Haka sukai ta farin ciki tace" bari na duba abincin mu Yaya" yace "tom" .
Haka suka gama hirar bayan ta sauke girkin san nan sukaje suka kwanta .
Ƙarfe uku da rabi suka tashi sahur har zata kwanta yace" Ikram yakamata murya daran watan nan mai albarka kinga muna da tarin bukatu a wajan Allah ya kamata mu dage".
Tace "gaskiya ne Yaya Allah ya shiga lamarin mu " yace "amin" .
Haka suka cigaba da zama yaja su sallah har aka kira asubah san nan ya barta ya tafi masallaci ita kuma tayi ta- ta ita kadai tana idarwa ta wanke kwanikan. . .