Skip to content
Part 8 of 18 in the Series Warwara by Haiman Raees

Makiyana

Allah Kai ne Ka yi kowa,

Da sunanKa zan farawa,

Albarkacin shugaban kowa,

Annabi Jagoran Annabawa.

*****

Allah Kai ke da kowa,

Kai min ni’ima ina godewa,

Kamar yadda Ka yi wa kowa,

Ka tsare autan Hauwa.

*****

Tun fari dai da farawa,

Ka duba cikin Larabawa,

Ko su cikin Yahudawa,

Ko kuma cikinmu Hausawa.

*****

Babu tantama a Yarbawa,

Kai har da su Jamusawa,

Duba cikin Amurkawa,

Maƙiya kamar saukar tsawa.

*****

Ko me ka ke yi Malam,

Magana ka ke yi ko gwalam,

Noma ka ke yi ko kwaram,

Maƙiya ba za ka rasa ba.

*****

Nima akwai su a gabana,

Na baro wasu a bayana,

Ga wasu nan a dama na,

Ga wasu kuma a hagu na.

*****

Rayuwar kenan ba ba ƙari,

Jira suke yi na yo tari,

Yanzu-yanzu su yo ƙari,

Su je su ce n kashe ƙwari.

*****

Komai na yi ban burge ba,

Alherin ba za su gani ba,

Kuskure ba za su ƙi gani ba,

Sharri ba za su ji nauyi ba.

*****

Allahu Kai je jigona,

Sannan kuma Kai ne gata na,

Kare ni da ahalina,

Daga sharrin duk maƙiyana.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Warwara 7Warwara 9 >>

2 thoughts on “Warwara 8”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.