Skip to content
Part 14 of 22 in the Series Jahilci Ko Al'ada by Harira Salihu Isah

Ɗage kafaɗa Jay yayi irin ko a jikina ɗin nan, yace “uban masu jin kai ai wallahi tun wuri ka rage wannan ji da kan ko kuwa kasha wahala a hannun ‘yar mutane don na tabbata za’a wahalar da kai kamun a baka haɗin kai kuma kai kaja, sannan za ta qeraka staff ka shiga hankalin ka dan mata dai sun wuce duk tunaninka a seta maza duk mulkinka a waje a gida sune masu mulkin ƴan aljanna ba Allah dai ya qarawa mata albarka da ni’ima mu kuma ya qara mana qarfin kwasan ni’iman”.

“Mtssswww! Kai fa Jay iskancinka bai da uban gida, yaro qarami sai son maganan banza” cewar DMD da ya ciro wayansa yana lastawa kaman ba shi yayi magana ba.

Wani wawan dariya Jay yayi kaman wanda akawa kyauta yace “dude kai cikakken ɗan renin hankali ne Wallahi nine yaro? Inaji shekara biyu zuwa uku ka bani to ba banbanci sannan kuma maganan banza dole nayi ta atou harka ce ta sharholiya kuma ta jin daɗi da samun nistuwa, ni wallahi zama haka ma ya ishe ni dole amun aure a wannan shekara dan bazan yarda na cika shekara talatin na stofe kaman kai bansan wancan hanyan ba, ni ko classic bazawara zan aura dan ban cika son gargada ba dama indai garin akwai ni’iman damuna sannan ko ina da damshi ga daɗi to an wuce wajan muje zuwa kawai kwasan albarkatun gari ba kakkautawa harka ta sharholiya, a shekara guda kuma za kaga yaro ya haifo yaro”.

DMD dubansa ya kai kan stadadden agogon dake maqale a kakkauran hannun sa, ganin time sai ya miqe yana faɗin “in ka gama maganan yarantan taka sai ka taso mu wuce dan ba kwana a garin nan zan yi ba, in kuma baka gama ba sai ka dawo”.

Hararansa Jay yayi ya miqe yana qwalawa Farooq qira, nan ya fito a shirye staff cikin qananun kayan da ya yi matuqar amsan sa.

Farooq (malam ba wasa) chocolate color ne amma ba mai duhu ba, yana da saje da gashin gemu, fiskan sa mai ɗauke da dogon hancin sa da idanuwansa ƴan dai-dai, yana da stayi amma ba sosai ba dan DMD ya fisa stayi sannan ba za’a ce masa stiriri ba kuma ba za’a ce masa mai jiki ba saɓanin DMD da Jay da jikinsu kenan kaman na mata waɗan da ake ce musu ƴan duma-duma abinda ya ɓoye jikin DMD kuwa stayin sa dan yana da stayi dai-dai burin ko wacce mace ga kuma faffaɗan qirji, shi Jay kuma stayin ba sosai ba sai jikin sa ya ɗan nuna.

Fita suka yi duka har inda suka Parker motocin su, Jay da Farooq suka shiga na Jay shi kuma gogan ya shiga nashi ya mata key.

Sweedy da sallama suka shiga palourn, Hajja da ke zaune tana kallon tashan kung-fu kaman tana jin Chinese, jin sallama sai ta juyo tana ganin su ta fara washe baki tana faɗin “maraba lale da kyawawan jikokin Hajja”.

Sweetie ce ta qariso ta faɗa jikin Hajja tana magana da turanci “Hajja ta nayi kewanki”.

Dundu Hajja ta mata tace “kindai san ke ƴar lukuta ce ba kamar sauran ba to ɗaga ni karki karyani da wannan yaren mutane da kuke satowa ba za ku iya naku ba”

Tura baki sweetie tayi dan ta stani ace tana da jiki, tashuwa tayi ta koma gefe tana magana da Indianci.

Gaishe da Hajja su sweedy suka yi ta amsa da fara’a dan Allah ya gani tanason yaran Mustaphan ta ba kaɗan ba barin ma dai yayansu babban jikanta.

“Halan ku da wa kuka zo? Naga ku kaɗai ku ka shigo.

Sweedy tayi shiru sanin tana faɗa Hajja za ta hau surutu amma sai ta ji muryan sweerie na faɗin “ai Hajja Darling ne ya kawo mu yanxu ma ya tafi wajan big bro ne zasu dawo tare” ajiyan zuciya sweedy tayi jin abinda sweerie ta faɗa tasan ko ba komai yanxu kam albarka zata saka masa.

Hajja jin haka sai ta washe baki tace “ban dai so qanin miji yafi miji kyau ba amma ba komai Allah kawo su lafiya ƴan albarka, shi kuma jabiru zai zo ya faɗa mun Maryam ce ko Nura suka ce ya fita da har zai ja mun jika wajan shirmen sa.

Da qyar ta lallaɓa sweetie ta haqura har ta sake suna dariyansu dan dama babbar abokiyar shirin ta kenan.

Su sweedy suka tashi suka shige ciki ɗakin da yake nasu ƴammataye amma banda sweerie dan ita ɗakinsu da Afrah ne sai sweetie kuma wajan Hajja take tarewa muddin tazo ba tare da Ammi ba.

Samun Afreen suka yi tana kwance tana chat, ganin sweedy kaman daga sama ba shiri ta miqe ta rungumeta tana cewa “sweedy yaushe kuka zo? ke da wa? Ina Darling?

Sweedy hugging nata tayi tana murmushi dan daman tasani wannan wajibi ne sai ta tambayi Darling dan mutuwan sonsa take yi shi kuma Darling ko a jikin sa.

“Yau ɗin nan muka zo ko hutawa ba muyi ba aka kawo mu nan kuma aikin Darling ne amma ya tafi wajan big bro” sweedy na faɗa tana ɓata fiska dan gajiya.

Afreen tace “sorry my dear, sannunku da gajiya”.

Sweerie ma ta gaida Afreen kana ta juya ta fice dan zuwa ɗakin su ita da Afrah su ma.

Da sallama ta shiga tana faɗin “qanwata Afrahty my love ina kike?

Afrah dake cikin banɗaki dan tashuwanta bacci kenan, jin muryan sweerie dan tasan ita kaɗai ke qiranta haka, barin wankan tayi ta ɗaura towel ta fito da gudu tana faɗin “oyoyooo sister sweerie”.

Hugging juna suka yi suna dariya Afrah tace “ke kullum ba zaki ce Afrahty kaɗai ba sai kince qanwarki kuma shekara guda kawai fa kika ban, shiyasa inajin qiran nan nasan kece, ina mintin zuciyata? Ina yaya sweedy? Yaushe a gari? Wa ya kawo ku? Ina Darling?

Hararanta sweerie tayi tace “kede baki sauya ba kullum tambaya kaman ƴar jarida”.

Dariya Afrah tayi tace “naji daɗin zuwanku dama ina missing na habibty na thank God gaku nan weekend zai yi daɗi, yanzu dai bani amsa ta”.

Sweerie murmushi tayi tace “1 mintin zuciyarki na wajan Hajja, 2 yau ɗin nan muka zo, 3 yau muka diro Nigeria,4 Darling ne ya kawo mu amma daga Gombe daga Canada kam Abiy ne, 5 Darling yana tare da big bro”.

Dariya Afrah ta sanya tace “kin bani duka kenan? Shikkenan sannunku da zuwa ba nayi wanka nazo na baki labarin Habibty ta” ta faɗa tana shigewa banɗaki ita kuma sweerie ta qarisa kan gado tana kwanciya.

“Hajja ina tambayanki ina Aunty masoyiya kinyi shiru ko? Faɗin sweetie tana tura baki.

“Sakalatun sakalalliya iyayen taɓara gaba ɗaya yarinya kin girma kin zama budurwa amma sakalci uwa sakakken mara, ni ina nasan kina da masokiya ne ko masogiya”.

Tura bakin ta kuma yi tace “Hajja yaya Afrahty fa nake nufi”.

“Au ai sai kice mun Fatu ni ina nasan wani masokiya, tana can ɗaƙin su”.

“Shikkenan Hajja na barki ke ɗaya na tafi wajan Fatu” ta faɗa tana dariya ta shige hanyan ɗakunan.

Hajja danqwalo ta bita da shi tace “tijararriya sakalalliya zaki dawo ki same ni ai ba dai sunana kika qira gastau-gastau kamar ba sunan uwar ubanki ba”.

Jay har sun iso qofan gidan Hajja sai ya waiga bai ga motan DMD a bayansa ba, cikin sauri ya ciro waya yayi dialing layin sa.

“Hello dude ya banganka ba ina ka tsaya?

“Mtsww! Ni ba zani gidan Hajja ba ku same ni a inda nace maka zan je”.

“Dude please ka zo wallahi kuwa za mu bika can ɗin ka ji” Jay magiya ya dinga wa DMD har dai cikin ɓacin rai ya kashe wayan ya juyo motansa hanyan gidan Hajja.

Farooq na dariya yace “gaskiya DMD ko mace ta basa hanya a rigima da jan rai”.

“Ai wallahi freind ba iya jan rai ba har da na aji kaman ance masa nima ba al’qalamin ne da ni ba kaman shi”.

“Amma ai zai zo ko?

“Tunda ka ji ya kashe waya to zai zo amma xansha surutu kam dan kasan halin sa da ya dinga yawaita magana ya gwammace yayi abinda bai yi niya ba”.

Murmushi Farooq yayi dai-dai suna qarisa shiga palourn bakinsu da sallama.

Ganin ba kowa a palourn sai suka zauna kawai suna kallo, Jay yace “gwanda da Hajja bata waje dan da taga shigowana bata gansa ba ta farawa mutane aiken surutun ta”.

Bai ida rufe baki ba ta fito sanye da hijabin ta hannunta da carbi tana cewa “munafiki wato ma uwar ubanka ce mai surutu kai amma yaran nan kun renani uwayenku duk basu muku tarbiya ba” nan ta fara masifan kuwa tana tambayan bata ga Muhammadu ba?

Farooq ya gaisheta ta amsa tana tambayan sa ayyuka da gidansu ya amsa lafiya.

Ta buɗe baki zata qara tambayan sa sai sallaman sa da ta jiyo yasa tayi shiru ta hau washe baki.

Abiy yana shigewa gidan yayi mummunan gani dan kuwa Amaryan sa ya gani da mayafi da qaton akwati tana kuka ta taho zata fita ko kallon sa ba tayi ba (dama tana jin qaran motan Abiy ta haɗa kaya ta hau kukan kirsa).

Kallonta yake cike da mamaki yama kasa cewa komai har ta fice a palourn, da qyar ya iya ɗaga qafansa a inda yake staye yayi waje ganin har ta shiga mota tana qoqarin tayarwa, da sauri ya qarisa jikin motan yana mata magana “sweetheart me ya faru? Me aka maki? Ke da wa? Ina kuma za kije baki gayamun ba gashi kina kuka?

Aunty Amarya ko kallon Abiy taqi yi sai aikin kukan da take yi ta qara volume ta kau da kai (kana gani kasan kukan munafurci ne).

Abiy sai aikin rarrashin yake da tambayan ba’a si dan ba qaramin tashin hankali ya shiga ba, babu maimuna itama wannan tana qoqarin tafiya ina zai sanya kansa da yawan buqatan sa? Ai dagewa yayi yana rarrashi Aunty Amarya wacce da abun ya mata yanda take so ganin har da cewa zai saya mata mota sai ta buɗe murfin motan ta fito nan ma bata ko kallesa ba kuma bata ɗau kayanta ba ta shige cikin gida har ɓangaren ta direct ɗakinta ta shige tana kan kukan ta.

Abiy ajiyan zuciya yayi ganin dai ta koma cikin wanda yasan yanzu lallashin zai zo masa da sauqi tunda ta fasa tafiyan, shima bin bayanta yayi yana ƴar waqan soyayya.

“Rabi’atul adawiyya masoyiya ta Amarya ta ƴar aljanna mai haquri ga kawaici ga hankali(Abiy ya faɗa sosai).

Har cikin ɗakin ya bita, yana shiga ya cire babban rigar sa ya masta kusa da ita ya jawo ta jikin sa yana bubbuga bayanta yana qoqarin laluɓo bakinta ta fiske cikin kukan kirsa tace “Ni a gidan nan ba’a ɗauke ni a bakin komai ba iya amfanina kenan a biya buqata da ni duk sanda aka so amma wai ace dan ban haihu ba baza’a girmama ni ba aban matsayin uwa ko da zanji sanyi a raina, kowa ya tashi bai da mareniyar wayo sai ni har ɗan ciki na ya mare ni” duk maganan da take cikin kuka.

Abiy da yake mamakin wa zai mare ta sai yace “sweetheart ke da wa?

Hararansa tayi tana kuka tace “Ni da wa kuma ina banda yaronka wai ace har yaronka yayi girman da zai mari matar ubansa ina a matsayin uwar sa dan ni ba mazaunin yadikko nake zaune da su ba yaro na kowa ne”.

Abiy da mamaki da ɓacin rai suka cika sa yace “wai har kina nufin MUFADDAL ya mare ki? Yaushe duk rashin kunyan nasa ya kai haka akan me zai mare ki?

Cikin taqaici Aunty Amarya tace “wato baka yarda ya mareni ba? Zanwa yaronka sharri ko? Hmmn! Ba komai dama nasan iya mastayina kai ma baka qaunata kawai amafanina gare ka biyan buqatan ka tunda har kana tunanin duk irin qaunar da nake wa yaran nan zan musu sharri, wai kana tambaya akan me ya mare ni ko? Hmmn! To akan gaskiya kawai dan ita gaskiya ɗaci gare ta, yarinyar nan sweerie na samu ta kunna waqa tana aikin tiqan rawa sai na kashe nace bai kamata ba tana ɗiya mace ga can mama mai aiki a kitchen taje ta tayata wani abun yafi wannan rawa dan ita mace ce kuma aurar su za muyi, kar a dawo mana da su basu iya komai ba, amma yarinyar nan tan tashuwa buɗan bakinta ba zata yi ɗin ba ina ruwa ai ni ba uwarta ba balle na sanya ta aiki. Na fito na dawo ɗaki bance mata komai ba sai can fitowa na na samu an juyemun gaba ɗaya ferfesun da na shiga kitchen na maka da kaina ina mamaki sai ga yarinyar nan ta fito tana faɗamun ita tayi na ɗau mataki, cikin ɓacin rai na fara mata faɗa nace nima mahaifiyar su ne bai kamata ba, ban ida rufe baki ba MUFADDAL ya wanke mun fiska da mari wai na daina haɗa kaina da Ammin su dan ita ba sa’a ta bace” Aunty Amarya na gama magana ta fashe da kuka mai qarfi wanda in kaji ka ɗauka ko uwatta ce ta sheqa.

Abiy cikin tsananin fushi ya miqe zai fice amma aunty amarya ta riqo sa tana kuka tace “nikam kayi haquri na yafe musu Allah shirya mana su dan kaga sun riga sun fita bai kamata ka fita cikin fushi ba banso komai ya samarmun kai mijina kayi haquri kaima ka yafe musu”.

Kallonta yayi ransa a ɓace yace “Rabi’a har zaki ce na yafe musu kin yafe musu to wallahi ba za’a yi haka da ni ba na auro mata yara su hanata sukuni dan suna taya uwarsu kishi to zan ɗau mataki dole da shi MUFADDAL ɗin da ita MUNAWWARA su san nine na haife su ba su suka haife ni ba renin yaron nan ya fara wuce gona da iri”

Aunty Amarya murmushi tayi ganin Abba baya ganin ta amma sai ta lanqwasa murya tace “komai suka yi kai ne ka ja dan ya kamata tun farko ka nuna musu ni ma uwarsu ce amma baka yi hakan ba dan haka haquri gare ni ya zama dole tunda yaran mijinane kuma ina sonsa matuqa dan haka dole gare ni na qaunace su suma”

Abiy na huci ya dage zai bi DMD amma Aunty Amarya ta hana sa nan dai ya bata haquri kan zai ɗauki mataki da ta nuna bata so ta haqura sai yayi fushi ya tafi ɗakinsa wanda ganin haka tayi hamdala a rai tasan komin yaya sai ya ɗau mataki dan shirin nata ya tafi yanda take so.

Wata ƴar iskan dogon riga ta sanya shara-shara ta tamke nononta da ya fara kwanciya a bresia tayi hanyan ɗakin Abiy, tana shiga ta same sa da waya a hannu yana aukin qira ana gaya masa “not reachable” alaman ba network, qwafa yake kan jerawa dan har yanzu cikin ɓacin rai yake, jin qamshin Amaryan sa ya sanya shi juyawa duk da kuwa fushin da yake yi da ita, wanda kallo ɗaya ya mata ya kau da kai.

Aunty Amarya ganin haka sanda ta girgiza da fushin Abiy tasan shi koma menene tayi wannan shiga da wannan qamshi zai haqura dan haka ta qarisa ta zauna kan cinyan sa tana qara basa haquri tana shafa sa.

Abiy da Allah yayo sa da qarfin sha’awa duk da kuwa manyantan sa amma garau yake dan haka lokaci guda ya biyewa Amaryan sa suka lula duniyan ma’aurata.

DMD qarisa shigowa palourn yayi da sallama a bakin sa qasa-qasa dan ko ka kasa kunne ba jiyowa za kayi ba sai dai in ka kalli laɓɓansa waɗanda ke mostawa a hankali kaman mai rigima da su, fiskan sa a haɗe kana gani kasan a cike yake qiris yake jira ya juye akan mutun, ba tare da ya kalli ko su Jay ba balle Hajja ya samu waje ya zauna ya fidda wayan sa ya sa Bluetooth.

Hajja kallon sa tayi ta kalli su Farooq ta kuma kallon sa, cike da masifa tace “Muhammadu uwaka maimuna”

Ɗago idanuwan sa yayi da har sun sanja kala, rai a ɓace ya wastawa Hajja wani mugun kallo, kallon karki sake qiran Uwata.

Hajja qwafa tayi ganin irin kallon da yake mata ta ce “an faɗa uwarka maimuna tashi ka cinye ni ɗanye ɗan gidan marassa ji yaro sai aukin zuciya kaman na fir’auna uwarka ta fi uwar wa? Dama wa ya kawo ka gida na tunda kasan rashin kunya ka ɗibo ka taho da shi ba kirki ba?

Cikin fushi ya miqe ya juya zai fice dan yasan muddin ya buɗe baki to abun ba zai yi daɗi ba dan kasancewarta kakarsa bai dame sa ba, kawai tayi kaɗan ya tamka mata shi yasa ya miqe ya fice.

Yana fitowa ya wuce ɗayan sashin da yake nasu yara maza yana ji kaman ya kamo Jay ya shaqe sa dan shi ya jawo masa shigowa gidan.

DMD na barin palourn Afreen ta shigo, jin hayaniyan Hajja ta san tabbas DMD ya shigo nan ta baza maganenta (idanuwanta) amma baya palourn, idonta har da qwalla ta haɗa fiska tace “ke dai Hajja wallahi kin cika masifa da surutu an samu ya zo shine kika kora sa da halinki, big bro Ina yake?

Jay da shima ya cika da surutun Hajjan hararan Afreen yayi dan shima yaji haushi yace “igiyar ajiyan sa da kika ban ya ɓata idiot kauce mun a gani”

Murguɗa baki tayi ta fice, tana fita kuwa ta ga motan sa wanda ke nuni da yana cikin gida bai tafi ba dan haka cikin sassarfa ta tuni sashin yayyunta mazan.

Hajja ma da ta cika da baqin halin jikan nata da ke damunta ga ta masa faɗa kuma bata jin daɗi duk da kuwa irin kallon renin da ya mata amma sonsa da take yi yasa take jin haushin faɗan da ta masa dan haka miqewa tayi itama ta fice dan tasan ba zai wuce yana sashin su ba.

Afrah da sweetie ne suka fito daga ɗaki inda suka baro sweerie a ciki.

Sweetie na ganin Jay ta yi wajan sa da gudu tana cewa “oyoyo big bro”

Afrah kuwa ganin wanda ke zaune gefen big bro ai sai ta storita ta waro ido a ranta tace “Malam ba wasa!”…

<< Jahilci Ko Al’ada 13Jahilci Ko Al’ada 15 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×