Skip to content
Part 12 of 13 in the Series Abbakar by Fadimafayau

Bai bi ta kan kowa ba ya shige bangaren su na ƴan mazan gidan, kai tsaye toilet ya shige, ruwa me dumi ya haɗa yai wanka ya wanke jikin sa, yakai sau goma still bedana jin wani iri ajinkinsa ba, haƙuri yai ya ɗaura towel ya hau shaving din gemun da ya yi wanni iri a fuskar sa, ya rarrage sumar kansa sannan ya sake wanka, aƙalla yadanji daɗi.

Ya fito yana saka kaya ne Hajiya ta shigo riƙe da kofi, Ummi na biye da ita taƙe da flask gabaki ɗaya sunyi mamakin Mahfuz ya koma mutun sak mai hankali, Hajiya tazauna gefen gadon ummi ta zauna gefen kujera.

Saida ya kammala saka kayan yazo ya gaida Hajiya, aƙallah ta danji daɗin ganinsa, yanzu ba kamar ɗazu ba,  “ga tea kasha ko zakaji dadin cikin ka, ga ɗanwake kuma sekaci” Hajiya ta faɗa tana nuna masa kwanunakan da suka shigo da su yunwa yake ji sosai hakan yasa be musa ba ya amsa ya fara sha.

Yana san Ɗanwake sosai, hakan yasa ya karba da zumudi yahauci saidai taunar farko yaji ba daɗi dan gabaki ɗaya bakinsa ba daɗi, dagyar ya haɗiye a hankula ya furta “Allah ya isa tsakani na dakai Nasir” hankalin Hajiya ya tashi tadai daure bata ce komai ba.

Ganin ya ajiye yaƙi ci ne ta kalleshi “kadaure ka ci”  ya tsina fuska ya yi, Hajiya wallahi ba test bakina ɗaci ɗaci ma nake ji.” Dafo shi ta yi “nasani amma  daurewa zakayi kaci se ahankula komi zai koma normal.”

Juyowa ta yi ta dubi Ummi ta ce “Ummi kije ki samo toka ki gasa masa nama da ita zai tai makawa test din bakinsa”  to Hajiya kawai Ummi ta ce.

Da yamma agun cin abinci kowa ya hallara, har Mahfuz inka ɗauke Nasir da baya gidan, Mahfuz yakai lomar abinci baki kenan Nasir ya shigo ɓangaren su ya wuce jaka kawai ya ajiye sannan ya fito zuwa falon gurin cikin abincin ya nufa in da yazo yaja kujera ya zauna, kamar koyaushe kujerarsa kusa da ta Mahfouz ya sha kan Mahfouz ɗin “ƙanina yajikin naka?,” tan kaɗe hannun nasa Mahfouz ya yi cema akayi banda lafiya ne?” ya faɗa tare da miƙewa fuuu yabar gurin.

*****

Koda Abbakar ya bar office ɗinsa gida ya wuce dan gabaki daya ransa ya baci yama rasa abinyi.

Da ummi ƙanwarsa ya ci karo zata fita, tace “lah yah sannu da zuwa”  ya amsa “yawwa ina zuwa haka da yamma?” Murmushi ta yi  “yah zani gidansu khairiyya ne zamu dan tattauna” yai dariya “zadai asha gulma” tai dariya wallahi yah ba haka bane hira kawai zamuri am bored ne” taɓe baki yayi tare da yin ciki kyaji dashi.

Ga bakidaya mutan gidan na falo har masu aiki, shima anan ya zauna bayan ya gaida Hajiya yasa baki cikin firar da suke, hakan ya rage masa kashi arba’in na bacin ran dake damunsa.

Kiran sallahr magariba ce ta tashi kowa dan kawo farilla, kai kayansa samansa ya yi kafin ya daura alwala ya fice.

Daga masallaci gidansu Mahfouz ya wuce baisan an dawo da Mahfouz ɗin ba, ganinsa a gida ba ƙaramin daɗi ya masa ba, sun tattauna kafin suyi sallama har ya fita ya dawo.

“Ban faɗa ma ba, wani abin takaici” nan ya zayyana masa komi cikin takaici Abbakar ke bashi labarin, Mahfouz ya goge hawayen da yazo masa “ba komai Aminin Allah ya kawon mafita”  “amin” Abbakar yace.

“Kasan me?” inji mahfuz “sai kafaɗa” Abbakar ya faɗa “ni wallahi bawai gidan mahaukata da aka kaini ne matsalata ba babbar matsalata itace San Ummu da kullun ke ƙaruwa cikin raina ko nayi yunƙurin cireta araina abu kamar ƙarashi ake.”

Nisawa ya yi kan ya ci gaba “Yana ɗaya daga abinda yasa nake jin haushin yah Nasir da ya aureta, ni wallahi yanxu ji nake da rashin Ummu gwanda abanni in dawwama gidan mahaukatan.”

Abbakar ya dafa shi “se haƙuri taka ƙaddarar ce a haka” murmushin takaici ya yi uhun “ba ƙaddarata bace, nasani haƙƙine ke bibiyata tunda Allah ba azzalumin sarki bane yana sakawa wanda aka zalunta,” Mahfouz ya faɗa cike da nadama, girgiza kai Abbakar ya yi,  “kadena sa haka aranka ka ci gaba da ƙoƙarin mancewa da ita ni zan wuce kar hajiya taga na jima.”

Yana barin ginda su Mahfouz din yahau share hawayensa wanda tun ɗazu suke san fitowa yana jarumtar riƙe su shi kaɗai yasan azabar da yake ji na san dalibar  tasa dauriya kawai yafi amin nasa. Ba tsaki yaja yahau gado ko Allah zaisa yadan samu bacci.

Baccinma gabaki ɗaya yaƙi zuwa, daya rufe idanunsa Ummu yake gani, tana masa murmushinta da yake ƙara mata kyau agunsa, yarasa wace irin zuciya gareshi me nacin tsiya da take jawo masa masifa kala kala, ace dik yan matan dake sansa takasa kallonsu sai matar wani.

Ganin da gaske idanunsa basu shirya yin bacci ba yasa ya miƙe yashige toilet dinsa ya dauro alwala ya hau nafil filu.

Yau lahadi ba inda Abbakar zaije, hakan yasa ya fito babban falo dan yin fira ko zai samu ya rage kewar da ke damunsa.

Hira suke sosai inka ganshi bazaka taɓa cewa yana cikin damuwa ba danshi din akwaishi da jarumtar boye damuwa, duk girmanta shi yasa ko hajiyarsa take cewa yana da zurfin ciki.

Yau litinin yanada kula da masu jarrabawa, ƙarfe biyu, hakan yasa tun asuba da yasamu bacci ya ɗebe shi yai me isarsa, dan ya dade be yi me daɗin sa ba, sai goma ya farka yai wanka sannan ya sauka danyin breakfast ɗinsa.

Bakowa a falon sai kwanukan abinci dake kan dining table, da alamu nashi ne kawai saida yaci sannan yaje dan gaida Hajiyarsu.

Tana kishin giɗe tana tasbihi suka gaisa, kafin yace “Hajiya mu zamu fita” tadan gyara zama “to Allah ya kiyaye ya tsare” ya amsa da “amin” cikin jin daɗi.

Gidansu Mahfouz ya wuce sun ɗan taɓa fira da Hajiyarsu sakamakon Mahfouz ɗin na wanka a hankula ya fara sako mata da maganar Ummu, aikuwa nan danan ta hau fada “wato mun samu ya mance da maganar shine zaka zo ka tayar mana da ita to ahir dinka.”

Sin sin ya miƙe yai ɗakin Mahfouz ɗin dan jiransa.

“Wai Mahfouz in tambayeka mana?,”
” Ina jinka” Inji Mahfus da ke shafa mai “in har ka yadda Ummul khair ba matar Nasir bace, me yasa sukayi karyar aure?” Mahfouz yai shiru na dan lokaci kafin yace “waya faɗa maka ban yadda ba?, ni wallahi na yadda matarsa ce.”

“Kasan kawai meke ban mamaki?” Mahfouz ya faɗa yana kallon Abubakar ” seka faɗa” inji Abbakar “kawai ina mamakin me yasa yah Nasir yakesan dole sai ya haukatani ta hanyar nunan bashi nake gani innaje gidan matar tasa ba.”

Abbakar yai dariya “ba dole ya haukata ka ba, fansa suke dauka shida matarsa” Mahfouz yai danshiru na wani lokaci, “yes u are right wallahi se yanzu na gano dalili wato ya zabi mace kan dan uwansa.”

“To wallahi tunda haka ya zabarma kansa ni nasan nafishi santa,  zan nuna masa hauka sedai kowa ya rasa dan wallahi kashe shi zan, yau bako gobe ba ya miƙe ya zari wuqar dake kan kayan marmarin dake bed side drawer yai waje yana huci Abbakar ya bi bayan sa da sauri.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Abbakar 11Abbakar 13 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×