Skip to content
Part 8 of 13 in the Series Abbakar by Fadimafayau

Har ya kusa office ɗin Dr Mansur HOD ɗin su, sai kuma ya tsaya cak yana kallon Paper ɗin da ke hannun sa, wadda ya rubuta, Ko me ya tuna oho, kawai ya hau yayyaga paper ɗin tare da juyawa zuwa office ɗin sa.

Sam kasa yin komai ya yi, rufe office ɗin ya yi, ya dawo ƙasa ya kwanta, bawai dan yana jin bacci ba sai dan damuwa ta masa yawa, zaman ma wahala yake masa, yana jiyowa daga bakin ƙofa ɗaliba na bugawa, ransa a ɓace yake ji yake tamkar yaje ya
miƙe ya zo bakin ƙofar ya hau su da faɗa, yana jiyo muryar wata cikin ɗaliban na fa ɗin ” kuzo mu tafi wataƙil baya nan” bai san ya sukai va ya kuma jin wata na faɗin “wallahi yana nan ba a idon mu ya shiga ba, in yaji da bugun namu ya buɗe” girgiza kai ya yi yaran yanzu akwai matsala, aiko mu zuba in zaku kwana ba zan buɗe ba ya faɗa aransa..

Ran litinin

Abinda bai saba ba wato yawo cikin sch din, yau  shi yaji yana sha’awa tafe yake cikin nishadi ransa fes yakejinsa, lokaci lokaci yana amsa gaisuwar da ɗalibai ke kawo masa, ban baiyi tsammanin ganin koda ɗan ajin su Khairiyya ba, ballanta kuma ita.

Daga nesa ya hango yarinyar da kema khairiyyan raino, haka kawai yaji yanasan ganin babyn, ya dan matso dab da inda yarinyar keta faman jijjiga yaron yace “ki miƙama mamansa shi mana, kar ya shiɗe” kallon sa yarin yar ta yi kafinta de ” tana test ne” ta faɗa tana ta faman jijjiga shi “ayya kawoshi to.” Ya faɗa tare da miƙa hannu.

Tai saurin kuma ruƙun ƙumeshi jaririn tare da faɗin “tace kar inbama kowa” ta faɗa cike da fargabar ar mutumin yace ta masa rashin kunya.

Murmushi Abubakar ya yi ” to ai ba guduwa zan dashi ba,” ta miƙa masa shi sabida kwarjinin da yai mata bawai dan taso ba cikin ranta kuwa tsoron kar uwar ɗakinta ta tazo taga ta bawa wani ne.

Kallon yaron yake haka kawai yaji ya shiga ransa, “Masha Allah” ya fada a fili yayin da a ransa yake fatan inama ace yaronsa ne, yaron kuwa ya bangale da dariya dimple insa me kyau ya bayyana “ya sunansa?” ya tambaya, sunansa “Mahfuz”

“Mahfuz” ya kuma mai mai tawa tace “eh anman abbasa ke kiransa dashi, ummansa tace sunan danta Abbakar” wani abu ya ziyarci zuciyarsa yai saurin kawar da tunanin da faɗin ” Allah ya raya shi” yarinyar tace amin ya miqa mata shi yabar gurin zuciyarsa cike da tunanin sunan yaron.

Abin duniya duk ya ishi Mahfuz hakan yasa shi yanke shawar zuwa yasamu yayansa Nasir.

Yana zaune yana rubutu a system insa Mahfuz ɗin yashigo da sallamar sa Nasir ya amsa batare da ya ɗago kai ya kalleshi ba ya cigaba da abinda yake “Yah gurinka nazo” Nasir ɗin bai ɗago ba bsi kuma dai na typing ɗin ba ya ce “ok I am all ears”

Kallon sa Mahfuz ya tsaya yi da alamu so yake ya vashi hankali, fahintar yaka yasa Nasir faɗin, “Inajinka maganar me zamuyi?”

Tattaro jarumtar sa wuri guda Mahfuz ya yi kafin yace “akan matarka ne”

Can Nasir ya tsaya da typing ɗin ya ɗago a ɗan tsorace “What? waya fada maka inada mata, ko kuma kai kamin auran?” yadda yawani haɗe gira yasa Mahfuz shiga taitayinsa ina tambayarka kaikamin auran yai saurin cewa ba…..bame ba, ya faɗa cikin rawar murya.

Dama me, in shirmen banza kazo faɗan kayi maza ka ɓacemun a gani inada abin yi. Nasir ya faɗa a kausashe.

“Daman kan Ummul Khair ne ta gidan Baba Yasir…” “anganta ne?” Nasir ya katse Mahfuz, Girgiza kai Mahfuz ɗin ya yi ” a’a kwanaki ne daman mukaje gun wata nida Aminin naga ashe tayi aure ta aureka.”

Bai nuna wata razanaba ko tsoro ba yahau faɗa “ni ta aura kum?,a sanin kanka ne banida aure bakuma ni da niyarsa, ayan kwanakinnan se dai in har alhakinta ne yafara haukata ka, kake zaton kowa ka gani ita ce, yarinyar da ba’asan inda take ba ake zaton tabi uwatta ƙasar su shine zaka zo kana tunanun na aureta, kai a hankalin ka zan yi aure ne gida basu sani?”

Cike da ƙwarin gwiwa Mahfouz ke magana “Wallahi yah ita nagani, kuma wallahi yah kai nagani a matsayin mijinta, ai ko na haukace naganka zan ganeka” saukar marin da yaji yasashi saurin miƙewa a firgice, cikin tsawa Nasir ke faɗin “fitar min aɗaki da alamin ka haukace din da gaske sha_sha kawai.”

Ganin bazai fita ba yasa Nasir tangaza shi waje, tare da banko ƙofar sa ya rufe, Mahfouz ya tsaya bakin ƙofa cike sa takaici, shi ya rasa wanne irin rainin wayo yayan nasa yake son ya masa, yasan tabbas shi ya gani bawai mafarki ya yi ba, ya jima a bakin ɗakin kafin ya wuce nasa, acanma juyayi da tunane tunane kawai ya yi ta yi har tsakiyar dare baisan sa’adda bacci ya ɗene shi ba.

Washe gari da sassafe Mahfuz ya yi ɗakin yayan nasa ya yi sa’a ya bar ɗakn buɗe bayan asuba, a kwance ya ganshi yana bacci, cike da kwarin gwiwa yai sauri ya fice daga gidan sai gidan Ummulkhairi.

Bugun da yake tamkar wanda yake cikin haɗari ya tsorata su, sam bai fasa na sai faman musu na hauka yake waannan yasa gabaki ɗaya suka yo bakin gate in, dan abinda basu saba ji bane.

Dabaya dabaya ya fara ja ganin yayansa Nasir sanye da rigar bacci yana mittsika ido alamin baccin be isheba.

Shima mittsika idon ya fara kodai dagaske na haukace ne ya fadawa kansa no wallahi da hankalina ya faɗa yana Girgiza kai.

“Malan lafiya?” mutumin da Mahfuz kena kallon Nasir ya faɗa “nazo tafiya da ƙanwata ne, kuma abarsona”

“what kanada hankali kuwa?, mata ta cefa” mutumin ya faɗa ganin bazai bashi hanya ba yasa Mahfuz tankaɗashi ciki ya hau jan Ummulkhairi tana tirjewa.

Mutumin ya dauko waya ya kira police sukai gaba da Mahfuz din yana faman kuru ruwar sai ya ɗauki masoyiyarsa.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 0 / 5. Rating: 0

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Abbakar 7Abbakar 9 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×