Ba wanda zuciyata ke kawo min kullum, sai hoton MA’AROUF dan wajenka, shi ne na yo tattaki in nemi wannan iri mai albarka. Ba na bukatar komai sai sadaq (sadaki) da Allah Ubangiji ya yi umarni. Amma idan Ma’arouf bai amince ba, don Allah kada hakan ya yi sanadiyyar da gaisuwar makwabtakar da muke yi da juna za ta tawaya, kuma kada a takura masa. Abu ne dai da nake da yakini a kai ba zai samu matsalar komai da Aisha ba, saboda ko cikin ‘yan uwanta ta fita daban wajen hankali da kyakkyawar tarbiyya.”
Malam Habib ya. . .
Jinjinna