Skip to content
Part 6 of 6 in the Series Izina by Matar Sadiq

Bayan shi tabi da kallo wasu hawaye masu zafi suka biyo idanuwanta
a zahiri ta furta,

“Allah ya’isa tsakanina dakai Anwar, ka cuceni ka lalata-mun rayuwa, ka rabani da iyayena, ka jefa rayuwata cikin wani hali, wanda nake ji a yanzu bazan iya jure rayuwa ba tare da namiji a kusana ba, ka rabani da zaman gaban iyaye, soyayyar ka ta rud’eni na mance daraja da mutuncina na ‘ya mace, karshe ka jefa rayuwata cikin mummunan hali na shaye-shaye, na neme ka da maganar aure ka nuna mun kai bazaka auri mace kalata ba, wacce ta lalata rayuwarta.”

“K’arshe na tsorata da kalaman ka agareni, naji tsoron k’ara furta maka makammancin maganar da ta shafi aure tsakanina dakai, saboda ina gudun wulak’anci, koma ka koreni daga inuwar ka.

“Hakan kuwa zai k’ara ta’bar’bara rayuwata, na k’ara tsunduma k’azamar rayuwar da tafi wannan, saboda bani da kowa sai kai kad’ai a garin nan!! amma na gaji da wannan aikin sa’bon da kullum muke aikata shi nida kai!”

“Shin yanzu ko ina iyayena, mahaifiyata tana nan raye ko bak’in cikina ya zama a’jalinta, shin mahaifina yana raye ko kuma shima ya mutu?”

“Shin idan wannan tinanin nawa ya kasance, wani daga cikin su ya fad’i ya mutu ya zanyi da hakkin-su, ina Zane shiga da tarun zunubin fushin iyayena a rayuwa?”

Lallai ya kamata na nemi mafita wacce zata wanke wannan manyamanyan zunuban da aikata a rayuwata, ko zan samu tsira ga ubangijin da ya hallicce ni!”

“Lallai wannan rayuwar bata dace dani ba!”

Wasu hawayen tausayin kanta da wannan k’azamar rayuwar da ta za’bawa kane suka gangaro mata!

“Lallai namiji ba d’an goyo bane, kuma duk wanda ya d’auki namiji uba to lallai zata mutu marainiya!

“Horn d’aya yayi mai-gadin, ya bud’e masa wantamen-men gate d’in, cike da mamaki yake hango motar jami’an tsaro a fake a harabar gidan, fitowa yayi acikin motar yana mik’a tamkar wani wanda yayi aikin gajiya!

“Bud’e idanuwansa ke da wuya, jami’an suka kewaye shi suna fad’in, “your under arrest? Anwar mustpha!

“Cike da mamaki yayi wata dariyar, rainin hankali tare da yi musu kallon sama da k’asa! da dukkan alamu bawan-da yasan waye-ni acikin ku.

“Wani daga cikin-sune yace tabbas bawanda yasan kai waye, ka rik’e bayanin-ka idan munje kotu gaban shari’a, sai ka fad’a mata kai waye!

Amma mu nan aikin-mu zamuyi kuma duk wanda yayi yunk’urun dakatar damu zamu had’a dashi.

Mahaifinsa dake can gefe, cike da takaici yace, am sorry my son, ka bisu kuje, nima gani-nan zuwa!

Daddy in-bi wad’annan tarkacan.

A zuciye wani daga cikin su yace, kai kar ka fad’a mana maganar banza, ka-sakawa harshen-ka lunzami domin agaban hukuma kake.

Za ka shiga ne ko mushigar dakai?”

Wani mugun kalloh ya watsa masa tare da, shiga motar suka wuce!!

Anushka POV.

Betron! Ta kira sunan-shi cikin tashin hankali, kallon-ta yayi sau d’aya ya d’auke kai saboda yasan bakomai zata masa ba da-ya wuce maganar maleek!!
Hankalin-ta a tashe ta k’ara kiran-sunan shi cikin harshen indiyan-ci tace, Betron what happen to malik? na bincike duk cikin fad’in barracks d’in-nan baya-nan, na kira number-n shi is-not reachable.
“Hankalina ya tashi sosai, saboda nasan malik baya kashe wayar-sa. dan allah ka fad’amun. nasan-ba wurin wanda zanje na-samu gamshashshen bayani da ya wuce kai!,

“Murmushi yayi tare da cewa, Malik baya-nan, ai ni na d’auka kinsan da maganar, waye bai-sani ba duk cikin fad’in barracks d’in-nan?

“Look at me betron is not understand bayanan? ina ya-je?”

“Jiya jirginsu ya sauk’a Nigeria.”

“What Malik ya bar-k’asar nan ba tare da sani-na ba, malik anya akwai k’wak’walwa acikin kansa, anya akwai sauran tausayi acikin zuciyarsa?.” wani irin kuka ta fashe-dashi maicin rai, idanuwanta kad’ai zaka kallah ka tabbatar da tsantsar bak’in ciki wanda ya saje tsantsar k’aunar da takewa Malik?

“Anushka anya kina da hankali?” wai kinsan wa zuciyar-ki take so? Malik fa kisani baze ta’ba auran ki a haka ba, ballantana ta kai ku ga maganar soyayya, meyasa bazaki lura ki fahimta ba? sam addinin ki bai amince ki auri malik ba, addinin ku ba d’aya bane, ki daina wahalar da kan-ki.

A hankali ta d’ago da jajayen idanuwanta, ta watsa masa wani mugun kalloh na rainin hankali, dogon tsaki ta-jahh tare da mik’ewa jiki ba k’wari ta barshi a tsaye a wurin.

“Kai tsaye babban offishi ta nufa, na sama tare da neman permission, zata ajiye aiki na d’an wani lokaci bata da lafiya. kai tsaye cikin motar-ta nufa tare da yi mata key ta bar cikin barracks d’in.

“Gudu ta rink’a shek’awa akan hanya duk da irin jirin da take yana d’ibarta, amma bataji a ranta cewar zata rage wannan gudun motar ba, horn d’aya tayi mai tsaron gate d’in ya wangale mata gate d’in.

“Cike da tsananin mamaki yake kallonta yaude yasan ba lafiya, tunda yaga Anushka ta dawo gida yanzu, tun lokacin tashin daga aiki baiyi ba.

“Rai a ‘bace ta haura izuwa falon da yake sama, bakowa a falon hakan ya-bata damar wurgi da Jakarta, tare da fad’awa saman royal cotion d’in tana sakin wani marayan kuka mai sauti!!

“Tun daga k’asa Momyn nata ke jiyo sautin kukan nata, da sauri ta fito daga cikin kitchen d’in ta nufo inda take? Cikin harshen yaransu tace, Anushka meyake faruwa? ban-saba ganin kin dawo a irin wannan lokacin ba, lafiya?

“Stop it Mom” banaso ki takura kanki, akan sai kinji abun da ba amfanar ki zeyi ba, saide ma yasa miki ‘bacin rai, wannan matsalar tawace ni-ni kad’ai kuma bana buk’atar kowa yasani.. tana fad’in haka mik’e tare da barin part d’in ga d’aya.

“Ita kuwa Momyn da kalloh ta-bi bayanta cike da tsananin mamaki maganganun Anushka.”

Daddy POV.

Riging phone d’in-ne ya katse shi da irin dogon tinanin da yake-yi ganin numbern mai-gidan nasa yayi saurin d’aga wayar!

Cike da risinawa yayi sallama!

Daga can gefen akace a’a rik’e sallamar-ka, Abdul-malik Ibrahim ahamad, jami’in bincike. hmm wato abun nashi ya tashi daga binciken kisan marigayi commissioner. ya dawo kan yaro-na!!, nasani cewar baisan kowaye ni-ba.

Toh shakka babu abincin-ka ya kusa k’arewa daga gareni, zan kwace company na guda uku a hannu-ka. zan k’wace duk wata kadara da ka mallaka ta sanadiya-ta. matuk’ar baka dakatar da wannan binciken ba.

D’an-ka ne idan ka isa dashi kayi wani abu.

Ana fad’in haka ya datse kiran, wata iriyar zuface ta keto masa!! meyakai abdul malik, wurin da ba nan aka aike shiba.

“Da sauri ya fito yana kwalawa mami kira, cikin tashin hankali ta fito saboda tunda take Hubby bai ta’ba mata irin wannan kiran ba.”

“Subahanallahi hubbi lafiya?”

“Ina Abdul Malik?”

Amma ai hubbi kasan ba’a samun-shi a gida da irin wannan lokacin!

“Toh lallai ya jangwalo ruwan dafa-kawunan mu gaba d’aya, ya ta’bo abun da ze ruguza rayuwar gidan-nan ta farin ciki!!, lallai talauci ya fara kwan-kwasa ‘kofar gidan nan!”

“Hubby kai-mun bayani kasani a duhu!”

“A fusace ya mangare ta ya wuce sai faman huci yake kamar wani mayunwacin zaki!!”

Abdulmalik POV.

“Kamar yanda suka tsara haka komai aka tafiyar da al’amarin fitar ta cikin sirri!!”
Club ne k’ato babba wanda aka kashe masa mak’udan miliyoyin kud’ad’e, kid’a ke tashi sosai acikinsa, wad’ansu na gefe suna rawa maza da mata cristoci dama ‘ya’yayen musulmai, kowa sha’anin gabansa yake amma masu aikata aikin masha’a da sauran mataye wasu kuwa suna kora ruwan alcohol.

“Wa’iya zubillahi”

“Tsikar jikinsa na zubawa saboda ganin tsananin bid’alar da mutanen wurin ke aikatawa!!” da kyar ya iya ratsawa ta cikin mutanen yaja ya zauna a gefe a wata kujerar da bakowa akayi.”

“Ma’aruf ya kallah tare da cewa a nemo mun shayi a duk inda yake a wannan wajen.”

“Cike da ladabi ya amsa da toh yalla’bai.”

“Kallonsa ya miyar izuwa wurin faruq yana fad’in kasa ido sosai domin samun neman hujar muka zo ne!”

Jami’in tsaro ba ruwan shi da gida ko office idan hakar bincike ya tashi.”

“Lallai kasa ido a ko’ina.”

Cike da ladabi ma’aruf ya mik’o masa shayin.

Kar’ba yayi yana fad’in “ya akai ka jima haka?”

Sosa keyarsa yayi kafin yace “ayi haƙuri yalla’bai.”

Murmushi kawai yayi tare da kur’bar shayin kad’an!

Ya dad’e a haka sosai yana kallon irin d’anyar masha’ar da sauran mutane ke aikatawa a wurin, daga cikin zuciyarsa abun na matuk’ar k’ona masa rai sosai.”

A hankali faruk ya k’ariso gare shi, ta’ba shi yayi ta baya cikin rad’a yace “yalla’bai Muhammad alhasan ya shigo yanzu da jama’arsa.”

Murmushi yayi yana fad’in

“Aiki yay kyau”

“Mikewa yayi, ya nufi wani wuri wanda aka k’awata shi sosai da kayan ciyeciye da shaye-shaye, yana zuwa ya mik’a masa hannu suka gaisa.

“Alamu yayi masa da ya zauna, zama yayi a kujerar da take fessing d’insa.

“Wani daga cikin mutanen sane ya zuba wani abu a glass cup ya mik’o masa.

“Da dukkan alamu giya ce, hakan yasa shi ya mutsa fuska ya kar’ba ya direta a saman katon glasa table d’in dake tsakaninsu, badan zai sha ba.”

“Sunana Abdul malik Ibrahim Ahamad, ni-ne jami’in da aka tsayar domin gudanar da bincike akan kisan G.I.G

“Kai kuma kaine mataimakinsa da aka tsayar domin gudanar da bincike kafin zuwana!”

“Ka bada shaidar karayar cewar baka wannan gari ka tafi ganin likita kasar Australia hmm sai gaka a nan.”

Anyway ba wannan ba, inason duk wasu bayanai akan aikin da ka kula dasu daga nan zuwa k’arfe biyar na yammacin gobe”

“A matsayin ka na jami’in tsaro mai kula da lafiyar al’umma bai kyautu a sameka a irin gur’bataccen wuri irin wannan ba, hakan karya dokar aiki ne, a matsayin ka na me gyaran tarbiyar al’umma, yanzu kuma kaine me tarwatsa ta!”

“Tirrr da wannan kazantaccen aikin naka!”

Yana kai nan ya mik’e suka fice, saboda bai ga abun da zai zauna ya cigaba da yi a irin wannan kazantaccen wurin da ake sa’ba ubangiji ba.

Dole a d’auki mataki akan irin wannan alfashar da ‘ya’yayen musulmai ke aikatawa a irin wannan wurin.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Izina 5

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×