"Ran ki ya dade...ma..za maza ki bude gidan Radion haske shirin nan na siyasa a yau! Akwai wani mugun labari akan ki! Ya kamata ki tari abun!"
Cikin rawar jiki ta yi amfani da wayarta ta kunna. Wasu irin maganganu ne suka dira a kunneta
" Kamar yadda na ce da ku sunana Nadiya. Ni diya ce ga Lubabatu Hamza Mai Dala. An haifeni ne ba tare da Uba ba. Uwa ta Lubabatu ita ta haifeni a saudiyya a garin Jedda wata unguwa mai suna Karantina.
Wadanda suka tsince ni sun ce sun tsinceni ne a bola ko cibiya. . .