Skip to content
Part 39 of 71 in the Series So Da Buri by Bulama

Da sauri Sakina tace “Mamaa” sai kuma ta k’arasa wajen da sauri ta hau tattab’a ta, ganin bata motsi yasa ta sa hannu ta juyo da ita!

“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Shine abinda Sakina Ummu da matar dake gefen Mama suka fad’a a tare, dan a yadda Sakina ta juyo da ita haka ta biyo hannun Sakinan ta taho yuuu ta zube wanwar kwanciyar rigingine.

Ummu mutuwar tsaye tayi a wajen, so take ta k’arasa inda suke amman ta gagara sakamokon ganin y’ar uwartata da tayi kwance tamkar gawa! Ta kasa tab’uka komai banda hawaye ba abunda take yi.

Sakina wadda ta rikice tana ta tattab’a Maman ne ta juyo tace “Ummu ki zo ki kamata mu mik’ata emergency. Mama ce amman bata numfashi.”

Jin hakan ba k’aramin sake rikita Ummu yayi ba, ita dai kawai ta ganta a gabansu a tsaye amman bata san ya aka yi ta isa wajen ba.

Matar nan ce ta matso itama ta hau jijjiga Mama tana cewa “kuma fa yanzun nan muka gama magana da ita, tun jiya muke nan tare da ita. In banda kuka ba abunda take yi, nayi tambayar duniyar nan tak’i kulani. Sai dai kawai taje tayo alwala tazo tayi ta sallah. Sai d’azu ne da naga kamar batta lafiya nace ‘tazo muje in rakata taga Likita’, shine na samu ta d’an kulani ta inda take ce min ‘bara ta d’an yi bacci, idan ta farka sai muje’.”

Ita dai Sakina cicib’arta ta fara k’ok’arin yi hakan yasa suma suka sa hannu suka taimaka mata suka yi waje da ita.

Su Madu suna tsaye a k’ofar shiga emergency. Kana ganinsu ka san hankalinsu ba a jikinshi yake ba!
Ga tsananin gajiyar da suke tare da ita
Dan ma Allah ya taimaka Abokin Junaidu ne ya biya musu kud’in jirgi su kuma suka biyawa Baba Saboda yaga yanayin tsufansu gashi da ya kira Baban ma a hanya ya jisu suna dawowa daga wata tafiyar. Ba dan haka ba da gajiyar ba zata yi musu da sauk’i ba.

Suna tsaye suna tunanin abunyi next suka hango su Ummu d’auke da mata suna nufusu, sai da suka matso su sosai sannan suka gane Mama ce. Basu samu damar tambayar su ba dan da sauri mai gadin k’ofar ya wangale suka shige kawai dukkansu…

Ana ganin su aka karb’es u bayan an kawo gado an d’aurata, aka tura ta ciki don yin bincike.. Ba a jima ba sosai, Dr ya fito! Likitan dai da ya karb’eta jiya shine, magana d’aya ce ya maimaita musu “hawa da jininta yayi over ne ya janyo komai, amman this time around har eco za suyi” Nan yake ce musu “ba yadda bai yi da ita jiya akan ta zauna ta shanye drip d’inta ba amma tak’i, ta biyewa wasu suka dinga hayaniya suna fad’a! Yayi yayi akan suyi shiru suka k’i, shiyasa shi kuma ya sallameta, so suma in sun san hayaniyar za suyi gara karma su shiga inda take, dan zai sake korar su ne!”.
Yana gama fad’in haka ya nuna musu inda take sannan ya wuce.

Bayan kamar awa d’aya, Kaka da su Baba suka wuce aka bar Sakina da Ummu. Su Kaka na fita Hudan wadda take kiran Sakina a kai a kai ta kira, nan Sakina ta gaya mata “sun ganta suna tare ma yanzu haka”. Sai a lokacin hankalinta yad’an kwanta.
Nan itama Sakinan take tambayarta “tana Ina?” Hudan tace mata “tana wajen Gwaggon su Aslam, amman still Abba bai san tana gidan ba, dan a b’oye ma Arshaad ya kawo mata wayarta data bari a gidan Gramma, so in shaa Allah gobe da sassafe za ta san dabarar da zata yi ta gudo.” Shiruu, Sakina tayi chan tace “ki bari mu yi magana da Ummu tukunna, kar ki yi komai, kinji?” Ummun ce tasa hannu ta karb’i wayar suka yi magana da Hudan ta d’an kwantar mata da hankali, kafin suka yi sallama.

Da kyar suka samu bacci ya kwashe su wajen k’arfe 3 na dare.

Da sassafe su Madu da Baaba Talatu suka zo kawo musu breakfast, har lokacin Mama bata farfad’o ba.
Sama sama take jin hayaniyar su dan haka ta fara k’ok’arin bud’e idanunta.
Sakina wadda take a kusa da ita ce ta lura dan haka ta maida gaba d’ayan hankalinta gareta, ganin Sakina ta k’ura mata ido ne ya sanya suma duk suka taso suka zagaye gadon suna tambayar “mai ya faru?” Basu ida tambaya ba Mama ta k’arasa bude idanuwanta. Tsantsar farin ciki ne ya baiyyana a fuskokinsu gaba d’ayansu, cikin murna suka hau furta “Alhamdulillah” suna tambayarta “ya jiki?”

Da kyar Baaba Talatu ta taimaka mata ta mik’e ta zauna.

Tana zama suka had’a ido da Ummu!
Kawai sai ta fashe da kuka abun tausayi. Duk shiru suka yi.

Da kyar Madu ya samu ya k’ara so inda take ya dafa ta sannan ya d’an fara bubbuga bayanta alamun lallashi.

Farin ciki ne ya mamaye zuciyoyinsu gaba d’aya, duk sai suka hau murmushi, Kaka har da y’a kwallar shi, ya sa hannu share ba tare daya bari kowa ya lura ba. Ita kanta Mama duk da yanayin da take ciki hakan sai da ya sanyata zubar da kwallar farin ciki, dan rabonta da Madu ya nuna kulawar shi a kanta kaman haka, yau
yau shekaru ashirin da bakwai kenan!.

Share hawayenta tayi sannan ta d’ago ta kalle shi, shima itan yake kallo, ba abinda ta hango a idanuwan shi sai tsantsar tausayinta, bakinta na rawa cikin kuka tace “Abba, ya raba ni da Huda! Dan Allah ku karb’o min ita, wallahi mutuwa zan yi in ba y’ata, na shak’u da ita sosai, ba zan iya yarda in bar mishi ita ba.”

Da sauri Ummu ta k’araso ta rungumeta, sannan cikin tsananin tausayinta tace “Ki yi hak’uri ki huta, munji komai, in kika warke sai a san abun yi, ki kwantar da hankalin ki dan Allah.”

Cikin jujjuya kai Mama ta zare Ummu a jikinta kafin tace “Bilkisu ba zan iya yin hak’urin nan ba!! Abba ya zama wani irin mutum! Mugun mutum. Shi ne fa ya turo Arshaad wajen Huda, Arshaad cousin d’inta ne! Suka dinga yaudarar mu, idanunsa akan mu yake all this time amman bai baiyyana kanshi ba sai yanzu? Saboda ko nace ba zata koma wajenshi ba ya san ai Arshaad zata aura, kenan ko?
Wanne irin ubane zai yiwa y’arsa haka? Bilkisu gaba d’aya kaina ya kulle, a baya yace ‘baya buk’atar ta’, yanzu kuma yazo ya raba ni da ita a lokacin da nafi buk’atar ta, mai yasa zai yi haka? Laifin me na yiwa Abba da zafi haka??”. Ta k’arashe maganar tana mai fashewa da kuka.

Lallashinta Kaka Baaba Talatu da Ummu suka hau yi, amman furr!! Tace “ba zata hak’ura ba! Ba zata iya yin hak’urin da suke so tayi ba, yanzu zata je ta taho da y’arta, barinta a hannun Abba danger ne! Tunda har ya iya turo wani wajenta saboda son zuciyarshi bai damu da yana sonta tsakani da Allah ba ko akasin hakan ba Tou tabbas zai iya yin komai. Ko bayaga haka ma idan duk duniya zata taru a kanta tofa ba zata d’auki y’arta wadda Abban ya ce ‘baya so ta fad’a mata ko da sunan shi ne’ ba, ta bayar a shi yanzu! Sai dai duk abinda zai faru ya faru. Su yi mata kwatancen gidan ko kar suyi mata zata tafi ta nema, tunda Allah yasa taji kwarin jikinta yanzu, daman jiya ma jiri ne ya hanata motsawa daga inda take.”

Gabad’aya Mama ta hargitse musu, data ga ma ba zasu bata goyon baya ba, sai ta fara k’ok’arin sauk’a daga kan gadon sannan tasa hannu zata cisge cannular hannunta.

Madu ne ya rik’e hannun nata, kafin cikin lallashi yace “Maryam koma ki zauna muyi magana.” Cikin sheshshek’ar kuka ta koma ta zauna tana share hawayenta.

Sai da yaga ta d’an sassauta kukan nata, sannan ya fara magana “Ki kwanta ki huta, ba ki da lafiya.
Koda kin fita za ki sake fad’uwa ne, saboda baki gama dawowa normal ba!
Ki zauna ki shanye allurai da magungunan ki, da ni da Babanku Bashir za muje mu samu Abba, in shaa Allah, kinji ko??” Da sauri Kaka yace “Za muje a yau! Ki kwantar da hankalin ki kinji?”

A hankali taji kad’an daga cikin nauyin da zuciyarta tayi ya d’an sauk’a, dan haka ta d’aga musu kai alamar ‘to’ kawai, tana sharar hawaye.

Ajiyar zuciya Baaba Talatu ta sauk’e, sannan ta nufi wajen kulolin da suka kawo ta zubowa Mama abinci ta kawo mata. Sakina ce ta karb’a ta fara k’ok’arin bata, amma sai ta kauda kai gefe tace “ta k’oshi” Cikin turo baki Sakina tace “haba Mama ki ce mana, kin ganki kuwa yadda kika koma? Gashi duk kin yi wata zuru zuru kamar…” Dukan da Maman ta kawo mata tayi saurin kaucewa, duk kuwa sai suka hau murmushi.

Da naci da komai haka nan sai da Sakina ta d’urawa Mama abincin nan, ta kuwa ci sosai, dan sai da su Madu suka sa baki tukun Sakina ta hak’ura.

Sai wajen 11 na safe su Sakina suka fara shirin tafiya don suke suyi wanka suyi girki, ita da Ummu.

Baban su Sakina ne yazo d’aukar su!
Ya d’auka Mama ko wani zai yi mishi maganan Arshaad amman yaji shiru shiyasa shima yana yiwa Maman ‘ya jiki’ ya fita, dan baya so suyi mishi d’in, but ya tsara a ranshi zai gayawa matar shi, duk abinda ya sani, da kuma dalilin yin shirun da yai, saboda kar ayi mishi kallon munafuki.

Sai da suka biya duk wani bill sannan suka tafi a lokacin an tafi da mama yi mata eco. Su Kaka ma shirin tafiya gidan su Abba suka yi, aka bar Baaba Talatu. Sai a sannan ne Baba yazo, ganin Maman bata nan yasa suka gaisa da Baaba Talatu ya wuce kasuwa akan zai dawo da azahar in shaa Allah.

Su Kaka basu samu damar zuwa gidan su Abba ba, sai la’asar, a sakamokon kiran da aka yi musu akan results d’in da ya fito, dangane da case d’in Junaidu.

Yadda Hudan taga rana haka taga dare, Gwaggo Asabe har mamakinta take yi dan duk juyi in tayi sai taga idonta biyu! Gaba d’aya ta kasa bacci ta k’agu Safiya tayi taje taga jikin Maama, da taga safiya ta k’i yi k’arshe kawai mik’ewa tayi taje ta d’auro alwalla, tazo ta fara jero nafilfili.

Tana idar da sallar asuba kuwa bayan ta gama Azkar ta d’anyi karatu, ta shiga tayi wanka. Tana fitowa ta tarar Gwaggo Asabe bata d’akin, hatta sallayar data barta akai ta nad’e.
Doguwar rigar da Gwaggo Asaben ta bata jiya had’e da Maclean da brush sabbi ta d’auka ta sanya, luckily ta samu comb a d’akin cikin drawer, dan haka ta goge shi da tissue sannan ta sa hannu ta zare ribbom d’inta ta hau ware tufkar da ta yiwa dogon gashinta wanda yanzu har ya kai tsakiyar bayanta, ita kanta tana mamakin yadda ya tofo a cikin shekara uku! Bayan askin dolen da Ya Jalila tayi mata. Tunawa tayi da Jalila wadda Sakina tayi mata k’us k’us d’in Khadija tace mata ‘kamar ciki ne da ita( Jalilan)’ amman Umma tayi k’arya tace ‘ta tafi jinyar Hansai’. A hankali ta sauk’e ajiyar zuciya a ranta tana adduar ‘Allah yasa ba cikin ne da ita da gaske ba’ abunka da zuciya mai kyau! gaba d’aya duk sai taji tausayin Yayar tata ya lullub’eta, don haka ta hau yi mata addua da fatan alkhairi, tana yi tana taje kanta.

Sai da ta gama tsaf, ta d’auko ribbon d’in ta tufke gashin a d’an k’asan tsakiyar kanta kad’an! Ganin yadda jelar take reto ne ya sanya ta kanannad’e gashin waje guda ta tura ta had’e da ribbon d’in, d’ankwalin doguwar rigar ta d’auko tayi style d’in V da d’aurin very simple amman ba karamin kyau tayi ba, ga gashin data duk’unk’une ana iya hango santsi da kyallin shi da uban yawa dan d’ankwalin k’aramine sosai so bai gama rufewa ba.

Ta d’auko wayarta kenan zata kira su Mama ta ganta a kashe, ba chargi.
Ajiyar zuciya ta sauk’e, daman ta san za ai haka, dan tun jiya chrgin ta yayi low sosai.

Zama tayi tana jiran Gwaggwo Asabe ta dawo ta ari wayarta ta kira su Mama don duk ta haddace nambobin su. Kusan minti arbain taji shiru, ga anxiety yana neman kashe ta! Shiyasa ta yanke shawarar mik’ewa, ta hau nemanta.

Bata wani sha wahalan neman nata ba, dan tana fitowa daga d’akin taji k’amshi ya cika ko Ina a gidan wanda hakan ne ya tabbatar mata da inda take(Gwaggwo Asaben), dan haka ta nufi k’asa. A k’ofar kitchen d’in suka had’u da Gwaggon, da tray a hannun ta, da kuma tea flask da ta rik’e da kyar. Sai da Hudan da d’an rissinar da kai tukunna ta gaisheta.

Da kulawa Gwaggo Asabe ta amsa.
Har ga Allah ta dad’e bata had’u da Yarinya mai hankali da nutsuwa irin Huda ba, ga kyau tubarkallah, shiyasa lokaci guda suka saba, taji ta shiga ranta sosai! Har k’asan zuciyarta take yiwa Aslam d’insu kwad’ayin auren Yarinyar saboda ta had’a komai ga kyau ga hankali ga nutsuwa gata y’ar uwarshi! Sai dai kuma yadda taga Arshaad yana shige mata sosai, watak’il shi ne zai fara cewa yana sonta, dan jiya ta lura har wata y’ar hira suka tsaya yi a parlour, sai wani nan nan yake yi da ita. Hannu Huda ta saka tana k’ok’arin karb’ar tea flask d’in dake hannunta wanda hakan ne ya katse mata tunanin ta! Ba musu ta sakar mata , dan itama tana jin yadda ya kusan fad’uwa. A tare suka nufi hanyar sama, tana gaba Hudan na biye mata baya, wata hanya suka kuma d’auka bayan sun shanye stairs d’in,
nan ta sake hango wani bene, benen suka bi suka hau, suna kaiwa k’arshe suka tarar ta wata y’ar k’ofa A bud’e k’ofar take hakan yasa suka shige, dogon corridor ne sosai, sai k’ofofi biyu, d’aya a farko farko hanyar dama, d’ayar kuma a kusan k’arshen dogon corridor d’in ta hannun hagu, Wadda itan taga Gwaggwon ta nufa, sai da suka iso bakin k’ofar, tukun suka tsaya! Rik’on tray d’in Gwaggwo Asabe ta gyara sosai a hannu d’aya sanna tasa hannu tayi knocking, tukun taja ta tsaya, ta gyara ruk’on tray d’in. Kusan minti biyu tukunna suka ji ance “come in” Hudan ta kalla tace “tayi amfani da empty hand d’inta ta bud’e musu.”
Hakan tayi, bayan ta murd’a handle d’in a hankali ta d’an tura sai kuma ta matsawa Gwaggo Asabe don ta fara shiga. Murmushi Gwaggon Asabe tayi sannan ta shige Itama Hudan ta bita a baya. Sai da ta rufe k’ofar tukun ta juyo ta fara kallon d’akin.

“Ma shaa Allah” ta ce, a ranta.
Ba za ka kira shi d’aki ba kuma ba zaka kiravshi da parlour ba, ga set d’in kujeru har da k’aramin dining, da makekiyar tv d’in da bata tab’a ganin irin ta ba, ga kuma set d’in gado shima komai akwai, royal, light blue da fari haka colour d’in kujeru da gadon suke, hatta pentin d’akin haka yake. Ga kuma wani glass door, wanda kana iya hango swimming pool da shuke shuke da kujerun shak’atawa. K’auyanci ta fara, don a ranta ta hau rayawa “daman ana pool a sama? saman ma ta biyu! Ita tunda take bata tab’a ganin d’aki mai girma sosai da kyau irin wannan ba!.”

Tunanin ta ne ya katse jin Dad yana cewa “Hudan k’araso mana ya kika tsaya a k’ofa?”.

Sai a lokacin hankalin ta ya kai kan Dad, da wata mata a zaune a gefen shi yana rik’e da hannunta.

Ji tayi kamar ta rusa kuka!! Da ta san gurin shi Gwaggo Asabe zata zo da bata biyo ta ba, kenan ita duk b’uyan da take yi ma a banza, tunda gashi a gidanshi ma ta kwana ba tare data sani ba, kuma yadda ya nuna it’s like ya san tana nan d’in, shikenan ta san yanzu zai kira Abba shi kuma ya hanata zuwa taga Mama.

Gwaggo Asabe ce ta katse mata tunani jin ta sake cewa “Huda k’araso mana.”

A hankali take takawa izuwa bakin gadon inda suke. Taji Dad yana cewa
“Ashe da gaskiyar Abba, daman ya ce tana wajensu Aslam ni ban yarda ba,
sune suka kawota jiyan ko?”

D’an murmushi Gwaggo Asabe tayi kafin tace “Eh jiya lokacin da ka kira ni, Arshaad bai dad’e da kawota ba, shi ya rakota.”

Hudan dake jin su duk sai taji jikinta yayi sanyi, ashe ita kad’ai take ta shirmen ta. A hankali ta k’arasa wajen, kanta a k’asa. Har k’asa ta durk’usa ta gaida Dad, wanda cikin tsananin son da yake yiwa y’ar d’anuwan nasa yayi saurin kamo ta ya zaunar da ita a kan d’an stool d’in da yake facing d’inshi,
cikin kulawa ya amsa kafin ya hau tambayarta “ya kwanan bak’unta?”
“Alhamdulillah” kawai ta iya cewa kafin ta juya ta hau gaida matar gefen shi har sau biyu amman ba alamun zata amsa kuma ta kafeta da idanuwa!
Tana shirin sake gaidata a karo na uku ne, Dad ya sauk’e ajiyar zuciya ya d’an dafa Huda tukun yace “Karki damu ba zata iya amsawa bane, amman ta fahimceki, tunda gashi tana ta kallonki.”

Yana gama fad’in haka ya juya ga Gwaggo Asabe jin tana cewa “ga breakfast, watak’il taci tunda naga yanzu jikin da d’an sauk’i, ko?”
Shiru ya d’anyi kafin ya sauk’e wata ajiyar zuciya tukunna yace
“Sai addua fa, amman Alhamdulillah, ni fa da Granpa zai yarda wallahi da an hak’ura da wannan theraphy d’in, saboda duk lokacin da aka je aka yi aka dawo ni sai inga kamar abun k’aruwa ma yake yi, kwanaki fa har hira tana yi, amman yanzu kiga gaba d’aya sai a hankali, danfa baki ganta last two weeks ba (Tym d’in da suka dawo. A Abuja), shiyasa ai na hanata dawowa nan, da kyar fa da addu’o’i tukunna abun yayi sauk’i ta dawo hakan.”

Ajiyar zuciya Gwaggo ta sauk’e kafin tace “nima dai gaskiya na dad’e da lura, magana ce kawai bana so.”

Cikin d’an fad’a Dad yace “Ai kuwa ta gama theraphy! Dan a gaskiya, ko ance za aje, sai dai In kaita Abuja kawai muyi sati mu dawo, abu ba fad’ar Allah ba amman an maidashi kamar dole!?”

Kwalla Gwaggo Asabe ta share sannan tace “Ai shima Granpa d’in naji yana cewa ‘daga wannan an gama’.”Cikin katseta Dad yace “ai tun last year yake cewa ‘daga wannan an gama daga wannan an gama’! Amman an kasa gamawa da gasken.”

Ajiyar zuciya Gwaggo ta sauk’e ranta duk ba dad’i da yanayin y’ar uwarta ta. A hankali ta durk’usa ta fara serving abincin cikin mutuwar jiki. Hudan itama duk jikinta yayi sanyi dan haka tace “Allah ya bata lafiya”. A hankali Dad ya d’an juya ya kalle ta sai kuma yace “Ameen” cike da jin dad’in adduar tata.

Juyawa yayi ya kalli Mommy, gani yayi har yanzu Hudan take kallo, kamar tana so ta tuna wani abun. Bai gama fahimtar yanayin ta ba yaga ta d’aga hannunta sannan tayi amfani da yatsar ta manuniya wajen sai da Huda!
Gaba d’aya hankulansu kanta ya koma, cikin rawar murya kamar ta mai koyan magana suka ji ta ce
“Aaa-sllam, ttanna kama ddda Aasllm d’Ina”.

Ba Dad ba hatta Gwaggo Asabe sai da
gabanta yayi wani irin mahaukacin fad’uwa! Rabon da Mommy ta kira sunan Aslam, tun kafin ta fad’o daga bene!

Gaba d’aya rawa jikin Dad ya d’auka, a hankali ya sa hannu ya juyo da fuskarta, ya kalli cikin idanunta sannan yace, “kina so kiga Aslam d’in naki?” Da sauri ta hau d’aga mishi kai, sai kuma hawaye, shaaarrrr suka zubo mata.

“Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!” Shine abunda Dad ya dinga maimaitawa, cikin kid’ima ya mik’e ya fita yana cewa “su Gwaggwon su tsaya gashi nan zuwa, kar kowa yaje koina.”

Ba ayi minti goma ba sai gashi ya turo k’ofa, rik’e da hannun Aslam Abba yana binsu a baya! Cikin zumud’i yace “Ga Aslam d’in naki” ya fad’a yana tunkarar ta, yana cewa su Abba “komai yazo k’arshe in shaa Allah, Aslam yau da kanta ta kira sunank.”

Razananniyar k’arar da ta fasa ce ta hanashi k’arasa maganar tashi, ta kuma rud’a duk wani wanda ke a cikin d’akin!! Basu ida dawowa haiyyacinsu ba ta kuma sakin wata k’arar! Wadda kusan rabin estate d’in sai da aka ji!.
Cikin tsananin tashin hankali firgici kid’ima da tsoron da ya baiyyana k’arara a kwayar idanunta take nuna Aslam d’in tana kururuwa!

A kid’ime Dad wanda duk ya rud’e ya sake nufota still yana rik’e da hannun Aslam wanda ya sake shiga tsananin tashin hankali da rud’ani don shi Dad ce mishi yayi “yazo Mahaifiyarsa tana nemanshi yau da kanta!” Gashi yanzu kuma ya tarar da haka!

K’arar da ta sake saki ne ya kid’ima su dan tafi ta ko yaushe! Sai kuma ta saki jiki rigif ta fad’i sumammiya akan gadon. Da sauri Aslam wanda idanuwanshi suka kad’a sukai jaa over, ya k’arasa inda take ya hau jijjigata yana kiranta amman bata motsi, d’ago jajayen idanuwanshi yayi yana kallon Dad. Gabad’aya sai Dad d’in yaji tausayin su, su duka ukun ya lullub’e shi.

Abba ne yayi k’arfin halin zuwa inda suke, yad’an kura mata ido kafin ya cewa Gwaggo Asabe “ta mik’o mishi ruwa!”

A hankali yake yayyafa mata ruwan, har sun cire ran zata farka sai kuma sukaga tana motsi da idanunta alamun zata farfad’o. A hankali Abba yad’an kalli Aslam wanda ke zaune a gefenta ya rankwafa kanta sannan ya kama hannunta gam!! Yana kallon idon da take k’ok’arin bud’ewa, alamun a kag’e yake yaga ta bud’e idanun nata!

Da kyar Abba ya tattaro courage d’in da ya iya cewa Aslam.

“Aslam, ko zaka d’an je waje ko? Kar ta farka kuma ya zamana kai d’in zata fara gani.”

Da sauri yace “No Abba, I think bata gane ni bane ba.” Sai kuma ya kalli Dad yace “Dad da kanta ai kace ta kirani ko?”

Ganin da Dad yayi Aslam d’in na neman koma musu wani firgitachche ne ya sanya shi kawai cewa “Kaje wajen tukunna mu gani.”

Jikinshi har wani karkarwa yake yi, sai da Dad ya sake cewa “I’m so sorry Aslam, ita tace a kiraka but ban san me ya sake faruwa ba kuma, for now just, ka d’an jira a waje ko?”

A hankali ya cika hannun ya mik’e ba tare da ya yarda ya had’a ido da kowa ba ya fice, daidai nan Dad ya fashe da kuka, gabad’aya sai hankalin su Abba ya sake tashi, saboda abune wanda basu saba gani ba! Don haka duk sai suka hau bashi hak’uri suna tausar shi, tare da adduar in shaa Allah Allah zai bata lafiya soon

A b’angaren Dad shi kuma Aslam yake ji, da ya sani da bai yi saurin kirans hiba, gaba d’aya duk sai yaji ya tsani kanshi. Da kyar suka samu ya tsaida kukan ya k’arasa gurin Mommy wadda ta farka yanzun tana ta faman dube dube a mugun tsorace alamun neman tsari take daga sake ganin Aslam d’in.

Sai da komai ya lafa sannan Gwaggo Asabe suka fito ita da Hudan daga d’akin.

Ita dai Huda gaba d’aya kanta ya kulle, hakan yasa ta kasa hak’uri ta hau tambayar Gwaggo “me ke faruwa? Mai ya sameta take haka? Tun yaushe? An yi mata sauka?”

Dan ita Huda har ga Allah kawai ta fi jirkita akan lamarin na iska ne, tunda gashi dai ita da kanta ta tambaye shi but yana shigowa gabad’aya ta firgice! Taya ya uwa zata dinga gudun d’anta haka?? Don ko ba a gaya mata ba ta gane itace Mahaifiyar Aslam ko dan yanayin kamar da suke yi da juna! But why him? Him alone?”

Ajiyar zuciya Gwaggo Asabe ta sauk’e sannan tace “ba ni minti talatin, inje inyi wanka, Ina dawowa za kiji komai in shaa Allah.”

Kamar yadda Gwaggo Asabe tace
Sai da tayi wanka ta dawo ta zauna sannan ta fara bata labarin.

Asalin sunan Mommy, Aisha ana kiranta da Humaira, k’anwarta d’ayar duniya Khadijah wadda ake kira da Asabe. Aisha da Asabe sun taso cikin yanayin k’unci na rayuwa ata dalilin babu. Yahaya ya had’u da Aisha ne lokacin da ya kai ziyara Taraba, jalingo a wani d’an k’aramin k’auye. Ata dalilin, masallaci da makarantun addinin daya d’auki nauyin ginawa.
A rafii yana zagaye ita kuma taje d’ebo ruwa suka had’u. Tunda ya kyalla ido ya ganta ya rikice, a lokacin Mahaifiyarsu ta rasu Mahaifinta kawai ya rage musu. Tun Aisha tana kauce mishi har itama ta fara kulashi sama sama. Tashi d’aya ba kwana kwana ya nuna mata yana k’aunarta kuma yana son aurenta, Bata bashi amsa ba tace “yaje ya samu Mahaifinta”. Yahaya bai yi wani jinkiri ba yaje ya samu Mahaifinta da maganar sannan yayi mishi alk’awarin ‘bayan auren zai barta tayi karatu har sai tace bata so’,
dan ya lura burin Mahaifin nasu kenan.

D’an guntun bincike akayi akan Yahaya, a lokacin, daga nan Mahaifinta ya bashi aurenta yace masa “duk lokacin daya shirya yazo da iyayenshi a d’aura” To fa!! anan ake yinta, dan k’iri k’iri Granpa ya nuna k’iyayyar shi muraran akan Aisha da inda ta fito, a cewarshi “sam ba a jin auren d’ansa bace ita d’in!!!”. Buwayar Ubangiji, rabon Aslam, da soyayyar Granpa a matarshi ne suka tabbatar da auren Yahaya da Aisha wanda aka d’aura a k’auyen Jalingo ba tare da halartar Granpa ba.

Tabbas anyi rigima ba k’arama ba, kafin, da kuma bayan auren! Zan iya cewa ban taba ganin macen da ta sha wahala a hannun suruki kamar Aisha ba! Sauk’in ta d’aya Gramma tana mugun sonta ba kad’an ba, dan tun lokacin da Yahaya yaje mata da labarin Aisha farat d’aya taji Yarinyar ta kwanta mata, ita ta dinga lallab’a Granpa har aka yi auren.

To bayan auren ma haka tayi ta fama, in tak’aice miki labari hankalin Granpa bai kwanta da Aisha ba har sai da ya aurawa Yahaya ajin nashi da yake ik’irari! Wanda ranar d’aurin auren ana d’aurawa Yahaya yana hawaye kamar k’aramin Yaro, dan zan iya cewa ban tab’a ganin Mijin da yake matuk’ar so da gudun b’acin ran matarshi ba kamar Yahaya ba.

Sauk’i d’aya da Aisha ta samu a gurin Granpa shine haihuwar Aslam da tayi, zan iya ce miki ko y’ay’an da Granpa ya haifa a cikin shi baya yi musu kalar son da yake yiwa Aslam, ko dan ya kasance jikansa na farko ne? Allah kad’ai ya sani. Tun ranar da aka haife shi da ya d’auke shi aka tabbatar da hakan, domin kuwa kalar farin cikin da ya yi kowa sai da ya gani ya tabbatar da ‘Granpa na cikin farin ciki’!. Zakkah da sadakar da ya bayar kuwa ba na jin har yau a tarihin kaf garin Kano an tab’a bada irinta.

Aslam ya taso cikin gata, duk wani abu da kika sani Granpa ne yake yi mishi.
A tunanin kowa, Granpa zai kasance irin kakannin nan masu shagwab’a jikokinsa ne, sai dai kuma shekarar Aslam biyar a duniya aka haifi Arshaad amman kwata-kwata Granpa bai yi wani murna sosai ba ma balle aje ga maganar shagali da jan shi a jiki kamar yadda kowa ya d’auka.

Tun ranar da aka haife shi da ya d’auke shi bai k’ara d’aukar sa ba, Aslam kuwa kullum suna tare, hatta abinci tare suke ci, takanas ya nemo wani bature yake yi mishi lesson a gida, da yamma kuma wani balarabe ne yake koyar da shi addini! Sai da Granpa ya fahimci loneliness da rashin wasa da Yara agemate d’in Aslam d’in kan iya jawo mishi wani ci baya a rayuwar shi tukunna ya nemi makarantar da tafi ko wacce tsada a kaf Nigeria ya tura shi a Abuja wajen mahaifinshi, tare da kwakkwaran warning a me makarantar na “kar a tab’a mishi jika ko me kuwa zai yi! Kuma kar a bari aci zalin shi.” Duk da yana da wayo sosai dan, a lokacin shekararshi tara Arshaad hud’u Auwal kuma uku wanda shima Granpa bai wani nuna farin ciki ko tunanin janshi a jiki ba tun sanda aka haifeshi.

A lokacin ne kuma Yahaya ya sake tadawa Granpa maganar yana so ya tafi da Aisha Abuja , daman ya tab’a nunawa Granpa son yin hakan amman fur k’iri k’iri Granpa ya nuna mishi sai dai ya tafi da Mammy saboda itace tayi karatu bayan k’iri k’iri babu irin artabun da baayi da shi ba amman fur haka ya hana Aishan yin karatu a cewarsa ‘irin su In suka yi karatu gagarar mutum suke yi!’. A lokacin ya nace akan sai dai ya tafi da Mammy ita zata iya zaman Abuja wata k’ilan ma ta d’an dinga taimaka mishi ta fannin aiki, shi kuma Yahaya yace ‘ba zai tafi da ita ba! Ko da ace Aisha bata kasance uwargidanshi ba tou tabbas da ita zai tafi’. Mistake d’aya wanda Yahaya yayi kuma yake kan yi har yanzu shine ‘k’iri k’iri yake nuna fifici a tsakanin matanshi’ (k’iri k’iri yake nunawa kowa ba tare da shakkar wani abu ba ‘ya fi son Aisha a kan Mammy’.

Da kyar a wannan lokacin dan sai dai Gramma ta shiga tsakani tukunna case ya mutu, dan daa Granpa cewa yayi sai ya tafi da Mammy dole! Shi kuma yak’i.

Tou kuma da Aslam ya koma chan ma da ya sake yin maganar Aisha ta bishi, still magana d’aya irinta farko shima Granpa ya maimaita mishi ‘sai dai ya tafi da Mammy’ shi kuma yak’i. Shiyasa har yau shi kad’ai yake zaune a Abuja, yanzu haka shi da Aaima ne kawai a gidan.

K’in tafiya da Mammy da Yahaya yayi ata dalilin Aisha yasa Granpa ya rufe ido ya dinga keta mata ruwan rashin mutunci kala kala, ga Adama da Ummi suma basu barta ba, Mammyn ce ma ita bata shiri da ita kuma bata fad’a da ita. A lokacin ne kuma Mahaifinta ya rasu, Allah yaso ni nayi aure don da ban san ya zan yi ba saboda shi kanshi Mahaifin namu su uku aka haifa biyun duk sun rasu, Mahaifiyar mu kuma daga gidan marayu ma aka aurota, balle inyi tunanin zuwa gidan y’an uwa! Dan a lokacin halin da Aisha take ciki a gidan nan, ko mage bata isa ta d’auko tace zata rik’e ba.

Aslam shekara biyu kawai ya iya yi a Abuja ya d’agawa kowa hankali Akan shi fa ‘Mahaifiyarshi yake buk’ata’ Dan ba kad’an ba suna mugun k’aunar juna, kuma yana da k’ulafucin uwa ba kad’an ba, itama kuma haka, komai Aslam, shima komai Mommy.

Saboda tsabar tsananin shak’uwar dake a tsakaninsu yasa har kusan zarewa tayi lokacin da aka kaishi Abuja, Idan nace zan tsaya fasalta miki kalar soyayyar da sukewa junansu sai mu kai jibi anan.

Ba yadda Granpa ya iya haka ya tarkatoshi ya dawo dashi kano gurin Mahaifiyarshi, akan dai ya bari a tafi da ita d’in.

Sai dai kuma daya dawo d’in abun bai yi dad’i ba sam! Dan k’iri k’iri Granpa ya dinga nuna banbanci k’arara ba tare da shakkar komai ba! Abun mamaki hatta driver d’in da zai kai Aslam makaranta daban ne da nasu Arshaad.

Tun abun baya damun mutane har aka fara k’us k’us, su kansu Yaran suma suka fara fahimtar wadansu abubuwan, dan shi Arshaad ma a tunaninshi Aslam d’in d’an Granpa ne shiyasa a lokacin yake kiranshi da ‘Uncle Aslam’ a lokacin.

Ranar 12th birthday d’in Aslam ne Granpa yayi wani abun da ya girgiza mutane! Gida guda ya d’auka ya bawa Aslam as birthday gift, a Dubai! Wanda su kansu y’ay’ansa basu ma san yana da shi ba, kar ki ce k’aramin gida fa mansion ne mai zaman kanshi! Dan ko a jikin takardar wajen d’akuna ashirin ne suka fito a cikin gidan, iya d’akuna kawai!.

Mutane basu dawo daga shock ba ya cewa Yahaya “ya yiwa lawyer d’inshi magana a fara had’a takardun MT! yana so zai mallakawa Aslam su tun yanzu, in yaso shi (Yahayan)sai ya rik’e mishi idan ya kai 18 years ya bashi abun shi.”

Cikin nuna k’in amincewa Dad ya d’an fara k’ok’arin fahimtar da shi akan shekarun Aslam d’in da kuma gudun abunda hakan ka iya janyowa, K’asa k’asa ba tare da ya bari kowa yaji ba.

Amman Granpa maimakon ya fahimceshi sai ya birkice mishi, ya fara magana yana fad’a kowa yana ji!
Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba! Fad’a a ranar ba kalar wanda bai yi mishi ba a gaban taron y’an birthday.
Sai da Aslam d’in yayi kamar zai yi kuka yana bashi hak’uri tukunna aka samu ya hak’ura. Jiki a mace haka Dad ya fita ya kira lawyer ya hau kora mishi bayani.

Kusan minti talatin tukunna ya dawo ya sanar mishi lawyer d’in yace zuwa nan da jibi in shaa Allah komai zai kammala. Kaf a wajen! Y’an tsirarrun mutane da Granpa ne kawai suke farin ciki amman kowa a family d’in in ka kalli fuskarshi ba zaka iya tantance me ke wakana a cikin zuciyarshi ba, sai dai tabbas tashi d’aya zaka hango damuwa binne a k’ark’ashin komai.

Ana i gobe takardun zasu iso, wato washegarin birthday! Wani mummunan al’amari ya afku.”

Ajiyar zuciya Gwoggwo Asabe ta sauk’e kafin ta kalli sama hanyar staircase ( parlourn k’asan da yake da matattakalr staircase d’in biyu anyi tsarin wajen ne irin me high ceiling dinnan, mutumin da yake falon sama wanda ya had’a staircase d’in dama da hagu yana iya hango komai na k’asa, shima na k’asan haka, sai kuma hanyoyin dogon corridor biyu da suke kallon juna, d’aya yana a right staircase d’ayan yana kusa da left one.
Sai d’akin special guest guda biyu da yake a main parlourn sama da kuma hanyar da zata had’a ka da benen da zai kaika chan sama). Sannan ta cewa Huda “kinga chan wajen?” Tayi maganar tana kallon falon saman, kafin taci gaba da cewa “Mommy tana tsaye tana waya a jikin k’arafunanan taba d’ab lek’o k’asa. Ganin shigowar Dad Aslam da Arshaad a tare yasa gaba d’aya hankalinta ya dawo kansu tana yi musu murmushi, Arshaad ne ya hau kawo mata k’arar Auwal tun daga k’asan yana yi yana hawa benen, dan haka ta mayar da hankalinta a kanshi tana ce masa ‘ya taho a hankali kar ya fad’i…’ bata ida rufe bakinta ba dai dai Arshaad ya kusan k’arasawa inda take kawai kamar wadda aka turo sai k’ara aka ji timm!!!A take kuma ihun Aslam ya karad’e gidan gaba d’aya. Da gudu ya k’arasa inda take kwance duk da cewa ta fad’o ne bisa wasu tumtum da suke kan kafet d’in k’asan, hakan bai hana kanta zubar da jini ba! Saboda ba duk jikinta ne yayi nasarar sauk’a a kan cuision d’inba!.

Da kyar Dad ya iya k’arasawa wajen ganin yadda take kallon sama tana karkarwa yasa kawai ya yanke jiki a take ya fad’i sumamme dan shi a tunanin shi ma mutuwace zata yi.

Banda ihun kiran Mommy ba abunda Aslam yake yi, wanda hakan ne ya jawo hankalin mai gadi ya iso..
Ya dad’e ya na knocking yaji shiru ga Aslam yanata rad’a ihu dan ita Mommy a lokacin mai aikin ta zuwa takeyi tana tafiya, kuma lokacin har ta tafi , so ita kad’ai ce sai su Dad da suka shigo wanda yake a sume! Kuma akai rashin sa a suka tura k’ofar bayan sun shigo ta shiga lock!.

Arshaad kuwa, mutuwar tsaye yayi, ya k’ame k’am! In banda kallon wajen da take a tsaye kafin ta fad’o d’in ba abunda yake yi, dan har lokacin da mai gadi ya nemo mutane aka b’alla k’ofar aka shigo, Arshaad yana nan a yadda yake, da kyar aka iya janye shi a wajen aka kaishi wajen Mammy, dan kurma ya koma musu, sai da yayi kwana biyu baya magana.

A asibiti kuwa da kyar aka dedeta numfashin Dad, bayan awa biyar Allah ya bashi ikon farfad’owa, garau ya tashi dan haka hankalin mutane ya d’an kwanta, saboda a yanda jinin shi yayi mugun hawa ba wanda bai yi mishi zaton stroke ba.

Mommy kuwa da kyar aka tsaida jinin aka kuma samu ta farfad’o bayan kwana biyu sai dai kuma scan d’in da aka yi mata na kwakwalwa ya tabbatar da cewa jini ya shiga kwakwalwarta, wanda sai anyi aiki an kwashe an kuma d’inke inda ya samu rauni. Dad bai yadda anyi aikin anan ba, waje ya fita da ita aka yi komai, sai dai kuma tun kafin ayi aikin dama sun tabbatar da cewa ba lalle inta farfad’o ta dawo kamar daa ba sai dai a hankali, wasu kan iya d’aukar 1 year wasu 10 wasu 20 wasu kuma 4eva ma basu dawo normal d’in ba! But ita case d’inta minor ne so ana saka ran ma ba lalle ta d’auki 1 year d’inba in shaa Allah komai zai dawo normal.

Granpa yayi mugun sauk’owa, ko dan ganin yadda hankalin Aslam ya tashi yasa shima nashi hankalin tashi, Allah kad’ai ya sani, dan tare ma suka tafi har shi da Mammy wadda itama ta d’aga hankalinta da ganin halin da Abokiyar zaman nata take ciki, dan da Dad yak’i biya mata kud’in jirgi ma da kanta ta biya ta bisu daga baya.

Tunda aka yi aikin kuwa ita take kula da Mammy sai Dad yayi da gaske take yarda taje hotel ta d’an huta, tayi bacci.

Aslam, tunda aka yi wa Mommy aiki, yake azumi kulli yaumin, har ranar data farfad’o. Da farko b’oyewa yayi dan ya san za a hanashi, dan har yi yakeyi kamar yaci abincin sai daga baya aka fahimta, ba yadda ba ai ba amman yak’i ajjiyewa, ganin haka yasa Granpa yace a barshi, sanadiyyar azumin da yayi tayi a jejjere gashi da k’arancin shekaru ya sanyashi kamuwa da cutar ulcer.

Kamar yadda Likitocin suka fad’a, haka Mommy ta farfad’o amman a iya rayuwarta Aslam kawai ta iya ganewa, bata magana sannan komai sai an nuna mata sai an koya mata! Abu d’aya ta sani ta gane take iya fad’i, shine ‘ASLAM’.

Anji ciwon hakan sosai, amman kwarin guiwar da ake ta samu a wajen manyan Likitoci ne yad’an kwantar da hankalin Jama’a, dan suna ta bada assurance d’in ‘zata dawo normal!’

Sai dai kuma ana yin wata d’aya komai ya burkice!!! Dan Aslam d’in da ta fara fahimta sai ya dawo ya zame mata dodo!!! Da farko yana shigowa zata fara kuka!! Sai kuma ta dawo ihu!!! Daga k’arshe dai ko asibitin in Aslam ya shigo tun kafin ya k’araso inda take zata hau kururuwa tana kuka kowa ta nan ne yake gane Aslam ya iso!
Wani abun mamaki shine ta warke garau ta fara magana ta gane kowa amman fa ko a labari idan aka sako Aslam tou yanzu hankalin kowa zai tashi!!

Ba k’aramin kid’ima Likitocin suka yi ba dan su kansu sun zama confuse. A iyaka sanin su masu irin wannan matsalar basa haka amman duba da suka yi da shi ta fara ganewa a lokacin data farfad’o ya sanya suka yi y’an bincikensu, iya abunda tunanin su ya basu ne ya sanya su dangantata da psychiatric.

Allah sarki Aslam, a lokacin
sai da ta kai ga shima aka bashi gado a asibitin tsabar tashin hankalin daya shiga. Yaro ne shi a lokacin amman kasancewarshi mai kaifin basira yasa ya fahimci komai. Dan zan iya ce miki har yau ban tab’a ganin Yaro mai wayo tarin ilimi da kaifin basira irin Aslam ba, har gobe in da wani d’an ajinsu da suka yi makaranta zai zo gidannan to ba zaki tab’a ji ya kirashi da aslam ba , sai dai suce mishi ‘gifted’ Dan wani abun time d’in a makaranta ba sai an koya mishi bama yake iyawa, in kuma ya iya to ya zauna kenan! Ga wayo kamar wani d’an shekaru da yawa.”

Ajiyar zuciya Gwaggo Asabe ta sauk’e sannan ta ci gaba “A lokacin hankalin kowa a tashe yake, ni kaina da nake nan da ban ganta ido da ido tana haukan ba sai da naji a jikina, abu yak’i ci yak’i cinyewa har aka shafe wata biyu a haka, ga Aslam a kwance.
Tausayin shi da ya lullub’e Granpa gashi yana ganin yana neman mutuwa
ne yasa shi fara nemawa Aisha magani gadan gadan ba kama hannun Yaro, duk inda yaji labarin Likitan kwakwalwa nan zai tarkata su su nufi k’asar! Cikin shekara biyu zan iya ce miki sun kusa zagaye duniya dan ba k’asar da ba a je ba, in dai kinajin ta kuma sananniyace. Amman dukda haka Allah bai kawo sauk’in ba, saboda lokacin samun sauk’in bai yi ba. Daga karshe dai hak’ura suka yi suka dawo gida Nigeria.

Ai ana dawowa abun yafi na daa, ba k’aramin tsorata muka yi ba dan nima nazo a lokacin…Idan Aslam baya gidan nan to k’alau amman ko bakin MT yazo yanzu zata birkice, abun tausayi In kana nan dole kayi kuka, don Aisha mahaukaciya tuburan ta koma.

Shawara d’aya Granpa ya yanke shine na ‘kai Aslam boarding school’ don samun sauk’in kowa and ya kamata yaci gaba da karatu kuma ya maida hankali saboda an barshi a baya sosai. A lokacin shekarunshi sun haura 14.

Da kyar Aslam d’in ya yarda, ya tafi bayan Granpa yayi mishi alkawarin ‘duk inda magani yake a duniyar nan in dai akwaishi to zai nemawa Mommy d’insa, ko nawa ne kud’in ba zai gaji da biya ba, koda kuwa zai k’arar da duk abunda ya tara ne!!!’.

Haka nan aka tarkata Aslam aka kaishi boarding cikin tsananin k’unci, yana kuka muna kuka ba dan munso ba.

Wani abun takaicin ko hutu Aslam bai isa ya zo ba, sai dai In kana buk’atar ganinshi kai kaje ka ganshi a inda yake, k’iri k’iri zaman estate d’innan ya gagareshi. Ganin abun na Aisha bana k’are bane yasa suka kira wani babban Likita daga k’asar waje har gida Nigeria ya dinga kula da ita, shi ne ya bada shawarar a kulle su ita da Aslam a d’aki d’aya su kad’ai, for 24 hours, to kuma abun bai yi dad’iba don shi yayi sanadiyyar da Aslam ya bar k’asar nan wanda sai yanzu ne Allah ya dawo mana da shi!

Da farko an tsara akan zai d’an dinga lek’owa Hutu sai yake sauk’a gidan Abba, yadda ba zasu had’u da ita ba, har zuwa lokacin da Allah zai kawo sauk’i Amman abunda ya faru a wannan rana ya sanya Aslam yin yaji mai mugun tsayi ya tarkata komai nashi ya tafi sai dai waya, shima wani lokacin sai yake gudun d’auka!.

Arshaad da su Abba suna yawan zuwa duboshi, Auwal ne ma yaje sau d’aya, amman Arshaad a shekara ma yakan je sau biyu shi da Abba..saboda shi Aslam ko hutu idan anyi na makaranta baya iya dawowa sai dai yayi achan Oxford Uni inda yayi karatunshi.

Aslam a Oxford yayi karatu,
Arshaad kuma Dubai aka kaishi Auwal kuma Cairo. Da yake Granpa ne duk ya kaisu, duk da halin da Aslam yake ciki sai da aka fara k’ananan maganganu, Adama da Ummi, wai ‘har yanzu Granpa bai daina nuna bambanci ba’
Sosai Granpa da maganar ta koma mishi yayi musu tataas!!!Kuma ya taso da maganar mallakawa Aslam MT gabad’aya in yaso sai yaga me za suyi!.

Da kyar da sid’in goshi Gramma ta tausheshi, sannan ta lallabashi, sannan tai k’ok’arin fahimtar dashi abubuwan da hakan ka iya janyowa. Awannan lokacin kuwa anci sa’a ya fahimceta sosai, don da kanshi kuma ya dawo yace ‘a tsakanin Auwal Arshaad da Aslam, duk wanda yaga he’s capable to shi zai mallakawa MT’. Dad yayi mugun mugun yin farin ciki daga jin wannan decision na Granpa, ba wai yana zargin wani ba, kawai dai yaji releaf, kuma shima baya son bambancin da Granpa d’in ya dad’e yana nunawa especially tsakanin Arshaad da Aslam, don duk abun nan da ake yi ko sau d’aya Arshaad bai tab’a nuna b’acin ranshi ba, duk da kuwa uba d’aya ne ya haifesu shi da Aslam d’in, Idan akwai fitinanne tou Auwal ne! Amman Arshaad shi ba ruwanshi yana da kauda kai kunyarshi ce ma ta sanya Dad yake yiwa Mahaifiyarshi wani abun dan kar yaga ga kamar bai damu da ita sosai ba.
Kowa idan zaki tambaya a estate d’innan ya baki sheda akan Arshaad to zai ce miki ‘yana da hak’uri da kauda kai da kuma saurin yafiya’.

Aslam yana kammala degree na farko aka d’aura shi a matsayin MD na MT branch d’in dake achan k’asar da yake, wanda ada Abba ne a wajen.

Ayyuka Aslam yake yi bashi da lokacin kanshima, kuma daman hakan yake so dan hakan ya tsarawa kanshi tun farkon komawarshi UK d’in, yana k’ok’arin kullum yaga ya zama busy dan kar ma ya bawa kanshi daman yin tunani.. Aikin kuwa ya taimakeshi ta b’angarori da dama dan yana da nashi campny d’in a chan, na sarrafa takalma wanda k’wazonshi guminshi da kuma taimakon Granpa wanda yake aika mishi kud’i kamar hauka suka taimaka masa ya had’a ya bud’e
wanda yanzu naji suna cewa yana so ya bud’e wani branch d’in anan ko kuma ya dawo nan ma, gaba d’aya. Kuma akwai wani daban da zasu bud’e na zanen gidaje shi da Abba! Ga mt ga kuma karatu wanda a yanzu ya kammala PHD d’inshi


A b’angaren nasarori Aslam ya samu kam ba a magana sai dai kuma shi duk basa gabanshi, inda za ace ya tatttara ya bada abashi lafiyan Mahaifiyarshi na tabbatar kafin k’iftawar ido zai iya sallama komai!

Ba shi kad’ai ba hatta mu duk tsawon wannan lokacin buri daya muke da shi shine ‘Aisha ta warke hankalin kowa ya kwanta dan shi kanshi Aslam d’in abun a jiye mishi ne, saboda gaba d’aya rayuwarshi ya yita ne cikin fargaba, k’unci da damuwa. Yanzu haka ko Abokanai baya iya tarawa shi kad’ai d’insa yake komai sai dai a d’an dinga zumunci sama sama, Abokin shi na k’ut da k’ut guda d’aya tak a duniya wato Arshaad, da Arshaad ne kawai za kiji suna waya suna d’an raha amma ko mu y’an gida wani lokacin idan ka kirashi sai yak’i d’auka.

Tsoronma shiga mutane yake yi balle yayi huld’a dasu. Naji su Abba suna cewa, ‘Kana ganinshi in dai ka fahimci yanayin shi tou tashi d’aya zaka fahimci he’s depressed! Kuma hakan ba a so a mutum especially mai k’arancin shekaru kamar nashi, zai hanashi yin farin ciki a rayuwa ne kwata kwata, har abada!.”

A hankali tace “to amman ya za ayi? Magani in dai sunanshi magani tou ba kalar wanda ba ayi ba amman har yanzu shiru.” Ta k’arshe maganar tana share d’an hawayen daya biyo idanunta a karo na ba adadi.

Hudan, itama hawayenta ta goge, a ranta tace “Allah sarki bawan Allah, ashe shiyasa kullum yake cikin fushi, da har nake jin haushinshi.. In shaa Allah daga yau na daina jin haushinshi, Allah ya bawa Mahaifiyarta lafiya.” Maganar Gwaggo Asabe ce ta katseta jin tana cewa
“Kema dan Allah idan kin yi sallah ki dinga sakamu a addua Allah ya kawo k’arshen wannan abu.”

A hankali Hudan ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace “In shaa Allah”
Sai kuma ta gyara zamanta ta ci gaba “Amman Gwaggo a duk cikin bayaninki banji inda aka yi mata Sauk’ar Alqur’ani ba!” Cikin katse ta Gwaggo Asabe tace “anyi sauk’a Huda, Granpa da Dad da kansu suka je suka raba kud’i lokacin da suka dawo farko farko a islamiyoyi da tsangayar almajurai aka yi ta sauk’a!.”

Murmushi Hudan tayi sannan tace “Gwaggo Asabe, idan zan bada shawara a d’auka ina ga daa mu da kanmu ya kamata muyi mata sauk’ar bayan an raba a islamiyoyin, kuma in na fahimceki kamar sau d’aya aka tab’a yin sauk’ar ko?” Bata jira jin mai Gwaggo Asaben zata ce ba ta ci gaba
“Ni a lokutan baya, idan bamu da lafiya ko wani alamari mara dad’i ya afku,vTou bayan Mama ta bamu magani sai ta kammala mana sauk’a, ko lokacin da nake k’arama akwai Yayanmu da yake shaye shaye sai da Mama tayi mishi sauk’ar AlQur’ani sau bakwai!! Ta fara tayi sau hud’u ya warke ya daina amman dake tayi niyyar bakwai d’in zata yi sai da ta k’arasa. Da kuma muka yi wayo haka zata rarraba mana muna tayata da ni dasu Ya Jalila koda izu d’ai d’ai ne mu kan taimaka. Ko yanzu haka In wani abun ya faru rabawa muke yi ni da ita da Sakina wani lokacin da Sumayya, bama wata d’aya muke k’arasawa, in kuma mun kwallafa to a sati muke idawa. Balle nan gidan muna da d’an yawa. Yanzu for example ace mutum shidda kowa ya d’auki izu goma, duk bayan sallar Farilla kayi izu d’aya a kwana biyu fa za mu dinga kammalawa, In kuma izu biyu za ana yi a cikin kwana 1 mun kammala, inda hali kowa in ya kammala sai yayi mata addua dafatan waraka bayan an tofa aruwa a bata tana sha, Daga nan ayita yi, kuma akai akai. In Allah ya yarda sai kiga an dace. Dan dai gaskiya kamar yadda kika fad’a abun sam kamar bana asibiti bane ba!

Koda a ce ma na asibitin ne Sauk’ar Alqur’ani fa shine k’arshen waraka
Especially idan mune muka yi da kanmu, saboda wadannan na islamiyya ba mu da tabbas, yanzu duniya ta chanja ba lalle In sun karb’i kud’in suna sakawa anayi ba.”
Maganarta ce ta katse jin mutum a tsaye a bayanta ya dafa kanta, tana juyowa sukai ido hud’u da Dad
da Abba a bayanshi suna murmushi, wadanda shigowarsu kenan suna d’an tatauna wata magani suka ji bayanin Hudan.

Dad ne yace “y’ar albarka, naji dad’in wannan shawarar taki sosai. Kuma daga yanzu in shaa Allah zata fara aiki.
Kafin masu kwashe kaya su gama na san mun kammala in shaa Allah, na yau.” Yana gama fad’in haka ya d’au waya ya kira Arshaad da Aslam yace “su same shi.”

Sai da ya gama wayar, Hudan ta d’an zame daga kan kujera inda take ta shiga gaida Abba. Shima Dad d’in ta sake gaidashi. Cikin kulawa suka amsa mata sannan suka cigaba ta tattaunawarsu da alamun magana mai muhummanci suke yi.

Hudan sai d’ar d’ar take yi a tunaninta kar Abba yai mata fad’an abunda tayi mishi jiya, shima ya lura da yanayin ta shiya sama ya fasa zuwa inda take, amman da yayi niyyar jin yadda ta kwana da kuma jin ko akwai abunda takebso dan harga Allah shi kam yana so ya zama tare da y’arsa ya jaa ta a jiki ko sa samu su saba da juna sosai.

Arshaad ne ya fara shigowa.
Tsayawa Hudan tayi tana kallonshi dan ta manta rabon da ta ganshi da k’ananan kaya, yafi ta’ammali da shaddodi da yadi, sab’anin yau da yake sanye da wata shirt army green dark an rubuta ‘KING’ a jikin gaban rigar da zanen crown d’in king d’in ata k’asa.
Rigar irin mai d’an kama jiki ce, hakan ya taimaka wajen fito da ainahin surar jikinshi dan kana iya hango packs d’inshi na sama sama ta cikin rigar da yadda dantsen hannunshi yake a mummurd’e! Wandon nashi shima ba jeans bane yana yin rigar ne black in colour bai kamashi ba kwata kwata ta sama amman roba ne, kasancewar ya d’an matse daga guiwar wandon zuwa k’asa yasa ya zama kamar pencil trouser ta k’asan…Kayan yayi matuk’ar fito da asalin surarshi ta giant! Ga wani fitinannen k’amshi mai tsayawa a rai da yake zubawa
dan tunda ya shigo parlourn ya karad’e da k’amshin shi, tun bai iso inda suke ba. Hudan bata gama k’are mishi kallo ba suka had’a ido da shi,
gira d’aya ya d’aga mata yana d’an murmushin gefen baki, da sauri ta sunkuyar da kanta k’asa kunya duk ta lullub’eta ganin ya kamata tana kallonshi . Ganin yadda tayi ne ya sanyashi sakin wani lallausan murmushi, kafin ya k’arasa inda su Dad suke ya shiga gaidasu cikin girmamawa. Ya so ya k’arasa wajen Hudan dan shima ba k’aramin kyau tayi mishi cikin rigar abaya blueblack mai stones, d’aurin da ta yiwa kanta da d’ankwalin abayan ya yi matuk’ar burgeshi! Amman sai Dad ya tsare shi ta hanyar fara yi mishi bayani abunda za suyi ba tare da b’ata lokaci ba, 100%ya amince da kuma jinjina ga wanda ya kawo shawarar dan abunda ya kamata ayi kenan, cikin jin dad’i Dad yace “ai Hudan ce” da d’an murmushi ya juyo yana kallonta, yanzun ma sauri tayi tai k’asa da kanta, don still satar kallonshi take yi, harga Allah Ya Arshaad yayi kyau yau sosai.

Tana wannan tunanin hancinta ya fara jiyo mata wani k’amshi na daban, wanda a take ya cika mata hanci, kuma ta fahimci wanene kasancewar a kan kujerar dake gaban side d’inshi take ne yasanya ta fara jin k’amshin kafin kowa, bata san daliliba ba kuma tasan mai ya faru ba, amman ko lokacin idan anyi laifi a islamiyyarsu za a dakesu tabbas zuciyarta bata yin kalar bugun da take yi a yanzu. A hankali ta runtse idanunta ta sake yin k’asa da kanta jin takunshi a daf bayanta!Sannan bugun zuciya da k’amshin da yake shak’a na k’ara yawa. Kamar yadda Arshaad yayi shima hakan ya gaida su Dad wadanda suke ata gefe kad’an kusan hanyar shigowa sai dai shi bai k’arasa inda suke ba, hasalima zagayowa yayi ya zo kan kujerar da Gwaggo Asabe take ya zauna. Kasancewar Gwaggo Asabe a 3 seater take zaune Hudan kuma a 1, sai ya zamana kamar suna facing juna shi da Hudan! A hankali ya d’ago idanuwan shi ya sauk’e su a kanta, da tayi k’asa da kai wanda ita kanta ta kasa tantance dalilinta na yin hakan

Magana Gwaggo Asabe take yi mishi amman kamar ma baya jin ta, ganin hakan yasa ta d’an tab’a shi kad’an.
Lumshe idanunsa kawai yayi kafin ya bud’e su ya sauk’e a kan Gwaggo Asabe, d’an murmushi kad’an yayi mata kafin yace “barka da gida”.
Cike da tausayawa Gwaggo Asaben take kallonshi, ko ba a fad’a mata ba ta san tun d’azu da ya fito daga d’akin Mommy yake cikin tashin hankali!! Dan gashi idanuwanshi sunyi jaaa sosai bakinshi yayi pink shima hatta kan hancinshi yayi jaaa Amman kuma ko ba a fad’a mata ba ta san ba kuka yayi ba wanda wani lokacin har addua take yi Allah ya bawa hawaye ikon fitowa daga idanun Aslam ko ya samu ya rage rad’ad’in da zuciyarshi take ciki.

Hannunta ta d’aura akan lallausan gashin kanshi ta d’an shafa
Hakan ya sanya shi sake maida hankalinshi a kanta! Tana shirin yin magana Dad ya fara yiwa Aslam bayanin abunda ya tara su anan bayan ya zagayo ya zauna, Abba ma ya zauna. Ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e bayan ya gama sauraron Dad wanda ya k’arashe maganar shi da cewa
“Zamu fara yanzu saboda mu samu mu gama akan lokaci kafin a gama Parking su Abba su tafi” A hankali ya juya ya kalli Abba kafin yace “Abba ka bari I’ll speak with Granpa, dan Allah don’t leave.” Murmushi Abba yayi ya mik’e daga kan kujerar da ya zauna ya k’araso inda yake kafin ya dafa kanshi tukun yace “Karka damu Aslam, ai bamu da nisa anytime kake so zaka iya visiting, ni kaina i need some time with my daughter, wanda in muna nan na san Granpa ba zai barni ba, and ya dinga k’untata mata kenan, ni kuma from this time forward ina so In bata cikakken kulawa da happiness d’in da ban bata ba a baya, so we need some space from him, Daddy kuma he wants to leave ne saboda ya ci ace Granpa ya fara rage abubuwan da yake yi.

In bamu tashi mun tsaya munyi mishi haka ba, al amarin family d’innan ba zai tab’a daidaituwa ba! I hope u understand”. Yayi maganan yana shafa kanshi, a hankali Aslam ya sauk’e ajiyar zuciya a karo na ba adadi sannan ya d’auke idanuwanshi daga kan Abba wanda tunda ya fara magana ya kafe shi dasu, a hankali
yace “shikenan” sannan ya mik’e ya wuce zuwa inda ya fito yana cewa“zan fara daga Fatiha zuwa Nisa’i ayat 147!
Someone should continue from were i stop.” Yana gama fad’in haka ya shige ya jawo k’ofar shi ya zuge.

Dad ne yace “Abba ko zaku tafi tare, kasan yadda kuka saba da shi, and ga incidence d’in daya faru d’azu kar abun yai mishi yawa”

“Ba zai yarda ba but let me try”
Inji Abba, ya mik’e yana k’ok’arin shiga side d’in Aslam d’in.

Dad ne yace mishi ya tsaya tukunna.
Sai da suka tsara yadda za suyi, su mazan za suyi arba’in d’in sama, Huda kuma da Gwaggo Asabe za suyi ashirin d’in k’asa, kowa ya d’auka izu goma goma. Tukunna Abba ya nufi side d’in Aslam. Kamar yadda yace d’in kuwa sam Aslam k’in yarda yayi ya bishi hakan yasa ya hak’ura, ya zauna a d’akin yana d’an kwantar mishi da hankali, daga nan suka hau karatu a tare suka kammala nasu, dede ana kiran sallar azahar.

A chan parlour ma Huda da Gwoggwo Asabe kusan tare suka kammala, Dad ne ma da Arshaad suka d’anyi delay don suna hawa sama Mommy taci gaba da kuka da kyar suka lallab’ata tukunna suka samu suka yi nasu.

Sunyi addua sosai, kafin su samu ruwan zamzam aka tofa mata aka bata tasha aka shafa mata.

K’arfe hud’u daidai komai ya kammala, duk sun shirya kaya kuma an gama jidesu, sai y’an tsirrai da za suna kwasa a hankali a hankali, wadanda ba wani important bane!.
Abba Dad da Daddy ne suka nufi wajen Granpa don yi mishi sallama..

Har sun kama hanya Daddy ya juyo ya cewa Arshaad “yaje ya samu Auwal yace masa ya kawo wannan Yarinyar nan sannan ya tabbatar komai d’inshi ya zama ready dan suna fitowa za a tafi” Da to ya amsa har ya juya ya nufi k’ofa ya jiyo wadda ta biyo shi da d’an sauri tana ki ranshi a hankali ya juyo yana kallonta. Sai da ta k’araso ta d’anyi k’asa da kanta tana wasa da y’an yatsun ta tukun tace “Ina wuni.
Dan Allah ka ara mini wayarka zan kira Mama”.

B’ata rai yayi kafin yace “Nima ba zan kulaki yanzu ba”. Yana d’an turo baki kamar wani k’aramin Yaro.

Dariya ma ya bata dan haka ta d’ab yi y’ar dariya mai k’aramin sauti kafin ta ce “To ka yi hak’uri naga su Abba ne shiyasa kuma ka d’an yi nisa ne, da kana kusa da sai mu gaisa”. Murmushi kawai yayi ya mik’a mata wayar sannan ya ce “bara yaje ya duba Auwal kar suyi ta jiranshi…”

Huda ba k’aramin tashin hankali ta shiga ba da jin Mama na asibiti an sake admitting d’inta har yanzu, Sakina sai k’ok’arin kwantar mata da hankali take amman taki hak’ura, barema da taji wai an mata har eco, gashi ance Maman tana bacci ba zai yiu suyi waya ba!! Kwata kwata sai ta gaza kwantar da hankalinta, dan haka kawai tabi Ummu da ‘to’ bayan tace mata tayi hak’uri ta d’an Kara jira Amman tasa a ranta yanzu zata samu ya Arshaad ya kaita emergency d’in…

Tana cikin wannan tunanin bayan sun gama wayar, wayar Arshaad ta hau k’ara!

Kiran shi akeyi akai akai, gashi ya fita.
Ganin an jera mishi sama da 20 misscalls ne ya sanya ta yanke shawarar kai mishi wayar.

A bakin gate d’in gidan ta tambayi mai gadin ko “Ina Arshaad d’in yayi?”
Opposite gidan da yake kallo wanda take ya nuna mata, dan haka ta nufi gidan.

Tun lokacin da Auwal ya dawo daga wajen Mom ake kai ruwa rana da Jalila har yau da suke shirin barin gidan!
Dan tace “wallahi ba zata je wajen wata Gwaggo Asabe ba, kuma ba zata koma gidansu ba! Ta gano wayo yake so yayi mata ya yakiceta, ai tunda babanshi yace baya sonta ta san in dai ta yarda suka bar gidan babu ita tou shikenan magana ta k’are” Bikin ma cewa tayi “ta fasa zuwa” gashi ta amshe kud’i, ta ce “sai anje sabon gida an nuna mata d’akinta ta zuba kayanta tayi settling tukunna maybe taje”
Tace kuma “In ya tilasta mata a yau sai ta tona mishi asiri, wallahi.”

Auwal kamar yayi hauka, gashi an gama kwashe kaya ya san shi kawai Daddy yake jira ya kai Jalila sannan yazo su tafi, ga kuma batun ta na zata tona mishi asiri, kar fa Yarinyar nan ta jik’a mishi aiki!! A daa yana underestimating d’inta yanzu kam ta fara bashi tsoro gaskiya, he has to do something, duk da cewa Mom tace mishi ‘ya jira ta tana dawowa zata yi maganinta’ amman gaskiya he cant wait!! Yana tsoro kar kwab’arsa tayi ruwa, gara kawai ya k’are komai dan shi gani yake ma it’s like sun rabu da Arshaad d’in tunda ta same shi dan haka tayaya zai iya breaking d’inshi!!!
Takaici ya taru ya yiwa Auwal yawa, ga Jalila sai maganganu take yab’a masa. Da kyar ya iya controlling kanshi dan ji yake yi kamar yaje ya rufeta da duka ko ya samu sauk’i!
A hankali very calm ya k’arasa inda take ya kamo hannunta Da sauri ta fisge hannun kafin tace, “Ai wallahi anyi an gama babu k’ari!! Mayaudari kawai, haka kurum ka cuceni! Ga wasu zantukanka waenda har yau na kasa fahimtar alk’iblarka a kaina..”

Cikin tsananin fushin da ya kasa dannewa yace “na cuceki ko kin cuce ni?? Ke kin San ko waye ni kuwa? Wallahi ba dan abunda na shirya akan ki ba ko a y’ar aiki ba zan tab’a yarda ki zo mini ba! Kina magana kamar irin dole d’innan nayi miki, Ina ce da yardarki kika bini har gidan?
Zaki wani rainawa mutane hankali, wallahi ki bini a hankali tun ban fito miki a asalin Auwal d’ina ba!!
Magana kad’an In anyi kice wani ‘za kije ki tona min asiri’ To bari kiji, tsaf! Zan iya cewa Daddy na maidake gida! In kulle ki anan yunwa ta kasheki daga baya in zo in fitar da gawar ki babu wanda zai ji labari, tunda itama uwarki kwad’ayi ya rufe mata ido ai bata cewa kowa kina nan ba! Stupid useless girl kawai! Banza wadda bata da daraja kwata kwata, Akuya ma ta fiki daraja tunda ita wani lokacin tana guduwa tana jan aji, ke kuwa ana ce miki kule za ki ce cass!.”

Takaici da tsoro ne suka sanya Jalila fashewa da kuka, wani irin takaicin Umma take ji yana taso mata..
Shiyasa fa ita tayi ta dodging, har ga Allah irin rayuwar nan da yadda ta yarda dashi nan da nan ba hakan ta tsarawa kanta ba! Ita dai ta san tanada burin son auren mai kud’i, amma
kalli yanzu yadda ta koma, duk ata dalilin biyewa son zuciyar Umma, gashi ta hanata zubar da cikin, kamar ba ita ta tsugunna ta haifeta ba!
Tunda take ba a tab’a yi mata zagin daya girgiza taji haushinshi ba kamar kalar zagin da Auwal yake yi mata especially na yau dan ko ranar daya maidata gida bata ji ciwon zagin kamar na yau ba, kuma gaskiya ya fad’a!. Gashi yadda taga ya birkice tabbas zai iya aikata abunda ya fad’a d’in… Kuka take yi bil hakk’i da gaskiya. A take ta gama tsarawa kanta zata ce a zubar da cikin kawai ta koma wajen Umma, kowa ya huta.

Ganin yadda tayi ladab ne ya k’ara bawa Auwal kwarin guiwar aiwatar da abunda kwakwalwarshi ta shirya mishi yanzun nan, dan haka ya k’arasa inda take tsugunne shima ya tsugunna, fuskarshi ba alamun wasa yace
“Look Jalila, let’s just get this done over with… Zan baki 5 million”. Da sauri ta d’ago manyan idanuwanta tana kallonshi. D’aga kanshi yayi alamun ‘yes’ sannan yace “Miliyan biyar!”
All I want you to do is ‘Ki ce cikinnan na Arshaad ne, kuma in sama da k’asa zasu had’e kar ki chanja maganan ki, ko a gaban waye, ke hatta uwar data haifeki ina so ki birkice mata kice na Arshaad ne kawai!’ Gaskiyar Maganar ya tsaya daga ni sai ke. Kar ki damu In komai yazo gangara ni zan san yadda zan yi, komai zai fita normal, ba zaki samu wata matsala ba, understood???”.

Rarraba ido ta fara yi tana k’ok’arin yin magana, suka jiyo sallamar Arshaad. D’agowa sukayi dukkansu suna kallon hanyar shigowa. Cikin takunshi ya k’araso cikin parlour…

Wani killer smile Auwal yayi kafin ya mik’e tsaye yace “D’an halak! Maganar ka muke yi”

Cikin nutsuwa Arshaad d’in ya k’araso inda suke, kallon Jalila yayi yaga yadda take kuka, a ranshi yana mamakin ina Auwal ya samota haka, gashi sai kuka take yi. Ganin ba wannan ne ya kawo shi ba yasa ya d’auke idonshi a kanta ya maida kan Auwal d’in sannan yace
“Daddy is waiting, infact everyone, for you, kayi sauri dan yace karka bari yazo ya sameka a nan!” Yana gama fad’in haka ya juya ya fara k’ok’arin fita.

Da mamaki Auwal yake kallonshi da Jalilan wadda tunda Arshaad d’in ya fara magana take kallonshi, Ganin Arshaad d’in na shirin fita ba tare da ya ma sake kallon Jalilan ba yasa Auwal yin ta maza ya zagaya ya tsaya a gaban shi sannan yace “Saurin me kake yi? I’m just trying to clean up your mess here fa, amman kayi kamar ma baka santa ba, ko In barta ta tafi wajen su Abba ne?”

D’an dakatawa Arshaad yayi sai kuma ya juya yana kallon Jalilan. Da ido Auwal yayi mata signal d’in da ta kasa ganewa, ita dai kawai sai ta mik’e, kamar an tsoma ta a ruwa jikinta na d’an rawa.

Murmushi Auwal d’in yayi sannan ya zagayo yace “Talk mana Jalila, ko tsoron shi kike ji yau kuma?”

Kame kame Jalila ta fara yi, ta rasa ta Ina zata fara dan Bata san me zata ce ba, gashi duk da halin da take ciki tunda taji Auwal ya ambaci miliyan biyar ta rikice, hali zanen dutse!.
Don haka tace “da man nazo ne akan maganar mu” Tayi maganar jikina na d’an karkarwa dan har yanxu k’irjinta bugawa yake yi, yau ce rana ta farko data tsaya ta k’arewa Arshaad kallo!!
Ita dai tun lokacin da yake zuwa wajen Hudan ta san yana burgeta kuma yanayin shi, maganarsa, tsayi da k’amshin turarenshi suna mugun k’ara kid’imata! Kawai dai ita ta san tana so Arshaad har cikin zuciyarta, amman yau data tsaya ta k’are mishi kallo ta sake rikicewa kuma ta tabbatar idan har bata sameshi ba to ko dai ta mutu ko kuma ta shiga hauka…

K’irjinta in banda bugawa babu abinda yake yi, gashi ya tsareta da dogayen shanyayyun idanuwanshi, cikin tsare gida yace “Wacce magana kenan?? Do i know you?”

Wata dariya Auwal ya saka kafin ya k’araso yana cewa “Okayy!! Bari in yi maka dalla dalla. Maganar cikinka wanda ke a jikinta! Shi ta biyo ka ku k’arasa.” Arshaad zuwa yanzu yazo wuya! Don haka ya yanke shawarar cin uban Auwal dan ya lura bayan rainin hankalin da yake yi mishi, harda hauka ma ya fara damunshi kwana biyu, gara a yita ta k’are ko zai dawo hankalin shi, in hauka ya za ayi ya d’auko Yarinyar da bai tab’a ganiba a rayuwarshi ya hau yi mishi wani maganan banza da wofi??!

A fusace ya juyo yana shirin yin kan Auwal, suka ji k’arar fad’uwar abu, da sauri duk suka juya suna kallon k’ofa..

Arshaad, ya san yana da gaskiya amman kalar kallon tuhumar da Hudan take yi mishi da kuma yanayin fuskantar, ne ya sanya gabanshi yayi mugun fad’uwa sannan wata zazzafar zufa ta hau keto mishi, tabbas ya san taji shirmen da Auwal ya gama fad’a yanzu. Auwal kam tsayawa yayi yana kallonta yana mamakin tsananin kamanninta da Abba da Aslam! “Who’s she!?” Ya fad’a a hankali ba tare da kowa ya jishi ba. Chan kuma sai ya tuno da case din y’ar gidan Abba da har ta kaiga kulle su Mom d’inshi a cell! Ai take kwakwalwarshi ta d’au chaji, don haka a zafafe ya nufeta, daman neman ta yake yi ya kora mata warning!! Jalila kuwa tsorone ya rufeta ganin Huda, a tunanin ta Umma ce ta fad’i inda take, su kuma suka zo har da su Kaka tafiya da ita, dan haka karkarwar jikinta ya tsananta ba abunda take tunawa irin auren ta da Mati mai wanki ta san yanzu kam babu fashi!.

Cikin zafin nama Auwal yana karasawa inda Huda take tsaye yace
“Hey! Couz… You must be Huda right?
Inaso kije ki samu uban ki kice mishi….”Cikin katse shi Arshaad wanda shima ya k’araso inda take yanzun yace “Huda lets go don’t mind him, he’s crazy!! Muje kawai za mu yi magana a waje.” Ya k’arashe maganar yana durk’usawa don k’ok’arin d’aukar wayarshi data jifar a k’asa.

Hudan ita kanta bata san tana da kishi irin haka ba, sai yau. Wato ba zai ma iya fuskantanta a gaban Jalilan ba?!
Gashi yadda duk ya rikice jikinshi yana d’an karkarwa yasa ta d’aura ayar tambaya akanshi…Ita Arshaad zai yiwa haka? Why? Of all people kuma yayarta!!! Ba ta san lokacin da ta fashe da wani irin kuka ba!.

Ai kuwa a rikice, Arshaad yace
“Oh nooo, Huda dan Allah kar muyi haka dake mana, na rantse miki da girman Allah ban san wacece waccar ba! Ban tab’a ganinta ba a rayuwata, wallahi! Muje waje we ‘ll talk outside.”
Yai maganan yana k’ok’arin kama hannunta..

Da sauri ta fisge cikin kuka tace
“Don’t touch me! Ai dole kace baka santa ba mana, Ya Jalilan ce baka sani ba? Daman Mama tace min rannan kaje kana nemanta, kuma nima naji Umma ma rannan suna wani magana da Anty Zainab dana kasa fahimta a kanka kaida Ya Jalila. And if baka santa ba mai take yi a nan ya aka yi ta san gidanku da ni kaina ban sani ba?
Ana tunanin tana gidan Anty d’inta a gida ashe tana wajen ka! I trusted you,I tot.”

Arshaad kam zuwa yanzu ranshi yayi mugun b’aci dan a tunaninshi ko Sakina ce zata fad’awa Hudan wannan maganar a kanshi bai ci ache ta yarda ba, balle a bakin mutumin da bata tab’a gani ba sai yau! Dan haka cikin katseta yace “Ba ki yi trusting d’ina ba Huda! Tunda gashi har kin d’auki maganan da aka fad’a miki a kaina.
Rantsuwa ta k’arshe da zan yi miki shine ‘wallahi ban san Yarinyar nan ba!’ Mutum d’aya na sani a gidanku age mate d’inki itace Sakina. Kuma ban san wanne Arshaad d’inne yaje nemanta gida ba rannan d’in da kikace, amman bani bane ba!. Maganar su Umman shima i don’t know anything about it, wallahi!.
Anyways na gode da irin shaidar da kika yi mini. Hudan aure za muyi ya kamata ace kinyi trusting d’ina tunda as far as i know inda ace ni d’an iskane da tuni ke zaki fara fad’a ba wai ita ko shi ba.” Yana gama fad’in haka ya juya ya fita dan in ya ci gaba da tsayawa a wajen zai iya yin abunda zai yi ending up yana regretting…

A hankali Hudan ta k’arasa ciki wajen Jalila ta kama hannun ta kafin tace
“Ya Jalila” Cikin kukan makirci Jalila ta fashe da kuka ta rungune Hudan kafin tace “Hudan Allah da gaske ne abunda Auwal ya fad’a yanzu, gashi na kasa fad’awa kowa, ban san ya zanyi ba! Arshaad ya cuce ni.” Ta k’arashe maganar da wani mugun kuka, don ta lura Hudan ta yarda da ita, duk da kuwa har yanzu tana cikin rud’u akan ‘’me Hudan take yi a gidan’ Dan kalaman Auwal da yadda yace mata cousin ya sake dilmiyar da tunanin ta…Amman yanzu ba wannan ne a gabantaba, raba Hudan da Arshaad shine first! Ga kuma zancen miliyan biyar! Don haka dole ta ajjiye komai a gefe ta duk’ufa ta cimma burinta.

Da kyar Hudan ta lallasheta, ta samu tayi shiru, rasa abun yi yasa Huda tace mata “bara taje ta dawo” da taso ta tafi da ita, amman tak’i, dan haka ta mik’e ta ce “tana zuwa, tukunna sai su san me za suyi”

Cikin share ragowan hawayenta ta d’agawa Hudan kai, Hudan kuma ta fita a zuciyarta tana rayawa yanzu zata kira su Ummu dan ba zata iya wannan abun ita kad’ai ba! Dole a kwatarma Jalila hakk’inta, tana tafe zuciyarta na tafarfasa, ita kawai idonta ya rufe da kishi har ya kaita ga kasa yin lissafi mai kyau a kwakwalwarta.

Jalila na ganin fitar Huda ta share hawayenta ranta fess! Sannan ta mik’e ta k’arasa inda Auwal ya daskare yake k’ok’arin hada 1+1 akan alamarin da ya gudana yanzun nan dan in dai shi ba dak’ik’i bane ba tou abu na farko daya fara fahimta shine ‘Arshaad Huda yake dating!’ And tabbas bai san Jalila ba, to who. Muryar Jalila wadda ta k’araso yanzu ne ta katseshi jin tana cewa “Nayi duk abunda kace, yanzu abunda nake so da kai shine ka kawo miliyan d’aya, ragowar kuma in aiki ya kusan kammaluwa, dan…” Shak’ar!! Da yayi mata ce ta katse mata maganar tata, cikin d’acin zuciya da k’arfi yace
“Who are you?”.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< So Da Buri 38So Da Buri 40 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×