Skip to content
Part 12 of 73 in the Series Sakacin Waye? by Sumayyah Abdulkadir Takori

Abba yana gama fadin haka shi da Anti suka tashi suka hau sama. Ya zama daga ni sai Ya Omar don Maryam Jamila ma ta sauka daga jiki na ta bi bayan Anti, daga ni har shi kan mu na sunkuye don ji nayi kamar Abba ya dora min dutsen Uhudu a kai na, ya daddaure ni da kalaman sa.

Umar kuwa tunanin sa daban ne da nawa wanda daga shi sai Ubangijin sa suka sani. Ba yau ya fara jin na ce ina son wani daban ba shi ba, karewa ma ya riga kowa ji tun ina fifteen years a Mambila ranar da muka je tebirin Garba mai shayi kuma tun a ranar yake jin ciwon abun a ran sa amma yau da Abba ya sake fade har yana rokon shi yayi hakuri da ni zamu daidaita a hankali kuma kaman by force zai aura masa ni sai ya ji kansa a mara sa’a, kuma mara abinda mace zata so.

Dacin hakan da ya ji a ran sa ne ya sanya shi saurin dago kai ya dube ni da idanun da suka kada, ya ce “Boddo feel free with me, it’s your Ya Omar, I know you don’t love me but please….. don’t hate me because of him, I beg you.

Ni na san I’m a loser, na sani amma ki kwantar da hankalin ki da yardar Allah in har ina raye ba zan bari Abba yayi miki auren dole ba.”

Ya karasa maganar cikin shakewar sauti, in ya tuna shi Boddo ta ke kiran auren sa na dole, kamar tana masa kallon matsala a rayuwar ta.

Na wani irin dago cikin slow motion na dubi Ya Omar, jijiyoyin kan sa sun fito rada-rada abinki da farin mutum idanun sa sun kada, ban taba ganin sa cikin kwatankwacin irin wannan yanayin ba.

Sai na ji duk wani guilty conscience na duniya ya rufto a kaina ya danne ni, anya abinda nake shirin yiwa Abba da Omar a kan wani da ban sani ba, bani ma da tabbas a kan sa daidai ne? Anya ba zan yi SAKACIN da zan zo na kasa gyarawa ba?”

“Ya Umar ban taba kin ka ba wallahi ka yarda da ni, ban taba alaqanta aure a tsakanin mu bane, ban taba baka matsayin ka mijin aure ba sabida na fi so kaci gaba da zame min bango abin jingina, wanda in mijin ya bata min wajen ka zan zo. I only love you as a brother not as a husband, I’m sorry Ya Umar, i’m very sorry.

I know it will hurt but you don’t know how much it deeply hurts the culprit (na san abin da ciwo amma kada ka so tona yadda yafi zama ciwo ga wanda ta aikata), na sani Ya Omar ko da aure ko babu you will stand by me, ka taimaka min in nemo shi bani da idea.

I may sound selfish but that is the bitter truth, my own fate, da iyakacin gaskiya ta nake magana. Babu gurbin kowa na soyayya a zuciya ta sai nasa.

Ba lokaci daya na soma son sa ba, na so shi ne tun ban san son sa na ke ba. Dare da rana yana hunting dreams dina da duk wani sako na zuciya ta cikin shekaru bakwai, alhalin kuma ban san shi ba, ban san inda zan gan shi ba…

Yet I’m craving for him!”

Na kifa kaina a kan teburin cin abincin na shiga rera kuka mai sauti. Jikin Umar har bari yake yi ya matso gabana ya dago ni, bansan ya aka yi ya aka yi ba, na samu kaina da fadawa jikin sa na rungume shi tsam-tsam, ina kuka ina kuma bashi hakuri.

Omar suman zaune yayi don wannan ne karo na farko da hakan ta faru tsakanin sa da Boddo tun balagar su. Irin reaction din da jikin sa ya dauka ya tabbatar masa yana son Boddo, so na hakika pure and real, ba irin wanda ita take masa ba, yana kuma kaunar zamowar ta mata agare shi uwar ‘ya’yan sa amma kash!

Ga abinda ke fita daga bakin ta a kan waninsa, Boddon da tun haihuwar ta ya ke son Mun jima a haka kafin Ya Omar yayi ta maza ya raba ni da jikin sa, yasa hankicin sa yana share min fuska ya ce “Alright Boddo, na fahimta ki daina kuka ki kuma kwantar da hankalin ki bazan biyewa Abba in aure ki dole ba, zan sama mana solution wanda bazai yi fushi da ke ba.

Amma lamarin naki is too complicated Boddo, ko ina son in taimaka miki din ban san ta ina zan fara ba, yau da ace kin san mutumin nan ne kuma kinsan inda yake, sannan kuma shima yana son ki it will be fine, but na kasa gane maganganun ki na baki san shi ba baki taba ganin shi ba sai a mafarki this is unblievable!

Ina so in taimaka miki amma ban san ta ina zan taimaka miki ba tunda bazan iya shiga cikin mafarkin ki in gan shi in yi magana da shi ba? I wish he’s real (na yi fatan ace akwai shi a gaske) da sai inda karfi na ya kare wajen lallashin Abba…”

“Wallahi a raye ya ke Ya Omar, kuma mutum ne kamar kowa, ka bani lokaci zan nemo shi, in dai zaka cika alkawarin ka na rarrashin Abba, da kunnuwa na naji muryar sa a radio bayan na mafarki”

“Radio?”

Omar ya tambaya cikin kakabi na mamaki da tunanin Boddo soyayyar gaibu ta sa ta zare. “Kuma sai aka ce miki shine na cikin mafarkin ki? Wahayi aka yi miki ko me?”

A wannan gejin na fara tunzura da tambayoyin da yake min masu son tabbatar da cikakken hankali na. Amma na san Omar yana nufin taimaka min da gaske, don haka na sassauta zuciyata na labarta masa abinda ya faru ranar, da Rukiyyar Aljanu da Anti tasa Abba yasa aka yi min.”

Duk halin da Ya Omar ke ciki saida yayi dariya yace “Boddo yanzu ta ina zamu fara neman Mr Radio?”

Na harare shi don ganin shikuma hauka zai lankaya min, nace “in da gaske kake zaka taimake ni ne Ya Omar to mu fara zaga gidajen Radiyon Abuja, kuma ka tambayi Abba wace tasha yake saurare ranar da na fadi musu? Na rantse maka idan na ganshi daga ganin farko zan gane shi, da jin muryar sa zan shaida ta”. Omar ya rufe fuska da tafukan sa yana murmushi mai ciwo, yace “a sa cewa mun same shi a gidajen rediyon da zamu je din, a sa cewa kin gane shi, sai mu ce masa me Boddo?

Mr. Radio ka zo ka auri Boddo tana mafarkin ka tana son ka? Kin wuce nan Boddo, a matsayin ki na bafullatanar Mambillah.

Ba kya tunanin hakan zubar da kimar ki ne ta diya mace mai darajar fulanin Mambilla, jikar Malam Dalhatu Gembu da Saudatu Ummatin Mambilla? Idan Ummati taji kin je nemowa kan ki miji a kan titin gidajen radiyo ba kya tunanin bafullatanar zuciyar ta zata iya bugawa da bakin cikin ki, don kuwa Ummati bata daukar abin kunya da zubda kima akan jinin ta.

Idan zan baki shawara ki dauka kada ki taba attempting neman sa a ko’ina. Ki koyi hakuri a kan soyayya ki kuma koyi juriya. Don na fahimci your love for him is extremely hot. (Soyayya mai zafi kike masa). Kisa a ran ki idan mijin ki ne kina zaune Allah zai jefo miki shi daga duk inda yake, idan Allah ya nufa ba mijin ki bane Boddo soyayya bata kisa, why not ni ki aure ni give it a try, nawa son will be enoughfor all of us mu raba ni da ke, bana bukatar martanin soyayyah daga gare ki, ba kuma jikin ki nake so ba. I will only love you Boddo till eternity and actualize my love alone!!”

Kuka na saka wiwi, na sa yatsuna hagu da dama na toshe kunnuwa na ina cewa “Ya Omar babu wannan maganar a tsakanin mu. Ba zan iya ba, ba zan iya yaudarar ka ba, in na aure ka na kware ka ba zan taba baka soyayyar da kake bukata daga gare ni ba.”

“Shine ni kuma nace miki bana bukatar taki soyayyar, tawa ta ishe ni. Ba zan aure ki don in huta da ke ba, zan aure ki don mu cigaba da rayuwar mu tare yadda Abban mu yake buri, har zuwa lokacin da tunanin ki a kaina zai sauya, ki sammini gurbi komai kankantar sa daga gurbin Mr Radio, i will be glad and grateful.”

Umar ya daina bani mamaki ya koma bani tu’ajjibi da tausayi, jin na kasa magana ya kara durkusawa a gabana, ya dora tafin hannun sa saman kafata ta dama yace,

“kin amince ko Boddo?”

Idanun sa na pleading, pink fatar bakin sa na motsawa a hankali kamar ba daga bakin sa maganar ke fita ba.

“Zan yi kokari in sayawa kaina muhalli a zuciyar ki in muna tare, idan shi a mafarki yake nuna tasa soyayyar ni a zahiri zan nuna tawa. Shi matsoraci ne Boddo, raggo ne, tunda ya kasa bayyana kan sa, sai dai ya sadado ta cikin mafarki yana neman haukata ki.

Boddo nine Omar dan Asshe da Hassu, Dan Gidado da Mamman jikan Ummati, shin wannan kakkarfar alaqa bata yi isar da zaki duba ki sadaukar da soyayyar bare a kan ta ba?

Zan bar ki da wannan kiyi tunani a kai daga nan har zuwa ki gama jarrabawa, ba zan kara damun ki da wata magana da ta shafi wannan ba, don na fi so ki tara hankalin ki waje guda yanzu. Watanni uku sun ishe ki yanke mana hukunci, ni kuma duk abinda kika yanke insha Allah zan karba, zan kuma yi kokari Abba ma ya karba, zan yi amfani da karfin soyayyar da yake yi min wajen ganin kin samu duk abinda kike so.”

A wannan daren ko na minti goma ban iya na runtsa ba sai juyi a kan gado, ina tuna maganganun Ya Omar, hakika ina cikin rudani amma na kasa gane cewa mafita ta guda daya ce a daidai wannan gabar wato barwa Allah zabi. Na kasa tuna in tashi in gayawa Allah yayi min zabin alkhairi kada ya bar ni da dabarar kaina.

Nafi karkata ga son Ubangiji yayi gaggawar bayyana min shi kawai, idan har ya bayyana komai zai zo da sauki don Umar ba ya magana biyu, tunda ya ce zai lallasar min Abba to kuwa zai yin. Ya Omar zai sa Abba ya aura min shi, Anti zata sa Abba yayi hakuri ya aura ma Ya Omar wata daban ko a cikin dangi, bana son tuno ko daya cikin kalaman Omar domin kuka suke saka ni, a daren ranar ma da kuka mai tsanani muka rabu, ban iya na bashi amsa ba.

Washegari ban gan shi a gidan ba ban ji duriyar shi ba, haka na shirya na tafi makaranta duk jikina sukuku. Jarabawar ma ta yau na dai zana ta ne amma ni kaina nasan sunana loser. Har tsayin kwana uku ban kara ganin Umar ba, daga baya ne na ji Anti na waya da Anti Nasara wai ashe can ya tafi zai yi wata uku kafin ya dawo.

Ko meye hikimar Umar na kauracewa gidan mu? Wata zuciyar ta ce don ya baki dama kiyi karatu. A fili nace Allah sarki Ya Omar, ko kana nan ko baka nan wannan jarabawar ta tashi a banza. Sunanta Fatima Tara (F9×9).

Aka gama WAEC aka shiga NECO, a NECO ne kam Ko’oje ta ankarar da ni wai ina zana Radio akan answersheet dina na darasin lissafi. Da sauri na duba, kwarai Radio nake zanawa da sunayen gidajen Radio a Najeriya dana sani da manyan baki

Bayan mun fita paper din Ko’oje ta kamo ni kamar ta fashe da kuka,

“Aishatu Mamman Gembu me kika zamar da kan ki a kwanakin nan? Maths paper kike zanawa Radio? Meye gamin ki da Radio? Are you in your full senses? (Kina cikin cikakken hankalin ki)”

Kai tsaye na sunkuyar da kai nace “I’m in LOVE Ko’oje, sincerely in love, unimportant love kuma!”

Azima Salim Ko’oje ta kama hannaye na biyu ta rike gam cikin nata, ta ce “how did it become unimportant?””Sabida auren dole Abba na zai yi min da Ya Omar Azima, sun ki yarda mutum nake so dan Adamu da Hawwau, sun fi zaton na samu matsala ta aljanu ko ta kwakwalwa ne”.

“ni kuma na yarda da cewa kawata will never lose her sense because of a man, who is he? Who isthatLucky? Ki gayamin ko wanene? Shi din ya san kina son sa?”

“Bai sani ba Ko’oje, nikadai nake kida na nake taka rawa ta karewa ma ban san a inda yake ba””to meye alaqar sa da Radio da kike zanawa a mathematics answersheet?””He’s a Radio Presenter I guessed”. Ko’oje ta ware manyan idanun ta akai na tana kallo na “kika ce baki san shi ba, yaya akai kika san hakan to?”

“baiwar Allah ke lawyer ce ne?”

Dariya ta yi tace “kwarai shi nake fatan zama,ke kuwa gaki nan a kan yardstick na ruining future din ki gabadaya.”

Bude idanu na yi na dube ta sosai, sai tace “ban taba jin wannan almarar ta ki ba, wallahi na dauka saurayin yana tare dake, ko a gida ne ba’a yarda da shi ba. Shiyasa na tsaya ina sauraron ki. Ashe ke you are just on delusions and illusions.

Kafin ya zama worse zan gayawa Anti ta kai ki asibiti a dauki matakin gaggawa, sannan next year ki sake papers din ki.”

A fusace na tafi na bar ta tana kiran sunana amma ban ko juyo ba. Na yi tafiya mai dan nisa kafin in zauna akan wani kututturen icce in yi kuka na mai isata. Ko’oje is my last hope, amma kalla….itama yanzu tace delusion nake yi har ina ina hadawa da hallucinations.

Ni na san kaina, kuma a dan ilmin da Allah ya bani na san lafiya ta kalau, kawai kalar tawa jarrabawar kenan, ko kuwa kaddarar rayuwata da ya barranta da na kowacce mace. Ni a mafarki da kuma imaginations nake tawa soyayyar.

Our own love tragedy is unbelievable ga kowanne mai hankali.

Ji nayi ana yimin horn, sai na daga idanuna jage – jage da hawaye na dubi inda motar ke tsaye, Anti ce ta zo dauka na da kanta yau don na gaya mata paper daya kawai zan yi.

Tare da Ko’oje na gan su a tsaye can gefen motar suna magana, suna kuma kallo ni da tausayi a fuskokin su. Mikewa nayi na isa ga motar na shige Anti tayi sallama da Azima ta ja motar bayan ta dora min Nadia a cinya ta. Muka kama hanyar gida daga Mabushi.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 4 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Sakacin Waye? 11Sakacin Waye? 13 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×