Skip to content
Part 5 of 9 in the Series Kaddarar So by Fatima Rabiu

Funtuwa, Local Government Katsina States Nigeria.

Tunkwal tunkwal tunkwal. Sautin dakan da D’an Lami keyi a tsakar gidan, yake bada wannan sautin. Dakan yake abunsa, yana yi yana chab’e tab’aryar, yana wak’ar umar m sharif, yana tab’awa had’e da rik’e k’ugu.

Yanzu ma d’an dakatawa yayi da dakan gana duban Maryam dake wanki a duk’e a k’asa, fari yayi da ido, yana cewa “ke y’ar uwa ke kuma a haka zaki k’are da zaman gida, da bautawa wasu, ya kamata dai ki san abunyi kinji k’awalli?”

Dubanta ya sake yi jin babu abunda ta ce, kai bama ta d’ago ba bare har yasa ran zata tanka masa. Tsaki yaja yana cewa “miskila kawai” yana murgud’a baki.

“Ahayee nanaye”. Ya saki wata shewa ganin Mafida an fito za’a tafi yawon data saba.

Matsawa yayi suka tab’a da Mafida, suna sakin shewa kamar wasu abokai.

“Kai kin ganki kuwa ta waje na, kyau iya kyau, dan uban namiji dole ya sara miki, dole k’anwar nak’i kici kud’in k’ato, ahh ahhh haaayeee”, ya idasa maganar tare da sakin wata shewar

Fari tayi da ido, tana cewa”kai Lami shi yasa fa, duk gidan nan, nafi shiri dake, ke d’in k’awar arzik’i ce. Ni ko ya maganar mu ta zuwa wajan Malamin nan, ka amso mana ganin nan, kasan wannan harkar dole ake had’awa da Malaman tsubbu”

Wata shegiyar dariya ya saki yana tab’a hannu, ya ce “ai kin san Lami bata wasa da Malaman tsubbu kwaro-kwaro lingu-lingu, ba inda bata san inda Malamai suke ba, ai ko nan da birnin sin ne, indai nasan Malamin tsubbu yake to sai na je can, domin duniyar nan ba’a zama haka”

Dariya suka sake saki had’e da shewa. Maryam dake jin mi suke cewa, yasa ta saki ajiyar zuciya, tana binsu da kallon takaici, bare ma Mafidar wai y’ar uwarta ce haka, ita kam baccin ance dangin Mahaifiyarta ba’a san inda suke ba, kawai dama K’anin Kawu Jafaru ya had’u da ita, ya taimaka mata ya aureta, amma harta koma ga Allah basu san danginta ba. Wasu hawaye ne taji suna shirin zuraro mata, ba shiri ta kai hannu ta share su, tana addu’ar duk inda dangin Mamarta suke, watan wata rana, Allah ya sadata dasu.

Sukuntuni Karamar Hukumar Kankia Katsina States Nigeria.

“Zauna Fulani ina so na sanar dake wata magana wacce ya kamata ace kin sani a yanzu, domin ina ji a jikina kamar lokacin sanar dake ne yayi”

Da mugun sauri Fulani ke duban Inna Wuro dake maganar, ganin ta d’akko wani k’unshin zani had’e da wata sark’a. Usman ne ya jawota a jikinsa ya zaunar da ita. Audu kuwa bai so Inna ta sanar da Fulani abunda ya dad’e da shud’ewa ba.

Inna ta ci gaba da cewa “hak’ik’anin gaskiya, Fulani, nida Baffa Mlm ba mune muka haife ki ba….. Wata irin hajijiya Fulani, ta fara gani, duk da a zaune take, amma gani take kamar juyata ake, maganar ce ta dake ta tunda take a duniya bata tab’a jin magana makamanciyar wannan ba.

“Inna, amma dai wasa kike min ba?”

“Fulani mun tab’a wasa irin wannan dake ne?, ki natsu kiji abunda nake son sanar dake”

Kwata-kwata Fulani ji take kamar ba a duniya take ba, wasu zazzafan hawaye taji suna zub’o mata, kai ina hakan bazai yuwu ba, tunda taso ita su Baffa ne ta sani a iyayenta, koda wasa basu tab’a nuna mata wata alama da zata fahimci cewa ita ba y’arsu bace, amma rana d’aya azo ace mata wai ba sune iyayenta ba, ina hankalinta bazai tab’a d’auka ba.

Tashi tayi a zabure tana girgiza kai, tana cewa “wallahi Inna bana son sanin gaskiyar, ni dai ki barni a hakan, dan Allah Inna ki ce min wasa kike”

Wata tsawa Audu ya daka ma Fulani, wacce tasa ta koma ta zauna ba shiri, jikinta ya kama kyarma hawaye na zuba kamar an bud’e fanfo.

Inna Wuro ta kalli Audu tana watsa masa harara, k’asa yayi da kansa yana batsarwa.

“Fulani ba wasa nake yi ba, tabbas ba mune muka haife ki ba, ki bani aron hankalinki kiji ya aikai kika kasance tare damu”

Shekarun Baya Da Suka Wuce.

Tsaye Baffa Malami yake, ya gama yo itacensa yana niyyar dauka domin ya nufi gida, Usman dake can yana k’ora masu shanaye da basu wace guda goma ba. Kamar ance Baffa ya juya ya hangi, wata mata yashe a k’asa duk taji ma kanta ciwo kamar bacci take kamar a sume take, ga k’aton ciki da take d’auke dashi.

Da zafin nama, Baffa Mlm ya kwad’a ma Usman kira, ba shiri Usman ya zo da saurinsa harda had’awa da gudu, ya iso wajan. Ganin abunda Baffa ya gani ne yasa ma Usman d’an tsorata, d’an ja baya yana cewa “Baffa, ko dai aljana ce karka tab’a ta Baffa”

“Haba Usmanu, ya za ka ce karna tab’a ta, kama min ita muje gida da ita domin mu bata taimako, baka ganin tana bukatar hakan, kuma ba aljana ba ce mutum ce, kuma koda aljanar ce ai mu da niyar taimako muka zo”. Ba yadda Usman ya iya haka ya taimaka Baffa wajan kama matar, domin yasan Baffah bazai fasa taimaka mata ba, shi haka yake da tsananin tausayi da kuma taimakon jama’a.

Shigowarsu cikin gidan, Inna Wuro dake madafa tana d’umamen tuwo, taji Baffa na kwala mata kira. Da sauri ta fito daga madafar, abunda ta tarar ne yasa itama waro ido waje, gabanta na fad’uwa ta ce “Baffa ina kuka samo wannan kuma?”.

“Yanzu dai kije ki samo min ruwan zafi, zan had’a mata magani, sana ki taimaka mata kiyi mata wanka, ki gyara mata jikinta, kayan dake jikinta ki tabbatar kin adana su saboda da nan gaba”

Da to kawai Inna Wuro ta amsa, tana tashi domin cika umarnin mijin nata.

Duk abunda ya kamata sai da Inna Wuro tayi, kayan kuma ta idana su, hatta wata sark’a dake wuyan matar Inna Wuro ta b’oye su kamar yadda Mlm ya buk’ata.

Kwana biyu matar nan bata farka ba, anata mata maganin hausa, da yake Baffa Mlm yana bada taimakon magani matane da yawa a garin shi ke basu magani.

Yau kusan sati kenan matar nan dai bata farka ba. Zaune suke a tsakar gida, Inna Wuro ta kalli Baffa ta ce “ni ko Mlm, anya matar nan zata farka kuwa, abu shuru kamar wacce ke baccin mutuwa?”

“Za ta farka in sha Allah, ai inda zaki lura, tana lumfashi a yadda take, motsawa ne kawai bata yi, bugun zuciyata na tafiya ina ganin kamar dogowar suma tayi, kuma kamar akwai sihiri tare da ita”

“Haka Malam nima na lura da hakan”

Suna cikin tattaunawa akan zancen ta suka ji ihu daga cikin bukar da matar take kwance. Ai ko da gudu suka nufi bukar, Malama na cewa Alhamdulillah.

Koda suka shiga, a zaune suka iske ta, sai bin d’akin take da kallo, babu um babu umm umm tana ganinsu ta sake tsorata, da kyar da kyar suka samu ta d’an saki jiki dasu, a tak’ace dai sai dai suyi mata magana ta d’aga masu kai, amma baki babu shi.

A haka ta shafe wata d’aya a tare da su, harta yi sabo da su, a hankali a hankali kuma bakin nata shima ya bud’e sosai sukai sabo da Inna Wuro.

Watan haihuwarta yana kamawa, da Baffa da Inna kai harma da su Usman ko ta ina ganin gata take, inda ko sunanta ta manta shi, sai inna dake kiranta da Fulani kawai.

Wata rana ta tashi da nak’uda sosai hankalin Inna ya tashi dan har Baffa yaso a kaita asibiti, amma ganin haihuwar ta taho gadan-gadan, data zo kuma saita tsaya hak’ik’a tasha wahala sosai, kamin Allah ya sauk’eta lafiya, ta haifo y’an biyu duka mata. Karku so ganin irin farin cikin dasu Baffa suka tsinci kansu a ciki, Baffa kuwa kamar shine akai ma haihuwar.

Kulawa iya kulawa, Inna Wuro nayi ma Fulani sosai suke bata duk wata kulawa data dace. Ranar suna aka sama yara sunansu na asali wato Hassana da Husaina, Baffa ne ya yanka masu rago har biyu da shano.

Wata rana da su Baffa baza tab’a mantawa da ita ba, ranar da suka tashi da safiya babu Fulani babu labarinta sama da k’asa suka nemeta suka rasa, ita da babynta guda d’aya, sai dai ta tafi ta bar mana ke Fulani. Wadda ni ce nasa miki sunan Fulani na maida miki yadda muke kiran Mahaifiyarki dashi, domin Allah yayi muku kyau kamar Fulanin asali, hakan yasa nake kiranki da hakan keda ita. Wadda Baffa yayi kukan rashinta , ke hatta muma da kyar gidan nan ya dawo yadda yake, domin kamar kurciya akayi mata ne, take yawo gari-gari, kuma tana tashi tayi gaba da y’ar uwarki, amma tabar miki kayan jikinta data zo dasu, da sark’ar dake a wuyanta ranar da su Baffa suka kawo ta gidan nan”.

Inna ta idasa maganar hawaye sun wanke mata fuska, kuka kawai Fulani keyi, ta rungume kayan Mahaifiyarta, tare da kallon sark’ar, gaba d’aya kayan ta had’a ta rungume tana rusar kuka. Usman dake kusa da ita ya rungumeta yana d’an bubbuga bayanta alamar lallashi, idonsa shima yayi jawur tuno da Mahaifiyar Fulanin mace mai kirki da sanin ya kamata.

Da kyar suka lallashi Fulani da daina kuka, amma duk ta zama suku-suku ko magana yanzu wahalar yi mata take, sai dai tabi mutum da ido, gashi wannan fad’uwar gaban har yanzu sake jinta take, sosai.

Dare 11:00Am na dare

Garin sukuntuni ya d’auki shuru, kowa yana makwancinsa yasa hak’ik’arinsa domin ya huta. A dai-dai wannan lokacin kuma Fulani ta tashi domin shan ruwa, wata irin k’ishir ruwa ce ta tayar da ita. A sanan kuma mafarin K’ADDARAR ta zai soma, domin yanzu bata ga komai ba, harta kai ga matakin nasara a rayuwarta. Haska fila tayi, tana kallon Inna dake bacci, fita tayi gabanta na tsananta fad’uwa, bakin randar ta tsaya. Ta kai hannunta domin d’ibar ruwan kenan, taji wata irin k’arar Bindiga, had’e da kururuwar mutane, kamin kota ina k’arar Bindigogi su k’arad’e gaba d’aya ilahirin garin nasu, ihun mutane had’e da kururuwa, tashin k’arar Bindigogi kawai kunnuwanta ke jiyo mata. Sakin k’ofin Fulani tayi ruwan da bata Sha ba kenan, jikinta ya kama kyarma kamar wacce aka jonama wutar neper. Da gudu su Inna Wuro suka fito daga d’aki, tsayawa sukai tsakar gidan hankali a mugun tashe.

Inna ta ce “mun shiga uku, Audu ba dai y’an Bindiga bane yau a garin nan, Innallihi wa’inna alaihir raju’on”

Da sauri taje ta kama Fulani tana cewa “wayyo Allah Usman ku ceci y’ar uwarku kurku bari a kasheta bata sadu da y’an uwanta ba”

Inna na idasa maganar suka ji an banko k’ofar gidan, an shigo, wata wawar bugar zuciya ce ta riskesu su duka. Zubewa su kai gaba d’ayansu a k’asa, gani y’an Bindigar sun shigo gidan, sun zagaye su, ga Bindigogi nan rik’e a hannunsu masu hatsarin gaske.

“Dan darajar Allah kuyi hakuri karku yi mana komai in… Wata uwar tsawa wani daga cikin y’an Ta’addar ya bugama Inna dake maganar, ya ce “kai jirin miye kuke dasu, ku kashe kowa amma banda wannan y’ar shilar, da ita zamu tafi sana ku koro shanayensu gabad’aya”

Kamin ya rufe baki ma, wani ya sakarma Usman harsashi a tsakiyar kansa, nan take ya zube babu rai a tare dashi. “wayyo Allah na shiga uku na lalace sun kashe mana Y Usman wayyo Allah Inna kin gani”

Cewar Fulani da gabad’aya ta fice daga yaccinta. Wata gigitacciyar tsawa suka bugama Fulani wacce tasa tayi suman wucin gadi ba shiri ta had’e maganar dake bakinta. Kamin ta dawo duniyar mutane taji k’arar sukar harsashi guda biyu. Wata irin k’ara ta fasa, ganin Inna Wuro ce da Audu aka harba gashu nan yashe a k’asa babu lumfashi.

A lokacin itama da za’a d’au rayuwarta itama da zata so haka. Tashi kawai tayi tana matsawa kan gawar Inna Wuro, sai da ta tab’a fuskarta ta k’ara tab’awa, ganin fa babu rai a tare da ita, yasa kawaii Fulani fad’awa kanta ta fashe da wani irin kuka, mai matuk’ar ban tausayi. Kuka take tana surutai wadda basu da kan gado. Tashi ta sake yi ta matsa kan gawar Usman shima, maganar take tunawa inda yake cewa “ki daina kuka haka nan kinji, baga mu ba tare da ke, kuma zamu ci gaba da kasancewa a tare da ke”

“Wayyo Allah na Y Usman ina al’k’awarin da kayi min na kasancewarku tare dani har abada, ya zakuyi min haka?, ya zaku tafi ku barni cikin wannan duniyar mai d’auke da azzalumai, dan Allah nima ku kashe ni”. Ta Idasa maganar tana duban wani daga cikin y’an Ta’addar dake tsare da ita sauran sunje koro shanayensu.

Wani abu Fulani ta tuna da sauri tayi cikin d’aki, d’an Ta’addar harya saita bakin Bindigarsa zai sakar mata ita, kawai yaji wani ya ce “kyale ta dole dai sai ta bimu tunda Oga ya ce banda y’an mata irinta, su a taho dasu kawaii yake so”.

Fulani kayan Mahaifiyarta ta d’akko ta k’udundune su a mararta sark’ar kuwa, a cikin gashin kanta ta sata ta d’aureta, sosai yadda ba wadda zai ganta, kuma bazata tab’a fad’u ba.

Wani ne yaje har d’akin ya janyota ya tasa keyarta a gaba yana dungurinta da bindiga yana zaginta, suka fito waje, a yanzu kam Fulani zuciyarta ta bushe sai kallon gidan take had’e da kallon gawar su Inna, a cikin zuciyarta wani irin rad’ad’i mai azabar zafi take ji, a yanzu kam sai had’iyer zuciya take, idonta sunyi jawur.

<< Kaddarar So 4Kaddarar So 6 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×