Kukan Yusra ya tab'awa ishaq ZUCIYA ya Dube ta tana zube a Gaban shi tana Fadin.
"Don Allah don ANNABI Abba ka yafewa mamar mu tace na Rok'a Mata gafara wurin ka ka yafe Mata don Allah don ANNABI ka yafe Mata Wallahi Bata da lafiya Abba har tana ce min mutuwa Zatayi Abba in ta mutu Yaya Zanyi? Ta fada cike da tabbaccin Abinda ta fada tana tsananta kukan ta.
Tausayin ta yayi matukar kama ISHAQ ya kama ta Yana Fadin
"Daina kukan Nan Yusra ADDU A Zakiyi Mata ba zata mutu ba kuka Baya maganin komai. . .