"Kar in kara jin ance an ganki da Datti..."Kashedin da Babanta yayi mata yana dawo mata yana kuma saka zuciyar ta dokawa a cikin kirjinta a lokacin da take tsaye tare da Dattin, yana mata murmushin shi da zaka hango kyallin shi har cikin idanuwan shi da wahala bata saka su yin ja, ko ita ta samu kyawu da hasken idanuwan shi tana so.
"Wahalar mu ta zo karshe Dije, na samo mana wanda zai aure ki ya sakomun ke bayan wata daya...anjima zai zo wajen ki, gobe sai yaje wajen Baba..."
Ya karasa maganar fara'ar shi. . .
Nice