Da dare sai da Bashir ya kori su Khaleel zuwa gida, wai ba su son tafiya su bar ni. Tun safe kam sai ga su, don karfe bakwai a gidan ta yi masu.
Kuma duk yadda nai ta korarsu su tafi na ji sauki, kin tafiyar su ka yi, har zuwa lokacin da Zahra da Maman Usi suka gama abincin breakfast, bayan sun karya ne suka dauki na matansu.
Ba jimawa suka kuma dawowa, Zahra ta ce "Wai a hanya za ku gama naku angoncin ne?"
Affan ya ce Auntynmu "Momy ko mun zauna hankalinmu yana nan, kuma gidan ma. . .