Skip to content
Part 1 of 4 in the Series Yasmeenah by Deejasmaah

Prologue (Thriller)

Rungumeta yayi ta baya yana mai lumshe idanu, k’amshinta yake shak’a cikeda so. Murmushi ta yi cikin shagwab’a da soyayya tace ” good morning Noorie” Morning ya amsa yana juyo da ita ga fuskantar shi, a mugun tsorace ya saketa ya na mai cewa “who are you?”

Da mamakance ta kalleshi tace ” Noorie!!”, katseta yayi da cewa ” don’t call me that!, where’s my wife?”. Sai kuma ya juya da mugun gudu yana k’wala kiran ” Hayatii!”, da sauri ta biyo shi a baya tana mamakin abunda ya faru ya zaayi gashi a gabanta amma kuma yana nemanta. Turus ta tsaya ganin yanda ya fara nemanta a lungu da sak’on gidan sai dai babu ita.

Dawowa yayi gabanta kamar wasa taji ya shak’eta cikin fitar hayyaci yace ” where’s my wifeeee? what have you done to her?”. Rik’e hannunshi tayi tana mai k’ok’arin k’watar kanta, sai dai ina k’arfi ba d’aya ba ya shak’eta gam. Kakari ta fara tana kallonshi da fararen idanunta da suka rine saboda tsabar azaba, juyawa idanuwanta suka farayi tana shirin shid’ewa sa’annan ya sake ta.

Fad’awa tayi akan sofa tana nishi tana mai shafa wuyanta don ta tabbata yanda take farar nan sai shaidan hannunsa yai mata tambari, kallonta yayi cikin fushi yace ” before I do anything stupid, where’s my wife?”. Cikin muryanta da bai fita tace ” Babeee!”, kafa yasa yai ball da ita yana tambayan ” where’s my wife?, or do you think I’m a fool or blind da zan kasa bambance Mata ta?,,,,,now tell me where’s my wife before I kill you.”

Runtse idanu tayi cikeda azabar muguntar da yake mata, don k’afarshi ya d’aura a cikinta yana matsewa lumshe idanu tayi ta sadak’ar mutuwar tace tazo kuma tabbas aljanu sunyi wa mijinta mugun rik’o in ba haka ba ya zai dinga bugunta kamar ya samu jaka?.

Ta san yanada anger issues but she never know that he can be this dangerous to ko dai mahaukaci ne bata sani ba?. In ba mahaukaci ba ya za’ayi daga kawota gidan shi jiya da dare, yau ta farka da duka?. Ita kuma tata jarabawar kenan?, toh wallahi bata tsayawa Mama zata kira azo a d’auketa daga gidan wannan mahaukacin kafin ya kashe musu ‘ya.

Kallonta ya tsaya yi har lokacin ka’farshi yana cikinta sai kuma kamar an tsikare shi yace ” I’ll call the cops right away since you don’t want to talk, you’ll definitely talk in the station”.

Shafa aljihunshi yayi babu waya hakan yasa ya tuna da cewa wayar tana d’aki, k’ofa ya nufa yai locking tareda zare key sannan ya koma ya rufo kitchen d’in da suka baro shima ya sake locking da kyau don kar ta gudu kafin ya nufi d’akin don d’aukar waya. Tana a yashe a k’asa dafari yana fitowa daga bakinta saboda haurin da yayi mata a cikin da bai ga abinci ba, jan jiki ta fara yi zuwa toilet d’in parlorn da k’yar ta iya tsayuwa a ciki.

Wash hand basin ta isa tana kunna ruwa, ta d’ibo ruwan zata kai fuska ne ta lura da sauyin da hannunta yayi. Da sauri ta zubar da ruwan tana jujjuya hannunta cikeda taajjubi, kallon madubin dake gabanta tayi a take ta sanya ihu tana mai rirrik’e fuskarta cikeda tsoro ta furta ” this ain’t no me!, who is thissss?!” A take ta sulale k’asa cikin rashin k’arfi don yanzu ta yarda ko waye zai iya dukanta don ko ita kanta tana tantamar waye a gabanta a yanzu haka shafa jikinta ta fara yi ta na fashewa da kuka cikeda damuwa tace ” ya lateef what’s happening to me?”

Me ya sameta?.
Meye matsalar?.
Shin da gasken canja ta akayi?.
Ko dai ita ce?.

Salon na daban ne, haka ma matsalar ta daban ne. I bet baku tab’a jin salo irin wannan ba ku biyo ni muje zuwa kar ku yarda a baku labariiiii….

Rate, share, comment.

Khadeejah bint Isma’il (Deejasmah)

Mikiya Writers’ Association (MWA)

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

Yasmeenah 2 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×