Washe gari kuwa da safe sai na ji shigowar Yaya Almu wurin Umma. Bayan sun gaisa sai ya ce mata,
"Umma da za ki amince da sai yan matan gidan nan su karbi aikin abincin daga hannun Baba Maigyada ita ta zama tana sa musu ido ne kawai, amma ba ta rinka yi ba."
Umma ta dan jinjina lamarin kafin ta ce mishi, "Abincin baya dadi ne?" Ya ce, 'A'a Umma mun dai gaji da cin natan ne.
To kawai ita ma ta dan huta ai ta girma tun muna yara fa muke cin abincinta."
Umma ta yi murmushi. . .