A yadda muke waya dasu na san sha Allah 7:30pm zuwa 8:pm sun shigo gida.
Dalilin da ya sa kenan karfe biyar na fara shirin abincin tarbarsu, kowa abin da yake so na yi niyyar yi mishi, Oga tuwo, Maman Khalil dambu, yarinyata kuma danwake.
Tun da nake kira ba ta cewa komai amma haka nan zan sanya a kanga mata wayar a kunne in yi ta surutu tana ji, amma dazu da na ce "Me kike so in dafa miki" Sai cewa ta yi "An wake" Ina jin su Maman Khalil na mata dariya, ni ma na. . .