Kwana biyu da Baba ya bata wasiƙun da Mamanta ta bar mata guda biyu kafin rasuwarta. Kwana biyu da hargitsewar komai na rayuwarta.
Kwana biyu da sanin wacece ita. Tayi kuka kamar ranta zai fita. Kukan da babu wanda ya lallashe ta banda Yaya Musty. Babu wanda ya damu da tana yi banda shi da Baba.
Ranar ta lallaɓa ta je makaranta, tana aji shida. Tana dawowa ta ga su Hauwa na tsaitsaye a ƙofar gida ita da Fadil suna kuka. Tun kafin tasan abinda ke faruwa ta ƙarasa wajen su hawaye na cika mata idanuwa.
"Hauwa me. . .