Skip to content
Part 25 of 49 in the Series Wace Ce Ni? by Hafsat C. Sodangi

Na sha kwalliya sosai, an yi mini gyaran jiki na ban mamaki, an kuma kawata jikin nawa da adon lalle mai kyan gani, ga wasu kaya na alfarma da Hajiya ta sanya mini. Sannan ta dauko mayafi ta lullube ni ta kuma wuce gaba tana rike da lullubin nawa ta yadda babu mai iya ganin komai nawa. Ta wuce muka shiga ni da ita mota, muna baya direba shi kadai a gaba ya ja muka bi bayan sauran motocin da aka basu umarnin su fara tafiya.

Sannan wasu suka biyo bayanmu. A haka har muka isa gida. Wajen karfe tara na dare aka saka mana lalle gaba dayanmu a wuri daya aka hadamu aka sanya mana. Muka kuma kwana wuri daya.

Washe gari da safe ta ko’ina dirin mutane kake ji alamar dai gidan a cike kwarai yake. Gaba dayanmu mu shidan muna nan a dakin kowacce ta shiga cikin nutsuwar ta ni dai babu abin da ya tsaya mini a rai irin kewar rabuwarmu, shi kenan zaman tae ya kare, sai kuma zumunci abin da kullum Ummana take gaya mini kenan.

Ina cikin wannan tunanin sai ga Hajiya ta shigo cikin wata irin kwalliya ta kasaita tasa katon mayafinta ta rufe ni ta yi waje da ni.

Sashin Ummana ta kai ni a wani daki da babu kowa a cikin shi muka shiga ta ce, “Shiga ki yi wanka ki fito ki shirya, don mu karbi Fatiha tare.” Na fito daga wanka hajiya ta tasani a gaba tana shafa mini mai tana dariyar abin da ke faruwa a falon Umma, inda wasu suke tambayar ina uwar Zubairu? Ta yi maza ta ce, “Gani nan.”

Suka gaya mata abin da suke nema, ta sa aka yi musu. Ba ta zauna ba sai ga wasu sun iso.

“Uwar Junaidu muke nema.”

Ta ce musu, “Ni ce.”

Nan suma suka kama bayani. Hajiya ta gyada kai a hankali ta ce, ‘In kika gama wannan bikin mijinki ne zai ji jiki da ke, mu duk gudu za mu yi mu bar mishi ke.”

Kwalliyar amarci sosai Hajiya ta yi mini.

Karfe goma sha daya daidai aka fara daurin auren ina kwance a jikinta ina sauraron abin da ke

faruwa cikin zuciyata ina cewa, yau ne zan tabbatar tsakanin ni da yaya Almu  wa ke da Baba a matsayin mahaifi? Gabadaya sai da aka yi daurin auren guda biyar gaba daya kuma mutane daban-daban ne suka bayar ko suka karba. Sannan sai na ji ana cewa, “Ina wakiyar Rabi’atu da wakilin Mustapha, mai bayarwa da mai karba kenan” Sai na ji ana cewa, To ya yi gasu nan sun zauna, Alhaji Bello Mustapha, uban ‘yar gabadaya uban angwaye da amaren duka shi ne da kanshi zai bayar da auren Rabi’atu yayin da Amininshi Alhajin Malle żai karbarwa Mustapha auren.”

Ina jin haka na ce shi kenan na rasa baba a matsayin mahaifi na san babu yanda za a yi Baba ya haifen. Sannan ya zauna ya bayar da aurena a gaban ‘yan’uwanshi da abokanhi bai wakilta wani ya ce ya yi mishi hakan ba. Hawayc suka zubo mini sharr! Ana shafa Fatiha Hajiya Hauwa ta kalleni ciki nutsuwa ta ce, “Yau din nan ranar farin cikin uwarki ne. Ban yarda ta ga hawayenki ba, ta kuma ga bakin ciki iri-iri, don haka taimaketa ta girbi alhcrin hakurinta, koma me ke cikinki watstsake mu yi shagalin bikin tare, hankalinmu kuma a kwance.”

Kalaman Hajiya suka kara fahimtar da ni cewa bai kamata in bari Umma ta san halin da nake ciki ba a yanzu. Ana ta hidimar biki ta ko’ina sai tashin kida kake ji amare suna can a tsakar gida suna ta faman cashewa, angwaye da abokansu suna ta yi musu kari.

Ni kam ina daki kwance a jikin Hajiya sai kukan sharbe nake yi, babu abin da ke kai kawo cikin zuciyata sai tambayar wane ne mahaifna? Shin yana raye a duniya ko ya mutu? Shin da gaske Umman ce ta haifen ko kuwa ma ni din ‘yar tsintuwa ce,  tun dama gashi wasu na yi mini łakabin shegiya. To in kuwa ni shegiya ce ai na tabbatar ba Ummana ce za ta yi wannan cikin shegen ba, na san darajarta ta ta wuce hakan.

Sau biyu ana aikowa wai a fito da amarya ta yi rawa, sai kawayen Umma da ke falo su ce a’a a je a gaya musu wannan amaryar ba mai rawa ba ce, ba ta iya ba.

Da daddare misalin karfe takwas aka fara tafiya kasaitacciyar liyafar da Baba ya shirya, don taya shi murnar auren ‘ya’yanshi da ya yi. Ni kam ko goggoron da amare ke sanyawa ban saka ba, katon gyale kawai Hajiya Hauwa ta miko mini na yi lullubi da shi, hakan nan da abokan yaya Almu suka nemi a ba su ni in tafi tare da ango kamar yanda aka yi wa sauran angwayen, hakuri hajiya Hauwa ta ba su ta ce musu su je za ta kawo musu ta su amaryar.

Wurin liyafar ya kai ya kawo ko iyakacin abin da Baba ya kashewa liyafar shi kadai ya kashe ya isa a ce ya kashe kudi. An yi matukar kawata wurin, abin ba a magana. Angwaye da amarensu suna kan high table ni kam ina zaune tsakanin kawayen Ummana Hajiya Hauwa da Hajiya Furera don su suka zo da ni daga inda muke zaune, ina kallon kowa ina hango Umma farin cikinta a bayyane yake, shi ma Baba haka.

Na zuba mishi ido ina kallonshi cikin zuciyata na ce, wannan wane irin mutanne mai iya maida dan wani ya zama na shi? Ina cikin wannan tunanin aka fara bude taro da addu’a aka yi ta gabatar da abubuwa iri-iri kamar yanda aka tsara su. Zuwa can sai aka nemi mutum daya a cikin angwaye ya wakilce su ya yi jawabi. Yaya Junaidu ne ya yi hakan. Da ya gama.

Ya zauna sai aka nemi wata daga cikin amare ma ta tashi ta yi magana a madadinsu. Ban bata lokaci ba na mike cikin lullubina har kasa hawaye suna zuba a idona na bude jawabin nawa da doguwar addu’ar da ta sanya gaba daya mutanen wurin suka shiga cikin nutsuwarsu. Na yi wa Annabin Rahama salati. Sannan na yi sallama ga ‘yan’uwa Musulmi, wanda gaba daya dakin ne suke amsa sallamar, saboda hankulansu sun riga sun dawo gareni. Na fara gabatar da godiya cikin harshen turanci amadadin da sauran amare duka ga iyayenmu da daukacin jama’a maza da mata, wadanda suka taimaka wajen ganin komai ya tafi kamar yadda aka tsara shi. Sannan a karshe na ce, zan sake mika tawa godiyar ta musamman ga iyayena guda biyu da na sani a matsayin uwa da uba, wato Umma da Baba.

Na ce iyayen da suka rike ni, wani irin riko da ya shagaltar da ni daga tunanin ‘WACE CE NI’ sai a yau din nan na bayar da bayani na yarda na girma gabansu, ban taba tunanin iyaye ba, saboda tsananin gatan da suka yi mini.

Na fadi yadda zuciyata ta yi ta kai kawo a lokacin da Baba ya ce zai hadani aure da mutumin da nake ganin ni da shi duk daya, ma’ana dukkanmu ya’yanshi. A karshe dai na ture shi gefe na kuma yardarwa kaina cewar ni ce ‘yar baba ta cikinshi, sai a yau din nan da gaskiya ta bayyana.

Dakin ya rabu biyu wasu suna tausayin jawabin nawa, wasu kuwa dariya suke yi. Na kalli Wurin da baba yake zaune na ce mishi, “Godiya mai yawa gare ka ya kai Babana, har abada ni a wurina kai ne mahaifina.

Na koma na zauna ina zama sankiran da ke gabatar da abubuwa ya mike cikin ajiyar zuciya mai karfi ya ce, Wohoho! Ga wani jawabi mai ban tausayi jama’a kalubalane mu mutane nawa ne suke iya yi wa ya’yan da ba na su ba ne irin rikon da yarinyar nan take bada labarin an yi mata? Ko ni in ban da ita da bakinta ta fada da tambayata aka yi in fidda mutum daya tsakanin ita a angon nata wane ne dan Alhaji Bello na cikinshi ita zan zaba.”

Yana gama maganar cikin raha gaba daya dakin aka kwashe da dariya, ya tsaya yana Kallon kowa tamkar ba shi ne ya yi abin dariyar ba. Sai da ya ga an nutsu. Sannan ya sake cewa,

To kalubalenmu mu iyaye. Yanzu kuma za mu sake neman wata daga cikin amare ta yi mana karatu Alkur’ani mai girma kafin mu rufe taron da addu’a.”

Ganin da na yi amaren ba su motsa ba, ya sa na sake mikewa na karanto ayoyi goman karshe na cikin suratul Bakara. Sannan na koma na’ zauna. Ban san me, Baba yake radawa Umma ba, na dai hange su ne yana gaya mata wani abu a kunne, ita kuma ta sunkuyar da kanta kasa, sai murmushi take yi.

Mun fito daga wurin liyafar bayan an rufe taron da addu’a Hajiyá Hauwa tana rike da ni za ta shigar da ni cikin motar da muka zo a ciki, don mu koma gida. Sai na ji yaya Almu yana ce mata.

“Hajiya kin manta ai nine zan tafi da amarya.”

Ta yi maza ta ce, “Haka ne Mustapha mantawa na yi.”

Ta yi maza ta juya ta sakani çikin motar da yake tsaye a cikinta kan in ce komai har ya yi maza ya shige ciki ya zuge gilasan ta bakake ya rankwafo da kanshi jikina ya ce, yau iyaycn baba sun sake haduwa. “

Yana fadin hakan ya saki wani kyakkyawan murmushi ya ce, Ai kin riga kin yi sallama da Umma,Baba ya riga ya sallame mu ya ce kowanne ango yana da ‘yancin tafiya da amäryarshi a yau. Junaidu yanzu yana hanyar airport ya nufa ya ce jirgin dare zai bi a gidanshi zai yi angwancinshi, nima ban samu jirgin ba ne mai zuwa Kaduna yanzu da daddare, amma duk da haka muna da daki.”

Ya dauko dan makullin ya nuna mini. Sai da na ji gabana ya fadi, ya sake kallona ya yi wani murmushin ya ce, yanzu can za mu don ki gyara mini shimfida.”

Na ce, “Haba yaya Aimu auren da aka daura yau shi ne har za ka fara kira mishi irin wannan maganar?”

Ya bata-rai ya ce, To bari in jira sai badi.”

Na ce, ‘A’a ba haka nake nufi ba, amma dai kasan, ina da matsala da Umma, ina son ganinta don ta gaya mini wance ne mahaifina?”

Ya ce, “Ni ba ni da matsala da ita a kan wannan tun da ni a sanuna mun riga mu warware. Na ce ni na bar miki Baban, kuma ke ma dazu anan kin yi magana mai dadı’ cewar shi ne mahaifinki na har abada, to ba shi kenan ba?

Na ce, “A’a yaya Almu.”

Ya yi maza ya ce, ‘A’a kar mu bata lokaci a kan wannan na vi miki alkawari nan da wata uku zan kawo ki ki ganta, in ya so lokacin sai ta yi miki wannan bayanin.

Nan ce, ‘To gaskiya ni ban yarda da zuwa wani wuri ba mu je gida kawai.

Ya sake zuge gilas ya cewa direba shiga ka kai mu gida.

Muna shiga dakin na su al’amura suka sauya, abin da ban taba tunani ba kwana daki daya da yaya Almu bai zame mini komai ba an yi hakan ya fi a kirga, ban taba ganin ranar da ya dora hannunshi a jikina ba. Na yi kokarin kwance kaina daga gare shi na kasa, na kalleshi cikin haki na ce mishi.

Zan yi maka ihu ga su yaya Musa nan a dakin can su jika.”

Da ya dan saurara yana jn maganata yana jin abin da na fadi. Ya ci gaba da abin da yake yi yana cewa, “In ihun ya dame su sai su bar wurin, amma ni kam ai ba ni da matsala, don na dade da sanin cewar daren farko sau da yawa ba girma da arziki ake yin shi ba. “

Ganin da na yi ya kusa yin galaba a kaina, don tuni ya riga ya gama zubar da kayan jikina ya sa na fara rokon shi.

“Kar mu yi dambe da kai yaya Almu, kar ka ce za ka nuna mini karfi wanka kawai za ka bar ni in yi shi ne matsalata, don in ji dadin jikina.”

Yana jin haka ya yi maza yay tsallake ya ni ya nufi bandaki don shirya mini ruwan wankan. Nima na yi maza na suri sabon tawul din da ya wurga akan kujera lokacin muka shigo na daura a kirjina na yi a hankali na bude kofa na yi waje da gudu. Wurin Ummana na nufa. Na yi sa’a wurin nata a bude yake daga nesa kana jiwo kamshin da ke fitowa daga cikin shi, ita kadai ce a ciki tana zaune gaban madubinta wai gyaran jikinta take yi. Tana ganina ta saki baki tana kallona cikin mamaki ta ce, “A daren nan Adawiyyah ga hadari me ya hana ki tsaya ki bai wa mijinki hakkinshi?”

Ina jin wannan maganar tata na fashe mata da kuka na ce, “Umma!”

Ta ce, ‘Eh to mene ne Adawiyyah? Nima wurin mijina nake shirin zuwa me zai hana ke ma ki je wurin na ki mijin in ya so da safe mun hadu duk wata magana da kike son mu yi sai mu yi”.

Ina kukan na yi mata rantsuwa na oe, “Umma ba zan taba sauraran yaya AlImu ba. Ba zan taba bashi hadin kai ba. Ba zai samu abin da yake nema a wurina ba, har sai ranar da kika yarda kika gaya mini WACE CE NI?

Umma ta zuba mini ido cikin nutsuwa, kallona take yi. Wani irin kallon da, ban san me yake nufi ba.

Zuwa can ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Ya zama dole in gaya miki ke wace ce? Tun da an riga an yi iska asiri kuma ya tonu.”

Mu tafi littafi na uku don jin wace ce Rabi’atun

<< Wace Ce Ni? 24Wace Ce Ni? 26 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×