Sati biyu bayan wannan lokacin ya dawo gida ya zo ya same ni na yi kuka har idanuwana sun kumbura ko abincin dare rannan ban fito na dora ba.
"Lafiya dai na same ki a haka?"
Ina kuka na ce mishi, "Wani abu ne yake yi mini motsi a ciki."
"A ciki?" Da sauri ya yi tambayar na ce mishi, Eh." Ya nemi wuri ya zauna ya dora hannu a cikin nawa yana kokarin jin motsin da na gaya mishin, sai kuwa ya ji. Ya kalleni cikin nutsuwa ya ce,
"Anya kuwa ba ciki ne da ke ba kuwa Zuwaira. . .