Abba sai a san nan yasamu damar Magana yace" Haidar ka girma sosai ya matar taka?" Yana shafa kansa .
Ya dago yayi murmushi yace" Abba ashe kana nan nayi kewarka sosai na shiga mariaci sosai, shigowar Ikram ne ya dawo min da farin ciki cikin rayuwata " .
Yace kayi hakuri Haidar kullum da tunaninka nake kwana dole zaka shiga damuwa musaman da nasan na barka cikin mugayan 'yan uwana" .
Nan kowa ya fita ya barsu suka taba hirar yaushe gamo bayan anyi azahar suka dawo a ka sake sabon zama .
Alhaji Bashir ne yace" Haidar dafatan kuna zaune lafiya da Ikram. . .