Rumasa’u.
Abin da su Alaramma suia guda shi ne ya faru, domin kuwa ango Aibo, idonshi ya murzawa toka ya ce aure ba da shi za a daura ba.
Duk yadda wakilanshi suka juya shi dambu ya taliya ya ki amincewa, wannan ya sa dole aka dakata da dauran auran Ruma. Ba da son ran wakilanshi, saboda sosai suna ganin girman duk wani ahlin na Baba Malam.
Tun maganar fasa auran ana yin ta iya masallaci, har ta tsallake mutane ta leko waje, ba iya nan ta tsaya ba, Sai da ta kuma tsallake mutanen waje ta leka cikin. . .