A daren da kyar Zayyan ya iya yayi barci saboda tunani, a karshe ya tabbatarwa kansa ya kuma gayawa kansa kara aure shi ne kadai solution na dukkan matsalolinsu shida Safiyyah ta kowanne bangare ya duba yaga hakan shine kadai maslaha.
Amma daga bangaren ita Safiyyah shin hakan zai zamo solution a gareta? Kuma ta wace hanya zai bi ya gaya mata yau shi Zayyan ya ga wata mace daban a duniya bayan ita ya kalla sai biyu, kuma yana so zai aura ya hada da ita? Duk da cewa ba haramun zai aikata ba, kuma bai taba yi wa. . .