kisani babu abin da zakiyi don ki mallake ni kuma kisani bazan ta6a sonkiba.”

“Juyawa tayi da idanunta dasuka kaďa sukayi jajir na 6acin rai tafara masa mgn kamar hk…

“Kai har kana ganin ka kai na mijin da zan masa haka idan kana tunanin ka kai to ka farka baka da abin da zaisa nasoka fanko kawai wanda ko mace aka haďa ka dashi baza ka iya mata komai ba ďaki ne nashigo gyarawa shine zakamin wanna cin mutunci to wallahi kasa a ranka baza ka sake ganina a wanna qazamin part ba.” to fa mishi yahu tayi tajuya.

*****

Cikin mamaki take binsu da kallo “ayya kuyi hkri me gidan yanzu yafita amma muje daga falo kafin yadawo sai na kawo muku wani abin motsa baki.” cewan zahra “Kai amma yarinyan nan ke karamar yar rainin hankali ne mu zaki duba kece mu zauna daga falo zaki kawo mana abin motsa baki mujirashi to bari kiji ba gurin shi muka zoba gurinki muka zo.” Cewan Nadiya

“Ni “

Meenat ne ta amsa,

“Ok kina mamakine to baki ma yi mamaki ba gurin mukazo na farko munason sanin da me kika fimu da har yaji yanasonki ya amsa auren ki na biyu kuďi kika fimu ko asali na uku iya sarrafa miji ko me muna jinki karamar mara kunya “

Amrah ce itama ta amsa

“Ai wanna dagani kinsan irin abin da sukayi har suka mallake yanzu zamu koya miki hankali kuma Kiyi gagawa idan yadawo kice ya sake ki domin idan bakiyi hakan ba abun bazai miki daďiba.”

“Ok kungama ko baku gama ba idan baku gama ba kuyi saurin gamawa ni nasan ni ba kowa bace kamar yadda kuka faďa amma nasan darajar kaina kuma babu yarinyan da zato har cikin gidan mijina ta nima cimin mutunci ke ba ma hkba ko a hanya ai ku kananan….. Bata karasaba taji saukan mari tass -tass Nadiya ce tayi mata.

“Ke kikama kanki yan mata muyi abinda yakawo mu… kafin ta karasa ne itama taji saukan marika har biyu Zahra ta mata gaba ďayan su suka yo kanta duka suke mata ta ko ina Nadiya ce ta yaga rigan ta zata ciro mata breast ta da duka sosai yadda zasu mata tsami ita kuma Meenat gashin kanta take ja Amrah kuwa taka ta takeyi sosai da bata mari iya laushi Zahra tayi abin tausayi haka suka gama mata suka fice suka bar ta da tsamin jiki ko tashi takasa yi da kyar ta mike zuwa privacy na shi.

*****
Mom ne tare da Umman Zahra suke zaune suna hira sama sama Neehal da Neehila suna zaune su ma kusa mom nasu ummah ne tace,

“Ai yakamata wa inan yan matan su ma su taramu musha biki amma kullum kuna makale da Mom gsky aduba mgn na.”

“Kibari kawai idan suka ishani sai nayi sadaka dasu kinga hankali kwance.”

Gaba ďayan su suka sa dariya “oh kaji ja’iran yara ni kukema dariya zakusha mamaki!

Haka sukayi ta hira gwanin sha awa har yan ma yayi driver yadawo dasu gida cikin kewan juna suka rabu.

Ummah Fatima wato kanwar umman Zahra shigowa tayi part ďin ta takawo mata lafiyayun abinci sai Kamshi sukeyi sbd tace ummah Zahra ta huta ita zata rinka yi tana kawo mata kafin takara jin sauki sosai Umman zainab ma a 6angarenta hakane itama tace ta huta haka dai sukeyi da ita kowa idan yayi zai kawo mata! suzauna suyi fira zainab ma tashiryu ta daina duk abinda takeyi ta karya sim nata tayi sabo yanzu kullum adu a takeyi Allah ya bata miji tayi aure ko talakane ta auresa

*****
Aryaan kuwa tun ran da yama fareesat wanna aika aika be sake ganin ta ba ga wani sha awa da yakeji sosai amma yakasa nima wanda zata rage masa zafi yauma hađa kayan sa yayi yaja trolley nasa sbd yau yakeso yadawo Nigeria ya shiga rayuwar Nadiya ya tarwatsa tunda ta ďaga hanu ta maresa karfe huđu daidai jirginsa yatashi sai Nigeria

***
Mommyn Nadiya ce tunda tadawo gida takasa zaune ta kasa tsaye sai kaiwa da komawa takeyi sbd maganganun da boka ya gaya mata ita kuma tanason farin cikin yar ta akanta ba abin da bazata yi ko meye sbd ita kađai Allah ya basu đaukan wayan ta tayi -tayi darling number kawar ta Larai ringing biyu ta ďauka cikin rawar murya mommyn Nadiya ke sanar mata da duk abinda ke faruwa ajiyar zuciya kafin nan tafara magana

“Hmm turai duk abinda Allah ya kadara ma bawa a rayuwa zaisamu kisani ko ta wani hali ne saiya samu Allah y gaddara BARRISTER bazai aure ta ba dan haka muyi hakuri muzuba ma sarautar Allah ido ya mika wuya garesa Dan nikam ma a halin yanzu na tuba na daina saura ke yanzu haka ma ina madinah dama ni nashigo rayuwar kine dan na tarwatsa kuma gashi nayi nasara dan hka kiyi hkri ki yafemin dan yanzu na tuba dama sharin shaiďan ne.”

Wani irin rawa ne jikin turai keyi zufa na karyo mata magana takasa yi sake wayan tayi yafađi kasa war was itama ta bi wayan

“Hello hello taji wayan yakatse takira taji wayan akashe cikin tashi hankali itama ta tazauna

“Allah na tuba ka yafemin duk inda zanyi cikin satin nan zan koma Nigeria ban shirya mutuwa da hakin wani akaina ba zan je gareta duk abinda da zaifaru yafaru kawai.”

Itakaďai take ta surutu kafin daga bisani tayi shiru!

******
Zahra ta daďe a kafin ta fito tana tsane jikinta daga ita sai towel!

Yazid kuwa tunda yafita ya huce wani Islamic medicine ya siyo maganin kara karfin sha awa sbd yayi alkawari sai yarinyan nan ta gane kuranta tunda har ta iya ce mishi fanko shikuma sai ya nuna mata shi na mijine! sai wajen karfe takwas yadawo lokacin ya gama komai haka ya shiga cikin ďakin bakinsa đauke da sallama, lokacin Zahra ta gama gyara komai kamar ba abinda ya sameta ta zaune a kasan tyes taji sallamansa ya shigo ta amsa masa “sannu da dawo wa ” be ce mata komai ba can tsinkayo muryan sa yafito dg privacy alamun alwala taga yayi

“Kishiga kije kiyi alwala kizo muyi sallah.”

“Am am nariga nayi sallah.”

“Nace kije kizo muyi nafila banason jin komai”

“Ok “
Tashige bata fi 5 minutes ba tafito taďauka hijab dama ya riga ya shimfiďa musu sallaya tsayawa tayi abayansa ya ja musu sallah! raka, a biyu sukayi ya kama kanta yafara mata adu, o,i yakai minti talatin kafin ya saketa.

“ki ďauka wanna kaya kisa kizo mu kwanta sbd yau zan nuna miki niba fanko bane “yana gama fađan haka ya huce falo ďauka Lipton yayi yasha ya haďa da abinda ya siyo ya shanye.

Zahra zugum tayi tana tunani to me yake nufi da wanna magana.

“Ni kam ba abinda zaka min wlh kuma baz……… maganan tane ya tsaya sakamakon ganin sa datayi ya shigo ya kulle đakin ya kashe hasken ďakin.

“Ok bazaki sa ba da kinsa da kintaimake kanki.”
mtsssss taja tsaki “hmm bakiyi tsakiba “
“Dan Allah ka buďemin kofa na tafi naje na kwanta niba yar…… bata karasaba sakamakon hađe bakinta da yayi danasa wani irin felling ne yakeji sosai da sauri -sauri yake kissing nata cikin hanzari ya yage rigan dake jikinta dama ba komai a ciki rigan ne kawai jallabiyansa data sa haka ya rabata da komai na jikinta ya fara romance da ita.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Barrister 6

1 thought on “Barrister 7”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×