Bugu ɗaya aka ɗauka da sallama
Bai amsa sallamar ba ya zarce da cewa “ Barka da dare Alhaji ”.
“Yauwa barkanmu juna da wa nake magana ”
“Sunana fahat na kiraka ne akan maganar Faisal muna nan ya sakamu acikin tashin hankali wata yarinya ya ɗauko yana ƙoƙarin keta haddinta, iyayen yarinyar sunzo harda ƴan sanda sai ya sakar mana karnuka, shine nace bari na sanar da kai kazo ka dakatar da shi don mudai mun rasa mafita.
“Subhanallah shi Faisal ɗin ne yake ƙoƙarin aikata wannan mummunan aikin, kuna ta ina ne yanzu? "..
“Gate hause ɗinsa na barrack road. . .