Aman da Amira ke shekawa bai sa sun kula da halin da take ciki ba saboda cakewar da suka sa gaban su.
Gaba daya ciwo yayi Mata sallama
Hakoranta suka soma haduwa da juna tana makyarkyata ga kanta da yake sarawa tamkar zai rabe biyu. Ga kuma kaurin hayakin da suke busawa Wanda ya Kuma hargitsa ta.
Akan idonta bayan sun gama bushe bushen hayakin suka koma kan maganin tari na kwalba.
Ga mamakinta shi wannan maganin tarin tayi zaton sai ana tarin ake Shan shi.
Kawai gani tayi suna daga kwalbar suna zazzagewa cikin su.
Sai da suka gama. . .