"Me kika yi ne wai?' Mama ta tambaya dafe da kirji.
"Ban yi komai ba, dazu da kika aike ni gidan Baba Cindo, lokacin da na je Aunty Sadiya na wanka. Shi ne na ga Goga ya fita dakinta yana tura waya a aljihu, bayan ta fito wanka kuma ta ce ba ta ga wayarta ba. Na fada mata abin da na gani da aka kira shi ya ce wai shi bai dauki komai ba, shi ne suka tafi police station. "
"Yauwa to Mama kin ji dalilin kiran."
Cewar police din yana murmushi.
"To ita kuma me za ta yi. . .