Skip to content
Part 29 of 30 in the Series Fasaha Haimaniyya by Haiman Raees

Wakar Bakandamiya

Wata in har ta fito

Taurari dole su ja da baya

Rana in har ta fito

Tafin hannu bai karewa

*****

Da sunan sarkina

Allah na mai kowa da komai

Wanda ya yi mana rana

Yai ruwa gefe can kuma ga mai

Tsira da amincinsa

Su tabbata a gurin ɗan Amina

Alaye da sahabbansa

Da dukkan mai son Manzona.

*****

Bakandamiya mun danno

Muna nan ko a ina ka duba

Kambu in muka murzo

Saura ai dole su ja da baya

Shi mai nema na jini

Wannan ai sai ya yi can kwata

In ko labarai ne

Sai Bakandamiya ai ƙawata.

*****

Shirye-shiryen mu a tsari

Ƙwarai suna faɗakarwa

Komai namu tsari

Aiki tsaf ba wata hargowa

Marubuta ku taho nan

Akwai dama domin bugawa

Mai karatu ka taho nan

Kai karatu tamkar ba kowa.

*****

In harbi kake so

Sai kunama ko kuma jaki

In ko bayanai kake so

Sai Bakandamiya gandun aiki

Taskar mu akwai faɗi

Tana nan kullum kan aiki

Bata da kowa na haɗi

Ta zama sha kundum babu raki.

*****

Bakandamiya son kowa

Ba ma tsari na su ‘yan wawa

Ma’aikatanmu haziƙai

Aiki kawai muke babu ƙiwa

Ana batu na giwa

Wake kawo zance na sauro

Bakandamiyar kowa

Ita ɗai ce domin ta fi saura.

******

Kafa ‘yar zamani

Me basajar tafiya a tsari

Ta zagaye ƙauye da birni

Da ƙamshi babu batu na wari

Kayan aiki zan-zan

Komai na tafiya kan tsari

Aiki tangarasras

Babu shirme kuma sam babu tsiwa.

*****

Allahu nake roƙo

Ya ida mana manufa a kullum

Sarkinmu nake roƙo

Ya kare mu da sharri a kullum

Ni ne naku Jamilu

Ko kuce Haiman ɗan Kaduna

Mai waƙe Bakandamiya

Nake ta adabo sai watarana.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 5

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fasaha Haimaniyya 28Fasaha Haimaniyya 30 >>

5 thoughts on “Fasaha Haimaniyya 29”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×