Ranakun da suka rage daurin aurena da ya Safwan ƙara kusantowa suke fargaba kuma daɗa lulluɓe ni take.
Mami kam ko a jikinta ko da wasa kuma ba ta kuma ce min komai ba sau biyu tana kama ni ina share hawaye sai ta yi kamar ba ta gani ba abin da dai ta maida hankali gyara da ake min kamar ba gobe daga Haj Yar Shuwa.
Ana saura sati guda zan tafi Malumfashi in kwana biyar, sai in sauka Kaduna a ɗaura aure a taho da ni.
Daddy ya bayar da mota a ka kai ni can. . .