"Ayya..."
Bilal ya kira yana sa ta raba idanuwanta da inda yake tsaye tana kallon Rayyan daya daga mata kai yana tabbatar mata da yaji kiran, ba kunnuwanta bane kawai suka ji cewa Bilal ba tsaye kawai yake a cikin dakin ba, har magana yakeyi. Hankalinta ta sake mayarwa kan shi tana ganin yanda yake takawa yana karasawa inda take kamar wanda yake koyon tafiya, da duk takun da zaiyi da yanda zuciyarta take kara dokawa a cikin kirjinta da wani irin tsoro, sai dai kamar jira kawai yake ya karasa inda take kafafuwan shi su kasa daukar shi dan. . .
Ban taba karanta littafi mai storyline Irin wannan ba, I don’t even know how to express how I felt reading this book, it was all sort of emotion. Masha Allah it ended well, jazakillah khairan