Skip to content
Part 21 of 26 in the Series Kauthar by Jeeddah

Kamar wata barauniya, haka ta bude kofar dakin. Kai ta zura a hankali, a ranta tana addu’ar Allah Yasa ya riga yayi barci yadda zata sadada ta kwanta ba tare daya san da zuwanta ba.

Cikin rashin sa’a sai suka hada ido dashi. Zaune yake akan kujera yana sipping din green tea, da jarida a hannunshi yana karantawa. Ya daga kai yana kallonta.

Bata da zabi wanda ya wuce ta karasa jan jikinta ta shiga dakin tare da maida kofar ta rufe.

Ta ki yarda su hada ido dashi. Ta taka a hankali kamar mai tsoron taka kasa har zuwa bakin gado. Tana jin yadda ya bita da kallo, amma ta maze ta ki bari yayi affecting dinta.

Inda ta kwanta jiya nan ta kwanta har da hadawa da jera pillow ma a tsakaninsu. Ta ja bargo ta rufe jikinta har ka.

Tana jinshi yana motsi da matsawa daga nan zuwa can, amma ta kasa yin motsin kirki.
Har dai daga karshe ta ga dakin ya kara duhu alamun ya kashe wuta. Tana jin lokacin da ya hau kan gadon ya kwanta. Jiya dai ko kallon bangaren da take bai yi ba. Duk da sanin hakan da tayi, sai taji gabanta yana tsananta faduwa.

Sautin ya karu sosai lokacin da taji yana janye filullukan data jera, ya matsa zuwa inda take. A tausashe ya sanya hannu ya janye bargon data rufa, ya juyata ta kwanta a bayanta, suna kallon-kallo ta cikin dan hasken daya rage a dakin.

Wani irin taushi ne da tausasawa a cikin kallon nashi wanda ta kasa jurewa gani, hakan yasa tayi gefe daya da kanta.

Ya sanya hannu ya kama habarta ya kara dago da fuskarta. A hankali, kamar mai rada ya daga baki ya furta sunanta, “Kauthar!”

Wani yarrr! taji tun daga kanta har zuwa tafin kafarta, musamman hannunshi dake habarta daya fara shafar wuyanta a hankali zuwa gefen kunnenta…

Ya sake ambatar sunanta, “Kauthar!!”

Gabadaya ta rasa kuzarin amsawa, sai sautin “uhhmmm?!” daya fita da kyar daga can makoshinta.

Ya kara yin kasa da kanshi saitin fuskarta, idanunshi akan lebunanta dake motsawa a hankali cikin rashin sanin abinda zata ce, kamshin mouth wash da tayi amfani dashi yana dukan hancinshi. Ji yake kamar ya kama leben da harshen duka yayi ta tsotsa.
Amma sanin halin Kauthar, yadda take kamar yar mage sabuwar haihuwa, wadda zaka dauki lokaci mai tsayi kafin ka saba dasu, kuma da ka danyi kuskure daya su manta da wannan sabon, yasan dan cigaban da suka samu a yan kwanakin, komawa baya zai yi.

Amma duk yadda ya dinga son tausar zuciyarshi akan aikata hakan, ya gagara.

Fuzgarshi take kamar wani maganadisu da karfe. Kasa ya fara yi da kanshi.

Gabadaya komi ya cukurkude mata, ya’yan hanjinta suna wani juyawa da cakudawa, zuciyarta na gudu na fitar hankali. Ji take kamar zata tsaga kirjinta ta fita.

Ta zabura ta tashi zaune a sukwane, ta juya mishi baya, kafafunta suna zurawa kasan gadon. Ji take kamar ace arr! ta dafe keya ta falla da gudu. Numfashi take fiddawa a sukwane, tana kokarin saisaita bugun zuciyarta.

Ya kara bi ta bayanta ya rungumota, hannunshi daya dauki dumi ya dora akan ruwan cikinta, sai data zabura tana girgije jikinta kamar wadda wani kwari ya taba.

Ya dora bakinshi a saitin kunnenta na dama, kasumbarshi da saje suna mata waiwayi a wuya da gefen fuska. Wani irin numfashi irin na wanda ya wahaltu yake furzarwa, ya fada ya kara fada, amma ji yake kamar hakan bai wadatar ba, kuma ba zai isa ba. Don kuwa yasan kalma ba zata taba iya bayyana irin tsantsar so da kauna da yake yiwa Kauthar a cikin ranshi.

“I love you Kauthar! Really love you!!”

Ya furta mata hakan a hankali, murya a tausashe, wadda take nuna gaskiyar abinda yake fada tun daga kasan zuciyarshi har zuwa bakinshi.

Bai tsaya jiran amsarta ba ya cigaba, “ina miki son da nasan baki ko kalma ba zai iya furtawa ba Kauthar. Sonki ni nasan doriya ce kawai daga Allah, na kuma san duk duniya babu wani mahaluki da zai iya yi miki wannan son. Babu kuma wani abu wani, ko wani mutum da zai sa sonki ya ragu a cikin raina Kauthar, sai dai ma ya karu. Ina sonki, ina girmamaki, ina…!”

Ba zata taba iya jurewa jin irin wadannan kalamai daga bakin AbdulMalik ba. Idan ma aurensu da shi ba haramun bane, tuni gangar jikinta ta haramta hakan. kunnuwa sun haramta sauraren kalaman so, baki ba zai taba iya furta kalmar so ba! Wannan a tun lokacin da ta dalilin Anty Ummy ne kawai. To yanzu kuma ga wata mas’alar ta mahaifiyarta. Abinda ta aikata ga mahaifin AbdulMalik din. Duk da dai mahaifinshi ne, amma ai ya shafesu su duka.

Cikin sanyin jiki da tsananin cushewar da kwalwarta tayi har tana neman sanya mata ciwon kai, ta kai hannu tana zame aids dinta daga kunnenta. Gwara kawai ta daina saurarenshi ma gabadaya.

Haske taga ya mamaye dakin, ya sanya hannu ya juyata suna fuskantar juna.

Hannu ya daga, kamar a almara taga ya fara sign language. Daskarewa tayi a zaune tana kallonshi bakinta a dage.

Cewa yayi, *”ki daina guje min Kauthar, ki daina ja baya dani, ki daina janye jikinki daga gareni a yayin da nake kusantoki. Idan ban rabeki ba, wa kike so in raba ne inji dadi a duniyar nan? Ke kadai gareni, ke kadai ce a cikin raina, ke kadai kike kwana ki yini kina yawo a cikin raina. Na fara kai matakin da ba zan iya cigaba da jure wannan abin ba Kauthar! Me na roka a wajenki? Rabi-rabin son da nake miki kadai nace ki dawo min dashi, a ganina hakan ai ba wani abu bane mai wuya!”

Ya karasa hannunshi yana dan rawa, ya maidashi ya ajiye akan cinyarshi ya kife, shima nashi kan a kasa in defeat.

Kwalla ta cika mata ido, ace she was overwhelmed ma bata baki ne, abu ya tokare mata makoshi. Ta dinga hadiyar yawu har ta samu ta iya hadiyeshi da kyar, sai kuma ga kukan da take dannewa ya zo.

Ta kai hannu ta rufe fuskarta tana sakin kukan mai tsuma zuciyar mai saurare. Ace wai a duniya akwai wanda zai sota irin son da AbdulMalik yake mata? Son da har zai yi sanadin rufe mishi ido akan komi da kowa, da duk abubuwan da mahaifiyarta ta aikata a garesu? Har ya tafi ya koyi yaren da tana da tabbacin ko mahaifin daya haifeta ba zai iya zuwa to that extend ba?!

Hannuwanta ya kamo cikin nashi masu taushi da dumi, ya kalmashe su yana kallonta cike da tausayawa. Magana yake, amma bata jin sa sai kalmomi kadan-kadan da take tsinta, ta kuma kasa kallon bakinshi balle ta karanta abinda yake fada.

Ya dauko aids din da hannunshi ya mika mata. Ta amsa a sanyaye tana sanyawa, yayin daya sanya tafukan hannayenshi yana goge mata hawayen dake ambaliya a fuskarta.

Kallonshi take kasa-kasa har ya gama share mata hawayen. Ya kara gyara zama yana kallonta.

“Meye matsalarki Kauthar? Me kike ki a tattare dani? Me kike so in canza wanda ba kya so a tattare dani?”

Ta hau girgiza kai a tausashe, “Anty Ummy….!”

Shima ya tareta da girgiza nashi kan.

Ta kara daga baki cikin wata irin shagwaba da bata taba sanin tana da ita ba, “kuma Mommyna…!”

Yatsarshi manuniya ya sanya yana dafe lebenta yana cigaba da girgiza kanshi dai.
“Ni wai menene nawa a cikin wannan maganar? Rigimar iyayenmu tasu ce, babu ruwana a ciki. Sannan wanda ta aikatawa hakan bai damu ba, hasalima ya bude bakinshi yace ya yafe mata duniya da lahira, kudi kuma ko ta dawo dasu ya bar mata, nata ne. Ni ban taba rikonta ba, in fact, ni tuni na ma manta da abinda ya faru. Kema kuma don Allah ki manta da abinda ya faru…”

Ya sanya hannu ya kamo habarta yana kallon tsakiyar idanunta, “ni saboda ke, zan iya rasa komi nawa Kauthar, I don’t care…”

Ya fara matsawa da fuskarshi zuwa gareta yana furta, “I wouldn’t care…!”

Da haka ya hade bakinsu cikin wani irin kiss daya kidimata. Bata san lokacin data kamo gefen rigarshi ba dai-dai saitin zuciyarshi ta jimke. Hakan yasa ya kara kaimi, ya kwantar da ita, ya bita da runguma mai tsauri, ji yake kamar ya ma hadiyeta ta koma cikin jikinshi kawai ko ya huta ma.

Ganin abin nashi yana neman wuce gona da iri yasa tayi kokari ta janye jikinta. Don kuwa taga alamun idan ba hakan tayi ba, zai iya kaita garin da bata yi niyar zuwa ba.
Ya kife a jikinta yana nutsa kanshi a wuyanta yana shakar kamshin da jikinta ke fitarwa mai dadi har ya samu ya kamo zaren nutsuwarshi.

Sakinta yayi ya tashi zaune yana kallonta yana sakin wani miskilin murmushi, “babu abinda zan miki yar gaban goshin Antynta! Ni ai ba zan ballowa kaina ruwa ba a gaban babbar Anty!”

Da sauri ta ja filo ta rufe kanta da filo tana furta “kai ko!”

Ya saki wata irin dariya data fita daga can karkashin zuciyarshi cikin wani irin nishadi da farinciki irin wanda ya jima bai ji irinshi ba. Shima binta yayi ya kwanta, janye filon data rufe fuskarta dashi yayi, yayi matashin kai dashi don ma kada ta kara janyewa.

Ya lumshe ido yana sakin dan murmushi, yace, “ni ina da yakinin a duk inda Fahima take, tana binmu da fatan alkhairi da addu’a. Kauthar, nasan ko tana raye, wallahi babu wanda zai so aurenmu dake a duk duniyar nan fiye da ita. Kuma ko a wancan lokacin na tabbata, duk guje-gujen da kike yi na baki sona da waye da waye, nasan dan takaitaccen lokacine kawai ya rage, zata kamo min hannunki ta kawo min ke har gidana a matsayin mata!”

Tayi shiru kawai kanta a kasa, cike da matsananciyar kewar wannan baiwar Allah. Ta kuma yarda har cikin zuciyarta, maganganunshi haka suke babu ko digon ba dai-dai ba.

Shima yayi shiru cikin sanyin jiki da kewar, ya kalleta tana share wasu sabin hawayen, “Allah Ya jikan Fahima! Allah Yayi mata rahama! She was such a wonderful and pure hearted person. Allah Yayi mata kyakkyawan masauki a gidan aljannah!!”

Cikin karyewar murya da kokarin boye kukanta tace, “Ameen!”

Ya jawota ya sanyata cikin jikinshi yana rarrashinta har tayi shiru.

Ranar dai sunyi abinda suka jima basu yi ba, suka raba dare suna hira suna tuna da. Ranar kuwa har sai da suka so su makara sallar asubahi.

Tashi tayi jikinta da alamun zazzabi. Ta sha magani ta koma ta dan kwanta har ya sauka saboda bata son nunawa su Lukman rashin jin dadin jikin nata.

Tayi wanka ta shirya cikin wata abaya navy blue, tayi nadi irin na mutanen kasar Lebanon, sai ta fito kamar irin bakaken larabawan nan.

A wajen kari da suka hadu su kansu yan kannen nata sai da suka yaba kwalliyar tata. Shi kuwa gogan ya buge da satar kallonta ba damar ya daga baki ya yabeta a gaban Anty Aisha.

Haka suka yi karin ita da su Lukman suna ta hirarrakinsu. Sama-sama ta ci abincin saboda rashin karfin jikin da take ji.

Ranar a motar AbdulMalik suka fita su duka. Ya kaisu gidan Aunt Halima suka yini a can, bayan anyi Azzuhur yaje ya daukesu ya kaisu shopping mall suka jidi tarkacen kaya kamar me.

Da suka koma gida, shirin kayansu suka fara yi duk da cewa dama ba wani tarkace ne dasu ba.

Ta dauko musu akwatin data musu tsarabarshi ta damka musu.

Anty Aisha ta dinga bi tayi rau-rau da idanu tana shirin kuka. Ta kalleta tana dan murmushi, “babu fa abinda zai hanamu komawa gida yau Kauthar, don haka ki ma share hawayen nan naki. Kiyi saving dinshi for later sai ki yiwa mijinki!”

Ta hau dira kafafu a kasa tana neman sa mata kuka, ita kuwa sai ta yi yar dariya tana girgiza kai, tace, “lallai Kauthar, da sauranki ashe!” ta cigaba da tattara nata-i-nata.

Su suka musu rakiya har airport. Suna zaune a dakin jira kafin a kai ga kiran jirginsu, tana zaune a gefen Anty Aisha wadda take kara nusar da ita akan zaman aure da rayuwa a karan kanta, su Lukman kuma suna gefe da AbdulMalik.

Anty Aisha ke ce mata, “ita rayuwa musamman ta ya mace kalubale ce. Kin tashi a gaban iyayenki, a karkashinsu da kulawarsu, idan basu raye to zai zamana kina hannun wani kawunki ne ko kuma yayanki. Sai kiga har mutane suna yiwa wadanda suka tashi a hannun mahaifiyarsu kadai wani kallo-kallo. To wannan kadai idan kika yi duba sai kiga cewa ai ita mace gidan mijinta dana iyayenta shine martabarta. Idan Allah Ya bata iko ta rabu da iyayenta lafiya har suka damkata a hannun miji, kinga sai tayi kokari ta daure, ta jajirce tayi mishi biyayya irin wadda Allah da mansonSa suka ce ayi, kin gane?”

Kauthar ta gyada mata kai a sanyaye.

Tayi dan murmushi, “yauwa, to kinga a halin yanzu, babu wani abu da yafi miki muhimmanci Kauthar, irin aurenki da mijinki. Na sanshi, nasan yadda ya rike min Fahima cikin tsoron Allah da tattali da kulawa, na kuma san kema zai kula dake din ninkin-ba-ninkin. Idan kinyi hakuri akan kananun abubuwa da zasu faru wadanda dole ne faruwarsu, sai ki sameshi shi kuma yana yin hakuri dake akan manya-manyan abubuwa. Saboda ita rayuwar gabadayanta akan hakuri aka ginata. Idan kinyi hakurin sai kiga komi daren dadewa, kin duba baya kinji dadin hakurin da kika yi. Kina fahimtata?”

Nan ma ta sake gyada kai.

Anty Aisha taci gaba, “sai kuma juriya akan bukatun miji na yau da gobe. Tsaftar jiki da kayanki da nashi da gidanku. Kada kice zaki yi ganda akan hidimar miji, tana ragewa mace kuma a idon mijinta kwarai da gaske. Kada ki taba nuna mishi gajiyarki akan hakkinshi dake rataye a kanki Kauthar. Ki kuma kasance mai yawan kawaici da kawar da kai akan al’amuranshi, kada ki cika mishi shisshigi akan abubuwanshi, ki girmama mishi iyaye da yan’uwa da dangi kuma suma kiyi hakuri dasu. Ina ga idan kin riki wadannan abubuwa da kyau, in shaa Allahu zaki ga haske a rayuwar aurenku. Allah Yayi muku albarka, Ya albarkaci rayuwar aurenku da zuriyarku!!”

Da wadannan kyawawan kalamai da shawarwari suka rabu da ita. Ta kuma yi mata alkawarin zuwa Abuja nan ba da dadewa ba.

Tsananin kawar da kai ya hanata tambayar inda mahaifiyarta take, sai da zasu rabu ta ciro farar envelope daga jakarta ta mika mata. Koda bata ce komi ba, ta fahimta. Ta amsa tana mai furta mata ‘thank you!’

Tana tsaye har suka shige ta daina ganinsu.

Ta juya tana fuskantar AbdulMalik din, wanda ya dan juya musu baya yadda zasu yi sallama a nutse. Ya matsa ya kama hannunta cikin nashi ya jata har zuwa wajen daya ajiye motarshi.

Har suka isa gida babu wanda ya cewa dayansu kala. Da hannu daya ya dinga tukin, saboda ya ki sakar mata hannu daya kama ya rike sai kace dole. Yana yin parking, ta zame hannunta ta wuce ciki cikin sanyin jiki, dakinta ta shige kai tsaye. Shima kuma daya shiga sai bai takura mata ba. Ya wuce study room dinshi inda yake rage ayyukan ofis, ya kama aiki.

Bata warware ba sai da suka kirata waya sun isa gida lafiya, suka bata awa guda suna hira dasu Mahmoud, sannan ne taji dan dama-dama.

Faten Irish aka musu da dare, da grilled salmon wanda yaji cheese da salad. Su dukansu sun yi mata dadi sosai, ta bude ciki ta ci har sai daya cika mata ciki. Ta ture plate din kifin gefe guda tana shafa cikinta da taji ya cika taff.

Kallonta kawai yake cikin dan murmushi, yayinda yake cin nashi abincin a nutse.

Duk da cikinta ya cika bata tashi ba, ta zauna tana kallon -The Meg- da ake nunawa a tashar mbc 2.

Ya kalleta yana cigaba da murmushi lokacin daya gama cin nashi abincin, “hala yau anan zaki kwana ko? Ko kuwa kifin ne bai isa ba, a karo miki?”

Ta dan kama baki, “lallai ma, in dai ba so kake cikina ya fashe ba don cika ai ba zaka kara min abinci ba yanzu!”

Yayi dariya kawai ba tare da yace wani abu ba. Hannuwanta biyu ya kama yana mikar da ita tsaye, “oya, tashi to ayi haramar barci tunda dare yayi.”

Kokarin zame hannunta take yi amma ya ki bata damar hakan, sai daya kaita har kofar dakinta, ya bude mata kofar tare dayi mata alamun ta shiga sannan ya saketa.

Ta rufe kofar tare da komawa ta jingina a jiki. Jikinta kamar wadda aka hadawa shocking haka take ji. Shi sam bai san har yanzu ta kasa sakin jiki dashi bane, har yanzu idan jikinshi ya rabu da nata ko yaya ne sai taji wani banbarakwai. Shi kuwa ta kula ko a jikinshi ma. Yan kwanakin kadai ta kula yana da son skin ship sosai da sosai. Bata tunanin zata iya sabawa da hakan.

Da tayi wanka ta gama shirin barci. Sai kawai ta dauki wayarta, ta kashe wutar dakin ta fita.

Data tsaya a kofar dakinshi tayi knocking, sai ta tsinci kanta da sakin dan murmushi. Tana tuna ranar farko data shiga dakin da yadda ta dinga ji, yanzu data duba sai taji bata jin wannan dar-dar din.

Jin shiru ba a daga ba ko an amsa mata, yasa ta tura kofar dakin a hankali.

Baya nan, amma ko’ina tas a gyare yake, sai kamshi mai dadi da sanyi da yake tashi.
Jin alamun motsin ruwa a bandaki yasa ta fahimci yana ciki, kila ko wanka yake yi ko wani abu. Ta kwanta akan gado ta bude wayarta tana dubawa har zuwa lokacin daya fito.

Kallo daya ta mishi, ta dauke kai da sauri. Daga shi sai dan karamin boxer iyaka gwiwarshi, sai towel karami a hannunshi.

Ta kashe wayar ma gabadaya ta juya ta daya gefen don ma kada ta dinga satar kallonshi.

Tana jinshi yana yan shafe-shafe da sauransu, bata san lokacin da barci ya fara daukarta ba.

Ta motsa a hankali jin ya hau kan gadon, tana jin sanda ya ja bargo ya rufe mata jiki kafin ya sumbaci goshinta da kan hancinta, sai ta tsinci kanta da sakin murmushi a cikin duhun dakin.

A ranta tana fadin, “maybe she could get use to this!”

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 3 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Kauthar 20Kauthar 22 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×