Skip to content
Part 38 of 73 in the Series Sakacin Waye? by Sumayyah Abdulkadir Takori

Ni na san na so Hamzah Mawonmase mafificin SO, na so komai nasa, na yi burin kasancewar mu miji da mata a darare da dama da yawan su ba zai lissafu ba, kuma na sha yin mafarkai barkatai kwatankwacin irin wadannan masu kama da ido biyu, amma na yau special ne, wato (na musamman ne) yayi matukar bambanta dana cikin mafarkai na, kasancewar na yau a zahiri yake gudana, wato zallar reality ne mai sarrafa kan sa da kan sa….yake kuma tafiya (hand in hand) da karfin soyayyar da ke

zuciyar Hamzah…

Na ji ni tamkar ina shawagi a kan gajimare, Hamzah ya dauke ni ya kai ni wata duniya ta daban ba wannan tamun wadda muke ciki ba, duniya ta extreme ecstasy. Wani irin scene ne ya shiga gudana wanda har abada ba zai gushe daga zuciya ta ba. Ya sumbace ni a fuska, a wuya, a ido, ya kuma bada muhimmanci sosai ga sumbatar baki na yadda ran sa yake so, hatta karan hanci na bai tsira ba yau daga warm and romantic passionate kiss din Hamzah.

Kafin a yi haka naji tausasan hannayen sa suna ratsawa cikin rigar jiki na, har yayi nasarar zuge dogon zip din riga ta baki daya ta baya, kafin nayi wani hobbasa ko yunkuri na taimakon kai, ta hanyar riko wuyan rigar da yake son kaiwa kasa, ko bashi hakurin kada ya sauke min ita sakamakon wuta a kunne take, ina jin kunya ina jin nauyin sa… Ina kuma so in gaya masa ban shirya wannan abin kunyar ba tukunna (zama naked a gaban sa), sai kawai naji saukar doguwar riga ta baki dayanta a kasa….Sabida dama nauyin duwarwatsun jikin ta ya rinjaye ta.

A wannan lokacin Hamzah ya gama gigicewa gabadaya, nima kuma ya gigitani fiye da kintace, ban san haka lamarin yake ba ko kadan, ashe dai da mafarki nake yi! Mafarki kuma baka taba hada shi da zahiri, kalaman da yake furtawa sun fi karfin biro na ya rubuta su, sun yi nauyi a cikin kunnuwa da kwakwalwa ta, na tabbata a lokacin ko suna na “Aisha-Siyama” ban sani ba, ko in ce na manta, sabida dadin duniyar soyayyar da Hamzah ya dauke ni ya luluka da ni, bana iya ambaton komai sai sunan sa “HAMZAH…..!” Kamar ni na rada masa sunan. Haka babu komai a rai na da zuciya ta har abada sai “HAMZAH….!”. Bana ganin kowa a gaba na sai shi kadai “HAMZAH”. Son da nake masa ko in ce muke yi wa juna wata kaddara ce rubutacciya daga Allah.

Shi kuma kamar ya san hakan, kamar ya san bidirin dake gudana a cikin rai na, na kan yi mamakin yadda Mr. Hamzah ke ‘reading mind’ dina a lokutta da yawa, sai na ji yace,
“you know what? Even without calling me at this moment, with the sweetest name I like most (HAMZAH) kin same ni kin gama in dai ni Hamzah ne.

Let me confess the truth Siyam, na amince domin ke Ubangiji ya halicce ni, don ke aka qadarta min na zo VOA, don ke nake sha’awar addinin musulunci tun kafin in san ki, don haka you are my ‘soulmate’, na mallaka miki zuciya ta da gangar jiki na bakidayan su.

Idan yau na ce na baki amanar kai na da rayuwa ta wane irin riko zaki yi musu? Idan kika yi musu (rikon sakaci) na rantse zan iya rasa rai na.

Kiran sunan sa da nake ta yi a jejjere ban fasa ba, cikin kukan kissa (wadda ban san daga ina na koya ba), ban kuma san ina yi ba kara gigita shi da kunna shi yake yi. A lokacin da yayi nasarar balle bra dina ne komai ya karasa kwance ma dan mutanen Birom, haihuwar Riyom, ya rikice masa ya hautsine masa, azancin sa ya kwace masa bakidaya….
Ni kaina na san Allah yayi halitta a kirji na, wadda ni da kaina na san ta sha banban da ta sauran mata ‘yan uwa na. Nonuwa na masu gindin tasa ne irin wadanda ko ‘ya’ya goma na shayar sai dai su rankwafa ba dai su russuna ba. Da harshen turanci na ji Hamzah ya ce “tsarki ya tabbata ga Allah guda daya! Na shaida babu sarki sai Allah kuma guda DAYA ne bai da abokin tarayyah, na gode maSa bisa alfarmar da ya yi min ya halatta min ke!”

Ya jaddada imanin da yayi da Allah a fili da zuciyar sa, ya kuma tsarkake shi da sunan sa “Wahidun-Ahadun” wato guda daya. Daga wannan lokacin ban kara jin komai daga bakin sa ba sai saukar bakin sa da lips din sa kan kirjin nawa…. Al’amarin da ya sa ni cikin tunanin cewa ko dai mafarki nake yi? Ko ire-iren mafarkai na ne a kan Hamzahn,

wadanda basu da karshe? Don al’amuran da ke guda na a wannan ranar, sun fi min kama da irin mafarkan da dan adam baya so ya farka sabida kada ya fita daga cikin falala da ni’imar cikin su. Wanda gardin Zahiri da ke cikin su ya matukar banbanta dana cikin mafarkai na.

Idan kuwa har ire – iren mafarkai na ne, wadanda na saba yi a kai na da Dream husband dina…. YA ALLAH wannan karon kada kasa in farka… da dai in farka daga wannan mafarkin dana ke yi a yau, gara in zarce, wato in mutu a cikin dadin sa da ni’imar da nake dandana a cikin sa…. wadda gardin ta yafi na madara, zakin ta ya fi na zuma!”


Adai-dai lokacin da Hamzah ke gab da kwantar da ni a gadon auren mu, domin idasa cika sunnar aure sakamakon kafafun mu da suka kasa daukar nauyin gangar jikkunan mu ne na tuna bamu yi sallahr da Annabi SAW ya kwadaitar da sababbin ma’aurata ba. Amma a halin da Hamzah ya samu kan sa a wannan dan tsakanin, na san ba abinda zan fada, ba kalar bayanin da zan yi ya saurare ni, in dai maganar a dakata ne, ko da kuwa da wane yare zan fada ba zai fahimta ba, ko da da harshen sa na Birom ne, ba abinda zan ce da zai iya dakatar da shi daga abinda yake son cimmawa. Burin sa kawai ya cika alkawari na farko daga cikin ire-iren manyan alkawuran da ya daukar min kafin tabbatuwar auren mu, na cewa ‘he will make sure’ ban sha wahalar dakon soyayyar sa shekara sama da goma a banza ba! He will make up the ten years sufferings in only ONE night, in such a way that, zan zama ‘fi-sauran mata’ a fannin soyayyar miji da kulawar sa, don haka ba abinda zan yi in fahimtar da shi muhimmancin yin ita wannan nafilah, domin gabadaya idanuwan sa sun rufe ruf, sun makance a cikin uzurin sa, kunnuwan sa sun kurumce daga jin komai ban da kai kawon numfashin mu, kafafuwan sa sun gurgunce domin kuwa sun kasa rike nauyin gangar jikin sa a tsaye, burin sa na ga son kaiwa ga ci, da kuma son sauke samartakar sa da tuzurancin da ya kwashe shekaru 38 a cikin sa….


Babban burin sa a wannan lokacin kawai shine ya bi layin sauran maza magidanta ‘yan uwan sa, ya cika sunnar Ma’aiki SAW ya tabbatar da Siyam matsayin matar sa ta sunnah, kuma uwar ’ya’yan sa da yake fatan Allah ya bashi ta tsatson ta kadai. Yana so ne ya tabbatarwa Siyama bata yi wahalar banza ba, dakon nauyin soyayya a zuci tayi nata, shikuwa nasa a gangar jiki da ruhi ne.
A lokacin ne ni kuma wani irin matsanancin tsoro ya shige ni, ganin cewa al’amarin da Hamzah ya zo da shi a yau babba ne fiye da yadda zan iya kintatawa, nauyin sa da girman lamarin da Ubangiji ya boye a cikin sa ya shallake duk yadda nake tunani, ko jin sa a labaran hikaya. Kai tsaye so yake ya karbi sadakin sa babu bata lokaci babu jinkirtawa tun a ranar mu ta farko. Na fahimci Hamzah daban yake a wannan fannin ya wuce duk yadda nake tsammanin sa da mafarkin kasancewar sa, yanayin yadda yake tafiyar da matar sa a shimfida (with love, care, gentleness and affection) daban ne dana sauran maza, haka a kira ta suffer jiki da mazantaka ko a cikin maza shi Hamzah mazaje ne.


Wannan ya faru ne lokacin da Hamzah ya latsa makunnin fitilar jikin gadon mu, wata irin shudiyar fitila mai rangwamen haske ta mamayi dakin, nayi nasarar ganin miji na Hamzah in his physical reality, sai na kasa daurewa, sabida matsanancin tsoron da ya shige ni sakamakon ganin dana yi masa lallai wani abu sai aure domin ban taba ganin namiji haka ba. Na soma kokarin kwatar kai na ko da tsiya ko da arziki, don ban ga ta ina zan iya jure ma al’amarin nan ba tare dana cutu ba.

Hamzah ya rasa inda zai sa kan sa da turjiyar dana soma yi masa. Cewa yake, “…. Yi hankuri, ki barni in yi a sannu, kada in ji miki ciwo, kin ji my Damsel?!” Abinda ya iya fadi kawai kenan daga can kasan makogaron sa, kamar wanda ran sa ke shirin fita jikin sa, wani rangwame ko kuwa alfarma guda daya da a yau yake jin bazai iya yi wa Siyam shi ba, koda zata cutu, domin ya san zai fi ta cutuwa idan ya yi mata alfarmar data ke nufi zuwa wani lokacin. Ganin cewa Hamzah bai da niyyar sauraro na na soma rokon sa cikin rishin kuka, kan ya jinkirta min zuwa lokacin da zan samu amincin hakan da zuciya ta. Wannan karon kukan nawa dan asali ne dan gaske, babu waccan kisser ta farko, babu digon soyayya a cikin sa face tsagwaron tsoro irin na sabun shiga, da tsananin tausayin kai.

Hamzah yace cikin shakewar murya da rawar harshe “don’t do this to me, kada ki yi mun haka Siyam, in kika yi hakan zan cutu, zan…. zan mutu!!!

Ki taimaka min ki bar ni, ki daina mun turjiyar nan don Allah kada in in ji miki ciwo, for the first time just for today kadai ki bar ni in nuna miki girman matsayin kaunata gare ki, ba zan iya jinkirtawa ba, ki bar ni in cika alkawari na nima, na yi wa kai na alkawarin first night immediately bayan aure, kamar yadda na taimaka kika samu cikar mafarkan ki, nima ina son cika alkawarin dana yi wa kai na na cire samartaka ta a daren yau ko da sau daya ne a rayuwar mu, ko na yau ne kadai don Allah Siyaaaamah!

In ya so… In kin so daga yau bazan kuma ba sai da amincewar ki”, tashin hankali yasa ya kasa karasa maganar, ta shaqe shi iya makogwaron sa ta koma… ganin Siyam ta ki daina kokawa da shi.

Ya hada dogon karan hancin sa da nawa, ya shiga begging… roko sosai yake cikin dusasshiyar murya, yana hadawa da kissing, da shafa gashin kai na cikin lallashi da neman yarda ta, domin a lokacin nayi nasarar kwatar kai na, na koma gefe na cure jiki na waje guda kamar macijiya na hana shi access din komai.

Shi kuma Hamzah ne, Mawonmase ne na Siyama ba da kan ka a sare ba zai iya forcing dina ko ya saka min karfi ko makamancin haka ba, har abada ba zai yi wannan ba.

Yadda yake rokon, da rawar da muryar sa ke yi, sai naji kamar ja na yake yi da wani irin magaadisu, kamar kuka yake yi haka, amma ba zan gane hakan ba sabida rangwamen hasken fitila, amma a muryar sa na fahimci tabbas Hamzah kuka yake yi, wani irin sheshshekar kuka a cikin wani shauki na soyayyah, wanda yake ji tamkar an raba shi da dukkan numfashin sa, lokacin da na janye na dunkule jiki na waje daya na hana shi samun access din komai. And he didn’t force me from then. Ya kwanta ne kawai ya bani baya yana maida numfashi a hankali. Tausayin sa, kaunar sa da wannan dadadden son dana ke masa mai tsohon zango su suka taka rawar su a wannan lokacin ma, wato soyayyar dana ke masa ‘yar asali da tushe ta shekara da shekaru wadda tasirin ta ya janyo har ta samu lasisin kora daga Abba, ita ta motsa kan ta da kan ta, ta rinjayi tsoron da ya kawo min farmaki ta hanyar sarrafa ni akan miji na abin kaunata

yadda take so.

Lokacin dana mika hannuwa da kai na na rungumo shi ma ban sani ba. Kamar wadda ake yi wa umarni da hakan. Hamzah ne fa! Dream Husband dina da na ci bakar wuya kafin in samu ya zam mallaki na. Don haka ko me zai min na tabbata a cikin soyayya ne. A cikin son da Allah ya sanya a tsakanin mu ne. Daga haka na sakar masa ragamar komai, ya shiga wadaqa dani da juya ni da amfana daga komai nawa yadda yake so, na san ko zai cutar da ni to a cikin son da yake min ne, kuma hausawa sun ce wai wuya bata kisa…. sai idan kwana ya kare.

This happened to be our first night, which marked the beginning of our chronicles, wanda ya kafa tubalin rayuwar auren mu daga wannan ranar. Na zama shi, ya zama ni. Kaddarar rayuwar mu ta fara daga ranar, kuma ranar ne muka zama abu guda, muka san sirrin juna muka koma marufar asirin juna irin sirrin da aure kadai ke wanzar da shi.

Bamu samu kan mu ba sai gab da kiran assalatun fari, Hamzah bai huta ba, nima kuma bai bar ni huta ba a daren yau bakidayan sa, sai da ya tabbatar duk wani hijabi dake tsakanin mu ya cire shi a yau, na gama amsa sunan cikakkiyar matar sa wadda ko yau ya fadi ya mutu sai na yi masa iddah.

Ni kuma na samu cikar dukkan mafarkai na da burika na a kan sa, har fiye da yadda nake kintacen tabbatuwar su a lokutan mafarkai na. He is so genius, and so romantic beyond my expectations, ta fannin kula da matar sa a auratayya.

Shi da kan sa ya taimaka min da duk irin taimakon da ya dace a yi wa amarya a daren farko, alhalin shi Hamzah ba likita bane, amma taimakon da yayi min ko wani babban likitan mata sai haka.  Sannan muka yi sallahr asubah tare, amma kam a zaune na yi tawa sallahr sakamakon kafafu na duka ciwo suke min, a haka na daure nayi domin na ji dadin taimakon da ya yi min da ruwan zafi a toilet. Da muka idar da sallah muka koma cikin duvet dukkannin mu a gajiye, wani barcin asubah ya dauke mu tare, kankame cikin jikin juna kamar tare aka haicce mu, soyayyar dake zukatan mu ta kara habaka ta ninka ta farko, don a yanzu ne muka san ainahin muna son juna.

Hamzah ya riga ni tashi a wayewar gari, sai bai tashe ni ba, tausayi na yake ji sosai, kan rashin daga kafar sa a ranar mu ta farko, da irin wahalar da ya san ya bani don shi kan sa bai san haka al’amarin yake ba sai yau. Shiyasa ya kasa sarrafa kan sa.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Sakacin Waye? 37Sakacin Waye? 39 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×