Abdullahi ya Soma Fadin.
"Allah ya Saka min Kaunar Yara a Rayuwa ta. k'ananan Yara suna Debe min kewa shiyasa ban iya boye soyayyar Ya'ya na ba a ko Ina ba nawa kawai ba duk inda zanga yaro musamman Mai shirmen kuruciya ko Mai k'iriniya ko Mai yawan tambaya Ina Jin son sa da Kaunar Sa a Raina. Tun Lokacin kuruciyar Najwa da Nabeela idan Basma Zata Fadi gaskiya ta Kuma Yi min Adalci ta San yadda nake son kasancewa tare da yaran . Ko na Saka su mota Nayi ta zaga gari da su duk inda zanje. . .